Ticker

6/recent/ticker-posts

Gurbin Makada Sa’idu Faru a Sikelin Manazartan Karni Na 21

Citation: Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Gurbin Makaɗa Sa’idu Faru a Sikelin Manazartan Ƙarni Na 21. Four Decades of Hausa Royal Songs: Proceedings from the International Conference on the Life and Songs of Makaɗa Sa'idu Faru, 3(3), 37-49. www.doi.org/10.36349/tjllc.2024.v03i03.005.

GURBIN MAKAƊA SA’IDU FARU A SIKELIN MANAZARTAN ƘARNI NA 21

Daga 

Dr. Adamu Rabi’u Bakura
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara State, Nigeria
Email: arbakura62@gmail.com
Phone: 08064893336 

Da 

Abu-Ubaida SANI
Department of Languages and Cultures,

Federal University, Gusau, Zamfara State, Nigeria
Email: abu-ubaidallah@fugusau.edu.ng | abuubaidasani5@gmail.com
Site: www.abu-ubaida.com | www.amsoshi.com
WhatsApp: +2348133529736

Tsakure

Masana suna la’akari da waɗansu alƙaluma yayin ayyana makaɗan Hausa a ƙarƙashin wani rukuni na musamman daga cikin tarin rukunonin makaɗa da ake da su a farfajiyar adabi da al’adun Hausawa. Waƙoƙin fada na daga cikin shahararrun rukunonin waƙoƙin baka. Wani abin lura shi ne, akan samu makaɗan da ke ƙarƙashin wannan rukuni da suke sauya sheƙa ko su kasance jemagu sakamakon tasirin zamani ko waɗansu dalilai masu alaƙa da tattalin arziki ko waninsa. Binciken nan yana da manufar bitar rayuwa da waƙoƙin Alhaji Sa’idu Faru domin ganin ko ya sauya sheƙa ko kuma ya kasance makaɗin sarauta kaifi ɗaya na tsawon zamanin kiɗansa? An yi amfani da dabarun ƙalailaice waƙoƙin makaɗin da kuma yin hira da masana a wannan fanni a matsayin hanyoyin tattara bayanai. Sakamakon binciken ya tabbatar da cewa, Sa’idu Faru ya tabbata makaɗin sarauta na yankan shakku, domin kuwa dukkannin waƙoƙinsa ba su fita daga da’irar sarauta da masarauta ba. Daga ƙarshe binciken ya ba da shawarwari da suka haɗa da nuna dacewar tattarawa da kundace waƙoƙin wannan shahararren makaɗi domin gudun salwantar su.

Fitilun Kalmomi: Kiɗa, Waƙa, Waƙoƙin Fada, Waƙoƙin Sarauta, Makaɗan Fada, Makaɗan Sarauta

1.0 Gabatarwa

Allah ya arzurta mawaƙan Hausa da ɗimbin hikima da basira tare da fasahar sarrafa harshen Hausa wajen ƙaga waƙoƙi. Wannan ne ya sa sukan rera waƙoƙin da suka danganci fannonin rayuwar ɗan’adam daban-daban. A sakamakon haka ne masana da manazarta adabin Hausa suka karkasa makaɗan zuwa azuzuwa ta la’akari da rukunonin al’ummar da makaɗan ke yi wa kiɗa da waƙa. Masana kamar Bello (1982) da Yahaya (1983/85) da Mashi (1986) da Gusau (1996) sun raba mawaƙan zuwa rukuni-rukuni gwargwadon fahimtarsu, ta la’akari da abubuwa kamar haka:

(i)        Muhallin waƙoƙinsu

(ii)     Kayan kiɗansu

(iii)   Jigogin waƙoƙinsu

Hasali ma kowane rukunin da makaɗan ke yi wa kiɗa da waƙa akwai kayan kiɗan da suka keɓanta da su wajen sarrafawa a yayin da suke aiwatar da sana’arsu ta waƙa. Bello (1982) da Ibrahim (1985) da Gusau (1996) sun raba mawaƙan Hausa ta la’akari da muhallin waƙoƙinsu, kamar haka:

