TA AIKATA ZINA A RAMADAN SABODA TANA SON MALLAKAR KAYAN DA ZA TA SAKA DA SALLAH
TAMBAYA
(255)❓
Assalamualaikum
warahmatullahi wabara katuhu,malam ansha ruwa lafiya y ibadah
Dan Allah ina
da tambaya malam
Miye hukuncin wadda ta yi Zina a watan azumi Kuma d rana, Sbd dubu hamsin Batada ko dankunne na sallah ta yi Neman taimako ko bashi Bata samuba,taje ta aikata
Wannan
barnar watace tasani nama tambaya assalamualaikum👏
AMSA❗
Waalaikumus
salam warahmatullahi wabarakatuhu
Innalillahi
wainna ilaihirrajiun
Ita kam
wannan wace irin mace ce mara tsoron Allaah haka
Da watan
azumi ?
Aikata zina
ko da ba a watan azumi ba haramun ne amman a watan azumin zunubbin nasa yana
ninnunkuwa
Allaah
Azzawajallah ya ce:
( وَالَّذِينَ لَا
يَدْعُونَ مَعَ اللَّهِ إِلَٰهًا آخَرَ وَلَا يَقْتُلُونَ النَّفْسَ الَّتِي
حَرَّمَ اللَّهُ إِلَّا بِالْحَقِّ وَلَا يَزْنُونَ ۚ وَمَن يَفْعَلْ ذَٰلِكَ
يَلْقَ أَثَامًا )
الفرقان (68)
Al-Furqaan
Kuma waɗanda bã su kiran
wani ubangiji tãre da Allah, kuma bã su kashe rai wanda Allah Ya haramta fãce
da hakki kuma bã su yin zina. Kuma wanda ya aikata wancan, zai gamu da
laifuffuka,
( يُضَاعَفْ لَهُ
الْعَذَابُ يَوْمَ الْقِيَامَةِ وَيَخْلُدْ فِيهِ مُهَانًا )
الفرقان (69)
Al-Furqaan
A riɓanya masa azãba a
Rãnar kiyãma. Kuma ya tabbata a cikinta yanã wulakantacce.
( إِلَّا مَن تَابَ
وَآمَنَ وَعَمِلَ عَمَلًا صَالِحًا فَأُولَٰئِكَ يُبَدِّلُ اللَّهُ سَيِّئَاتِهِمْ
حَسَنَاتٍ ۗ وَكَانَ اللَّهُ غَفُورًا رَّحِيمًا
)
الفرقان (70)
Al-Furqaan
Sai wanda ya
tũba, kuma ya
yi ĩmãni, kuma
ya aikata aiki na ƙwarai to, waɗancan Allah Yanã
musanya miyãgun ayyukansu da mãsu kyau. Allah Ya kasance Mai gãfara Mai jin ƙai.
Abin da na
sani shi ne Allaah Azzawajallah yana yafe kowanne irin laifi ga wanda ya ga
dama in dai ba mutuwa mutum ya yi yana shirka ba. Allaah Azzawajallah ya ce:
( قُلْ يَا عِبَادِيَ
الَّذِينَ أَسْرَفُوا عَلَىٰ أَنفُسِهِمْ لَا تَقْنَطُوا مِن رَّحْمَةِ اللَّهِ ۚ
إِنَّ اللَّهَ يَغْفِرُ الذُّنُوبَ جَمِيعًا ۚ إِنَّهُ هُوَ الْغَفُورُ الرَّحِيمُ )
الزمر (53) Az-Zumar
Ka ce:
(Allah Ya ce): "Yã bãyĩNa waɗanda suka yi barna a kan rãyukansu! Kada ku yanke ƙauna daga rahamar Allah. Lalle Allah na gãfarta zunubai
gabã ɗaya. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai gãfara, Mai
jin ƙai."
An tambayi
Committe Fataawa na Saudiyya akan mene ne hukuncin wanda ya yi zina a watan
Ramadan ?
Suka ce:
"Zaiyi
Taubatun Nasuha ne, ta hanyar yan ta bawa, idan ba shi da halin hakan sai ya yi
azumin watanni biyu a jere, idan ba zai iya ba sai ya ciyar da miskinai 60
sannan kuma zai rama wannan azumin da ya karya (silar zinar) da kuma ya dade
bai rama azumin ba zai bayarda kilogram 1 da rabi na alkama"
(Fatawa
Al-Lajnah Ad-Da’imah, 9/255)
Yanzu don
Allaah matakin lalacewar wasu matan har yakai ace saboda ba su da kayan sallah
har sai sun bada kansu anyi zina dasu kuma a watan Ramadan ?
Wannan wanne
irin jahilci ne da rashin sanin yakamata. Ko a zamanin jahiliyya mata gori
sukewa mazinata ballantana kuma yanzu muna zamani ne da ilimi ya yi yawa sai
dai idan ba ka son ka tashi ka nema
Allaah ya
kiyaye mu daga aikata danasani
Amsawa:
Usman
Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.