𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Salamun Alaikum, Dr wai wani malami ne yake cewa bai halatta mutum ya cewa ɗan'uwansa musulmi da azumin nan ba ya ibada ba, wai sai dai yace masa ya azumi, Dr. Meye gaskiyar wannan maganar ?.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikum
assalam, Azumi ibada ne tun da Allah ya shar'anta shi ne saboda tsoransa, kamar
yadda ya fada a suratul Bakara, Ibada ita ce duk abin da Allah yake so kuma ya
yarda da shi na daga zance ko aiki, na fili da na ɓoye kamar yadda
malaman musulunci suka bayyana.
Azumi ibada
ne tun da Allah ya yarda da shi kuma yana nisanta wanda ya yi shi daga wuta,
kuma ya keɓance shi da daraja ta musamman wacce babu irinta, kamar
yadda hadisai ingantattu suka tabbatar, ga shi kuma sababin shiga aljanna,
ibada kuma ita ce hanyar shiga ni'imomin lahira, wannan yake nuna kuskuran
waccar maganar da kuma karancin ilimin wanda ya fade ta.
Allah ne
mafi sani.
✍️ Dr Jamilu Zarewa.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.