(i)        Mawaƙan sarauta/Fada

(ii)     Mawaƙan jama’a

(iii)   Mawaƙan Sana’a

(iv)   Mawaƙan ban dariya

(v)     Mawaƙan sha’awa

Wannan aiki ya karkata kan binciko gurbin Makaɗa Sa’idu Faru a cikin makaɗan fada. Makaɗan fada sun shahara wajen luguden kalmomin Hausa ta fuskar salo, raha, ƙaƙale, yabo, zambo, habaici, shaguɓe, zuga da adana tarihi, da sauransu. Sukan sauya falsafar da suka gada kaka da kakanni sakamakon sauyawar zamani da ire-iren sauye-sauyen da ke wanzuwa a tsarin sarauta da raguwar ƙarfin ikon sarakunan ƙasar Hausa. Wannan ya sa wasu makaɗan suka zama bigi-sa-bigi-taiki domin neman tara abin duniya. Fahimtar haka ne ya sa wannan muƙalar ta yi azamar ɗora waƙoƙin Ɗan’umma Uban Kiɗi bisa sikelin bin diddigin gano ko makaɗin ya sauya sheƙa sakamakon sauyawar zamani, ko kuwa yana kamilin makaɗan sarauta har ya karɓa kiran Ubangijinsa?

2.0 Bitar Muhimman Batutuwa

2.1 Kiɗa

Kiɗa Bahaushiyar kalma ce wadda Hausawa suke kiran ta kiɗaa. Kalmar tana cikin jerin kalmomi na suna jisin maza. Jam’in kalmar kuwa shi ne kaɗe-kaɗe. A wani karin harshen kuwa sukan ce kiɗe-kiɗe. Kalmar tana ƙunshe da ma’ana kamar haka:

(i)        Buga ganga ko kalangu da abin bugawa.

(ii)     Bugun ƙwarya ko goge ko garaya da hannu ko da makiɗi ko da wani abu, kamar yadda Kano, (2006 p. 243) ya bayyana.

Garba, (1990 p. 89) cewa ya yi kiɗa na nufin: “Yin amfani da abubuwa don ta da amo iri daban-daban.” A wata ma’anar kuwa cewa ya yi kiɗa na nufin, “Fasahar tsara amo na muryar mutum ko daga abubuwa ko duka a haɗe.” Yayin da aka dubi waɗannan ma’anonin za a iya cewa, kiɗa yana nufin buga wani abu a kan wani domin samar da wani amon sauti da ka iya jan hakalin mai saurare.

2.2 Waƙa

Kalmar waƙa tana cikin jerin kalmomin suna jinsi mace. Jam’inta kuwa waƙoƙi ko waƙe-waƙe. Kalmar tana ƙunshe da ma’anar: “Magana wadda akan rera da baki, aka tsara bisa wani zubi na musamman” kamar yadda Garba (1990 p. 152) ya nuna. Shi kuwa Kano, (2006 p. 466) ya bayyana ta da ma’anar, “Tsararriyar magana da ake rerawa a kan kari ko rauji.”

Waƙa a bisa ma’anarta, tana nufin furta abin da ke cikin ƙwaƙwalwa. Sau da yawa akan ji Bahaushe na cewa:

a.      Na waƙa yi masa dukan fitar arziki.

b.      Na sha waƙa zuwa aikin Hajji.

c.       Na waƙa masa farashin kayan.

d.     To, Allah ya sa ba waƙa ba ce.

A wata ma’anar kuwa, waƙa takan kasance wata murya ko zaƙin murya mai shiga zuciya da faranta rayuwa. Misali , Bahaushe kan ce:

a.      Ai na zaci waƙa ce.

b.      Ya matse sauti kamar mai waƙa.

c.       Zaƙin murya sai ka ce zabiya.

Ta wata fuskar kuwa, waƙa takan kasance wata magana wadda akan rera da baki, wadda kuma aka tsara bisa wani zubi na musamman.

Dangane da ma’anar waƙa ta ɓangaren adabi kuwa, za a ga masana adabin baka da dama sun ba da ma’anarta a wurare mabambanta gwarwadon fahimtarsu. Daga cikin masanan, Gusau (1984 p. 3) cewa ya yi:

Waƙar baka ita ce wani saƙo cikin zance na azanci da ake rerawa ba faɗa kurum ba, ta cikin hikima da fasaha da zaɓaɓɓun kalmomi, waɗanda suka dace da saƙon. Kuma tana zuwa gunduwa-gunduwa, dangane da sautin murya da kiɗa da amshi da gaɗa da taɓi ko zabiyanu mai saka zuciya jin daɗi.”

Shi kuwa Umar (1987 p. 7) ya bayyana ma’anar da cewa:

Waƙa ita ce nau’in sarrafaffen harshe da ake gabatarwa da sigar gunduwoyin zantuttukan da ake kira baitoci ko ɗiyoyi, waɗanda ake ginawa a kan kari ƙayyadadde, kuma ake rerawa da wani irin sautin murya na musamman.

Yayin da aka nazarci waɗannan ma’anoni da masana suka bayyana, za a ga cewa, suna ƙoƙarin nuna cewa, waƙa na nufin tsararriyar magana da ke ƙunshe da fasaha da hikimar sarrafa harshe da ake rerawa gunduwa-gunduwa, cikin wani amo na musamman.

 

 

2.3 Waƙoƙi Fada

Su ne wasu manazarta kan kira da waƙoƙin sarauta. Waƙoƙi ne da ake yi wa duk wani da ya jiɓinci jinin sarauta ko aka ba shi wani matsayi na musamman a majalisar sarki, inda ake taro domin gudanar da mulkin al’umma cikin tsari irin na gargajiya. Masu aiwatar da waɗannan waƙoƙin su ake yi wa laƙabi da makaɗan sarauta ko mawaƙan sarauta.

Ta fuskar ma’ana kuwa, Gusau (1988 p. 165) cewa ya yi:

Waƙoƙin baka na fada su ne waɗanda makaɗa na musamman ke gudanarwa ga sarakunan gargajiya da iyayen ƙasa da hakimai da dagatai da masu unguwanni da ‘ya’yan sarakuna da fadawa da masu riƙe da da muƙaman sarauta da sauran ƙungiyoyin da suka jiɓinci sarauta.

Waƙar fada na zuwa ne a rere cikin sautin murya da daidaita shi, wanda ya sa take zuwa gutsure-gutsure (gunduwa-gunduwa) tare da maimaita gindinta a tsakaninsu. Kowane gutsure kammalalle ne ga kansa, amma wani zubin ma’anarsa takan cika ta tumbatsa har ta tsallaka ga gutsuren da ke bi masa. Gutsuren nan ne ake kira ɗan waƙa, jam’insa kuwa, ɗiyan waƙa.

Ana iya cewa, waƙar fada shiryayyen zance ne mai zuwa gaɓa-gaɓa bisa ƙa’idojin tsari da daidaitawa da ake yi wa wanda ya shafi sarauta domin a yabe shi, ko zuga shi ko kambama shi tare da fito da shi fili kowa ya san shi. Takan ƙunshi nakasa (aibanta) abokan hamayyar wanda ake yi wa waƙar ta hanyar yi musu zambo da habaici da shaguɓe da nuna hushi da tsoratarwa da firgitarwa da sauransu.

2.3.1 Wanzuwar Waƙar Fada

Ana kyautata zaton an soma waƙa ne a farfajiyar doron duniya a daidai lokacin aka ƙirƙiro farauta da samuwar addinin gargajiya. Gusau (1988 p. 167) ya nuna cewa, waƙa ta ƙara bunƙasa da haɓaka sanadiyyar yaƙe-yaƙe da bayyanar sana’o’i da wasannin motsa jiki da wasu lamurran da suka jiɓimci al’adun gargajiya. Masanin ya nuna cewa, a farfajiyar ƙasar Hausa farauta ta kasance daɗaɗɗiyar sana’a da aka fara aiwatarwa. Hasalima an sami waƙoƙin da suka dangance ta.

Ana cikin irin wannan yanayi ne, sai sarautun gargajiya suka bayyana sakamakon taruwar al’ummar Hausa tsangaya-tsangaya. Wannan ya faru ne tun daga lokacin da suka kafa mazaunai don samar da wurin zama na dindindin, domin samun damar gudanar da sana’ar noma da kiwo da wasu abubuwan inganta rayuwa tare da kare kai daga farmakin namun daji. Ana kyautata zaton daga lokacin ne aka soma yi wa sarki waƙoƙi gajeru. Bayan bunƙasar waɗannan tsangayoyin mazaunin farko zuwa ƙauyuka da garuruwa da birane, sai yaƙe-yaƙe suka haddasu a tsakaninsu, domin ƙoƙarin tabbatar da mulkin danniya. Ana cikin irin wannan yanayi ne yaƙe-yaƙen ƙabilanci suka wakana a tsakanin ƙabilu da Hausawa domin son mulki da iko da kuma shugabanci na sarakuna da ke mulkin su, ko kuma don neman faɗaɗa ƙasa ta mulki domin ta zama babbar daula.

Sakamakon irin waɗannan yaƙe-yaƙe da suka auku ne ya wanzar da samuwar wasu masu rauni da ke da kishin al’ummarsu; waɗanda ba su da ƙarfin karawa da dakarun yaƙi. Su ne suka dinga amfani da hikimarsu da basirarsu da zalaƙarsu wajen gudanar da kirari na yabon sarakunansu tare da zuga jarumansu domin ƙara musu ƙwarin guiwar fatattakar abokan adawa.

A wani ƙaulin kuma, Gusau (1988 p. 167) ya nuna cewa, makaɗan da suka rinƙa yi wa sarakunansu guntayen waƙoƙi tun kafin a fara yaƙe-yaƙe ne suka cigaba da koɗa sarakunansu a fagen daga tun kafin a fita yaƙi ko bayan an dawo.

A wani ƙaulin kuwa an bayyana cewa, a lokacin da ake kaɗa wasu kayan kiɗan yaƙi kamar: Tambari da kurya, sai Ɗanma’abba ya rinƙa aiwatar da kirari tare da zuga sarkinsu. Daga irin haka ne ‘Yanma’abban suka samu sukunin ɗinka ganguna da ƙudurin in an tafi yaƙi ko bayan an dawo su dinga cicciɓa sarki da jama’arsa. Hasali ma tare da su ake zuwa yaƙin. Ko an samu ɓacin rana, ba za a kashe su ba, sai dai su bi sarkin da ya samu nasara su dinga yi masa waƙoƙi suna zuga shi kan bajintarsa (Gusau, 1988 p. 168). A sakamakon haka ne wasu ƙasashe suka samu damar mallakar tamburran abokan hamayyarsu. Misali, kamar yadda ake hasashen cewa irin haka ne ya haifar da Gumawa suka mallaki tamburran Zamfarawan Anka.

A tsakanin shekarar 1910 zuwa 1915 a daidai lokacin mulkin Sarkin Musulmi Muhammadu Maiturare aka daina kiɗan yaƙi, kamar yadda Gusau (1988 p. 170) ya nuna. Daga nan sai makaɗan suka koma ga aiwatar da waƙoƙin ga sarakuna suna yabon su ta hanyar bayyana musu irin bajintar da kakanninsu suka nuna a fagen fama.

Wannan salon kiɗan shi ne ake yi wa laƙabi da kiɗan fada ko kuma a ce kiɗan sarauta ko na iko ko mulki. Hasali ma shi ne ya maye gurbin kiɗan yaƙi. Daga lokacin ne sarki kan gayyato mawaƙi ya yi masa waƙa a inda zai yabe shi, ya kuma zuga shi, kana kuma ya kushe abokin gabarsa. Yayin da mawaƙi ya gama rera waƙoƙinsa, sai sarkin ya yi masa gagarumar kyauta ta ƙasaita. A sakamakon wannan, mawakin yakan ji yana ƙaunar sarkin. Soyayyarsa takan sa ba wanda yake yi wa waƙa sai sarkin. Sakamakon haka ne sarakuna suka samu damar mallakar makaɗa da mawaƙa a fadojinsu, har suka zama makaɗan fada, kamar yadda Gusau (1988 p. 170) ya bayyana.

2.3.2 Musabbabin Yin Waƙoƙin Fada

Akwai abubuwa da dama da suka sabbaba ƙaga kiɗan fada. Ire-iren waɗannan abubuwan sun ƙunshi, nuna buwaya (gagara) da rinjaye (fifiko) da dawwama cikin samun nasara da galaba a kan maƙiya da soyayya da kyauta da sauransu. Sakamakon irin waɗannan abubuwa da mazaje suka keɓanta da su ne, ke sa a shirya musu waƙoƙi domin ƙara zuga su tare da fito da martabarsu da kwarjininsu a idon jama’a. Misali, ga abin da Malamin Kiɗa Sa’idu Faru ke bayyana wa Sarkin Kiyawa na Ƙaura Alhaji Abubakar, a inda yake cewa:

Ni kiɗin yaƙi nay yi ma Abu na Isau,

Ba ni son kana zaunawa banza,

Ka ɗauki takobi da bindigogi da bakukuwa.

Ba mu sansani sai bakin Tsabre,

Kano da Katsina hak Kwantagora,

Duk riƙon Namoda na, shi na ac can,

Garba ka amshe riƙon duk da Umaru,

Umaru yab bam ma.

(Sa’idu Faru: Gwabron giwa na Shamaki, Baba Ubangandu)

2.3.3 Makaɗan Fada/Sarauta

Su ne makaɗan da ke yi wa sarakuna waƙa kawai. Ba kasafai suke yi wa sauran jama’a waƙa ba. Sun fi mayar da hankalinsu a kan uwayen gidansu. Sarakuna su ne iyayen gijinsu. A sakamakon haka, ba sa yi wa kowa waƙa sai da izinin sarkinsu. Wannan na faruwa musamman kasancewar sarakunan ne suke ɗaukar ɗawainiyarsu, kuma sun fi kowa ganin ɗaukaka da darajar sarakunansu. Makaɗa da dama da ke cikin rukunin farko na makaɗan sarauta suna da wannan falsafar a cikin zukatansu. Misali, Mu’azu Na’alalo cewa ya yi:

Darajar kaza gashinta,

Darajar makaɗi sarkinai,

(Gital, 1984) a cikin Abba da Zulyadaini (2002)

Haka shi ma Jankiɗi ya ce:

Jumirin kwaram a kwana ana tafiya sai goga,

Jaki bai kai nan ba,

‘Yan yara masu kurin waƙa ku bar wargi,

Ma’ana ba ta zama ɗai ba.

Ni ba ni kiɗin iska sai ga sarkina.

Idan aka dubi waɗannan ɗiyan waƙa, mawaƙan fada suna nuni da cewa, yi wa sarakuna waƙa ya fi kome martaba, don haka suna kallon yi wa talaka waƙa kamar aikin banza ne. A ɓangaren sarakunan da ake yi wa waƙar kuwa, sukan ɗauki ɗawainiyarsu da ta iyalansu tun daga muhallinsu, har abin da za su ci da kuma suturarsu. Sa’idu Faru ma ya nuna yadda ubangidansa ke ɗauke da lalurarsa a cikin ɗiyan waƙoƙinsa. Misali, ga abin da yake cewa:

Sarki zamaninka na ruhwa,

Na ta da kaina,

Kowag gane ni da Daudu,

Ya san sarki garan gawurtacce.

(Sa’idu Faru: Waƙar Abubakar Sarkin Kiyawan Ƙaura)

A nan za a fahimci cewa, makaɗin na ishara ne da cewa shi makaɗin sarauta ne, don haka ne sarkinsa ke ɗauke da buƙatunsa.

Haka kuma ya fito fili ya na bayyana wa al’umma cewa, shi ne kawai makaɗin sarauta da ya rage a wannan zamanin. Sauran makaɗa sun koma makaɗan jama’a sakamakon juyin zamani. Ga abin da yake cewa kamar haka:

Sa’idu Faru ka waƙar iko,

Komai kaj jiya ƙarya a kai,

Sa’idu Faru ka waƙam mulki,

Komai kaj jiya ƙarya a kai.

(Sa’idu Faru: Turakin Kano Amadu)

2.3.4 Rabe-Raben Makaɗan Sarauta

A wannan rukuni na makaɗan sarauta (makaɗan fada) za a tarar cewa Gusau (1996) ya kasa su zuwa ɓangarori biyu. Kashi na ɗaya (1) da na biyu (2). Jerin makaɗan da suka faɗo ƙarƙashin kaso na farko su ne:

a.      Abdu Kurna

b.      Abubakar Akwara

c.       Alhaji Muhammadu Sarkin Taushin Katsina

d.     Aliyu Ɗandawo

e.      Buda Ɗantanoma

f.        Ibrahim Gurso

g.      Ibrahim Narambaɗa

h.      Idi Ɗangiwa Zuru

i.        Jibo Maituru

j.        Muhammadu Dodo Maitabshi

k.      Muhammadu Inyaga

l.        Salihu Jankiɗi

Kashi na biyu kuwa ya ƙunshi makaɗan da suka haɗa da:

a.      Alhaji Ɗankurma Maru.

b.      Alhaji Musa Ɗankwairo Maradun.

c.       Alhaji Sa’idu Faru

d.     Alhaji Sa’idu Maidaji Sabon-Birni

e.      Alhaji Sani Aliyu Ɗandawo

f.        Muhammadu Ango Maitabshi

g.      Muhammadu Maidamma Sarkin Taushi

h.      Sarkin Taushi Muhammadu Ɗanbunguɗu

i.        Umaru Maisa’a Tubali

2.3.5 Alaƙar Makaɗan Fada Da Sarauta

Makaɗan fada na ɗaya daga cikin rukunin al’umma da sarakuna ke ɗauke da lalurorinsu na yau da kullun. Sarki yakan zama ubangidan makaɗi, shi yakan ɗauki lalurar cinsa da shansa, ya yi masa gida ya ba shi gona, ya kuma rinƙa yi msa sutura tare da iyalansa. Haka kuma yakan ba shi kuɗaɗen ɓatarwa.

Sarki yakan amince wa makaɗinsa fiye da sauran fadawansa. Yakan zauna tare da shi su yi hira cikin sakin fuska sosai da zaman amana da taimakon juna. Shi kuma makaɗin zai dinga girmama sarkin da mutunta shi tare da yi masa ladabi da biyayya tamkar yadda al’ummar fada ke yi masa.

A al’ada, makaɗin fada bai fita waje ya yi wa wani sarki ko jinin sarauta waƙa, sai da izinin ubangidansa. Yayin da ya je waƙa gun wani, zai nuna wa sarkinsa duk nau’in abin alherin da aka yi masa. Wani lokaci, yana iya bayyana masa a cikin sigar waƙa.

3.1 Siffofin Makaɗan Sarauta Da Matsayin Sa’idu Faru

Makaɗan sarauta suna da waɗansu siffofi da suka fi alaƙantuwa da su. Sun haɗa da:

a.      Makaɗin sarauta shi ne wanda kan samu wani basarake ya zauna a wajensa ya kasance ubangidansa da zai rinƙa yi masa yammaci (kiɗa daren Juma’a) ko daren salla. Sukan bi sarki a duk lokacin da zai fita rangadi (kewayar gundumar da ke ƙarƙashin mulkinsa).

b.      Sukan nemi izinin ubangidansu kafin su tafi yawon kiɗa gidan wani sarki ko alƙali ko bafade ko wani mai arziki da ke ɗasawa da ubangidansu.

c.       Akasarinsu sun gadi kiɗa da waƙa irin na sarauta idan aka cire Aliyu Ɗandawo Shuni, wanda ya kasance ɗan wani shahararren malami da aka yi a can Shuni ɗin da ake kira da suna Modibbo Aliyu, Kamar yadda Gusau (1984) ya nuna.

d.     Sun fi kowane Bahaushe sanya tufafin gargajiya, wato sanya manyan riguna da wandunan buje da taguwoyi masu manyan hannaye. Sukan kuma naɗa rawani. Suna riƙe wannan al’ada ce saboda irin wannan suturar sarakuna kan ba su. Abin la’akari shi ne, sarakuna ba sa rabuwa da sanya manyan suturu komi gumi ko zafi. Hasali ma sarki ba zai fito gidansa ba rawani a kansa ba. shi ya sa makaɗan sarauta suka riƙe wannan ɗabi’a domin kare martaba da alfarmar sarauta. Shi ya bambanta su da sauran makaɗa da mawaƙan ƙasar Hausa.

Duban ire-iren waɗannan siffofi da aka ambata a sama da la’akari da irin sigar yanayin shigar Alhaji Sa’idu Faru za ka tabbatar shi cikakken makaɗin sarauta ne. A lokacin rayuwarsa ba ka raba shi da shiga irin ta iyayen gidansa.

3.2 Kayan Kiɗan Makaɗan Fada Da Gurbin Sa’idu Faru

Ta sigar kayan kiɗa kuwa, makaɗan sarauta sun sha bamban da sauran makaɗa da mawaƙan baka na ƙasar Hausa. Haka kuma sun kasu kashi-kashi dangane da kayan kiɗan da suke amfani da su, da nau’o’in waƙoƙin da kuma uwa-uba irin garuruwan da suke zaune da kuma inda suka ƙaurato. Ta fannin kayan kiɗa, za a iya kasa su zuwa kashi uku kamar haka:

a.      Masu kaɗe-kaɗe

b.      Masu bushe-bushe

c.       Bambaɗawa (masu kirari) (Ibrahim, 1983 p. 2).

Ta wannan haujin kuwa, Alhaji Saidu Faru yana cikin sahun makaɗan fada da ke amfani da kayan kiɗa dangin na sarauta. Su ma kayan kiɗan sarauta sun karkasu kamar haka:

(i) Tafshi

(ii) Kotso[1]

(iii) Jauje

(iv) Tambari

(v) Banga

Waɗannan kayan kiɗa akan yi amfani da su wajen tsima sarki ta hanyar kambama shi da magabatansa.

Kashi na biyu kuwa sun ƙunshi abubuwan busawa ne da suka danganci:

(i) Algaita

(ii) Kakaki

(iii) Ƙaho

(iv) Farai

Waɗannan kayan busa suna ba wa talakawa labari ne cewa, sarauta tana nan daram ta kafu. Suna kuma jawo hankulan masoya sarki da cewa su zo su ji abin da za a faɗa game da masoyinsu.

3.3 Sauya Sheƙar Makaɗan Sarauta Zuwa Na Jama’a

Sauye-sauyen ubangida ga makaɗan fada yakan faru ne a zamanin da sarakuna ke da ƙarfin ikon gudanar da al’amuran tafiyar da ragamar mulkin al’ummominsu, kafin mulkin Jamhuriya ta farko. A waɗansu lokuta makaɗa na sauya ubangidansu, musamman saboda dalilai kamar haka:

a.      Yayin da ubangida (sarki) ya karɓa kiran Mahaliccinsa.

b.      Yayin da aka fitar da shi daga sarautarsa.

c.       Yayin da ya daina yi wa makaɗinsa alheri.

4.1 Nau’o’in Waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru

Sa’idu Faru ya yi wa sarakuna da jinin sarauta waƙoƙi da dama waɗanda shi ma kansa bai san adadinsu ba saboda yawansu. Hasali ma, dukkan waƙoƙin shi ne ya ƙaga su da kansa. Shi ba kamar sauran makaɗan sarauta ba ne da ke maimaita waƙoƙin da mahaifansu suka aiwatar ba. A ƙasa an kawo waɗansu sarakuna da hakimai da uwayen ƙasa da ya yi wa waƙa:

1.      Sarkin Yamman Faru Ibrahim

2.      Sarkin Yaƙin Banga Sule

3.      Sarkin Kiyawan Ƙaura Abubakar Garba

4.      Sarkin Gabas Na Mafara Muhammadu

5.      Sarkin Musulmi Abubakar III

6.      Sarkin Yawuri Alhaji Muhammadu Tukur

7.      Sarkin Sudan Na Wurno Alhaji Shehu Malami

8.      Sarkin Kano Ado Bayero

9.      Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo

10.  Sarkin Gabas Shehu Uban Ƙasar Talata Mafara

11.  Turakin Kano Amadu

12.  Muhammadu Muhammadu Maidabo Tudun Falale

13.  Alhaji Muhammadu Mode, Ɗan Alin Birnin Magaji

14.  Sarkin Zamfaran Zurmi, Suleiman Muhammadu Sambo

15.  Sarkin Zazzau Alhaji Dr. Shehu Idris, da sauransu

Ta fuskar waƙoƙin da ya yi wa ubangidansa kuwa, ya yi wa Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo waƙoƙi da dama. Abin da hannaye suka samu nasarar dafawa su ne:

1.      Farin cikin Musulmi duk kai muka taƙama yau,

Muhammadun Muhammadu ɗan Abdu mai darajja.

 

2.      Sai na zo in yi mai kiɗi in ƙaro ilmi,

Mamman Bajinin Magaji mai takakkay yaƙi.

 

3.      Farin cikin Musulmin Duniya, mai martaba na Abubakar,

Ci fansa Alhaji Macciɗo.

 

4.      Kana shire Baban Yan Ruwa,

Na Bello Jikan Ɗanfodiyo.

 

5.      Bajinin gidan Bello Mamman Na Yari,

Sarkin Kudu Macciɗo ci maraya.

 

6.      Shugaban sahun gabas riƙa ƙwarai,

Muhammadun Amadu Uban Zagi.

 

7.      Hattara Bajinin gidan Bello Jikan Hassan maganin wargi.

 

8.      Ya yi Sarki daidai wada mai yanzu yar riƙa,

Alhaji Macciɗo jikan Mamman mai dubun bara.

9.      Mai babban rabo ginshiƙin Sarkin Shariffai.

 

10.  Hattara mai martaba Bello ɗan Bubakar,

Sarkin Kudun Hausa.[2]

Yayin da aka kwatanta Alhaji Musa Ɗankwairo a matsayinsa na mawaƙin sarauta kuma Sarkin kiɗan ‘Yandoton Tsahe Alhaji Aliyu, da Alhaji Sa’idu Faru, za a iya cewa, Ɗanƙwairo ya canza sheƙa sakamakon juyin zamani. Hasali ma ana hasashen cewa, tun waƙar Shirya Kayan Faɗa ba wata waƙa da ya sake yi wa ubangidansa. A madadin haka, sai ya karkata ga yin waƙoƙin jama’a da suka ƙunshi ‘yan kasuwa da ‘yan siyasa da malamai da tajirai. Wannan ne ya sa mafi yawan waƙoƙinsa suka zama na gama-gari. Misalan waƙoƙin sun haɗa da ta:

a.      Alhaji Shehu Kangiwa

b.      Kanal Umaru Muhammad

c.       Alhaji Ahmadu Aruwa

d.     Alhaji Kabiru Mado

e.      Alhaji Ali na Malan Bawa

f.        Alhaji Garba A.D. Kano

g.      Alhaji Garba Nadama

h.      Alhaji Ahmad Muhammad

i.        Alhaji Bala Maiyafe

j.        Malan Lawal Ƙalarawi

k.      Alhaji Bala Salisu

l.        Alhaji Sikofiyo

m.   Alhaji Bature Dogon Tela

n.      Alhaji Ibrahim Maganinta

o.      Waƙoƙin Faɗakarwa

p.     Waƙoƙin Jam’iyyun Siyasa

Ta la’akari da jerin waɗannan waƙoƙin, za su iya kawar da Ɗanƙwairo daga cikin sahun mawaƙan sarauta. Ta fuskar Sa’idu Faru kuwa, babu waƙar da ya aiwatar da za ta iya fitar da shi daga cikin sahun makaɗan sarauta.

4.2 Turakun Waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru

Kasancewar Sa’idu makaɗin sarauta ne na asali, bai sake juyin zamani da kwaɗayin tara abin duniya ya ruɗe shi ba. Shi ya sa ya tsaya wajen gina waƙoƙinsa a kan turakun da iyaye da kakanni suka assasa tushensu tun farkon fara kaɗe-kaɗen fada (sarauta). Binciken masana kamar Gusau (1996 p. 121) ya tabbatar da cewa, Makaɗa Sa’idu faru ba ya yi wa kowa waƙa sai sarki da wanda ya kasance jinin sarauta. Waƙar farko da ya fara aiwatarwa ita ce ta Sarkin Yamman Faru Ibrahim. Gindin waƙar shi ne:

Bi da maza ɗan Joɗi na Iro,

Iro magajin Shehu da Bello.

 

Hasken hitila ba ɗai da wata ba,

Tauraro haskenka subahin,

Dawaya kora ɗimau na wakili,

Uban sarkin zagi Bello na yari.

Ruwa da kada ɗibgau na Magaji,

Sai tsohon wawa ka shigar su.

(Gusau, 1996 p. 119).

Tun daga wannan waƙar sai ya ci gaba da yi wa sarakuna da ‘ya’yan sarakuna waƙoƙi. Yana cikin irin wannan yanayi ne, Allah cikin ikonsa da baiwarsa ya sada shi da Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo ɗan Sarkin Musulmi Abubakar na III, wanda ya sarauci ƙasar Talata Mafara daga 1953 zuwa 1956, kamar yadda Talata Mafara (2007 p. 17) ya nuna. Ya fara yi wa Sarkin Kudu Macciɗo waƙoƙi a daidai lokacin da yake riƙe da muƙamin Ubanƙasar Talata Mafara. Ga gindin waƙar da ya fara yi masa, a inda yake cewa:

Kana shirye baban ‘Yanruwa,

Na Bello jikan Ɗanfodiyo.

 

Gardaye zo ka yi man iso,

Faɗa mashi murna niz zaka,

Ɗan Sardauna jikan Hassan.

 

Babban ɗa ga Baura Sarkin Kudu,

Na Alƙali baban zagi,

Mai ja ma ya bari ɗan Adamu.

 

Na Sarkin Gobir Amadu,

Ci fansa ga wan Sarkin Ƙaya.

 

Waƙag ga da nim maka Muhammadu,

Na ji daɗin ta Mamman Sarkin Kudu,

Tun dak Kabi hak Kano ham Masar,

Hab birnin Legas hab Bici,

Kowa ya ji waƙar Sarkin Kudu.

(Gusau, 1996 p. 120).

Sa’idu Faru fasihin mawaƙin sarauta ne da ya naƙalci harshen Hausa ga baiwar da Allah ya yi masa ta fasahar ƙulla waƙa yadda za ta yi daɗi ta kuma yi armashi da ma’ana. Sakamakon haka ne ya kira kansa da Malamin waƙa, a inda yake cewa:

Sa’idu Malamin waƙa,

Mai kwana ɗumi na Mamman na Balaraba×2

Ban wuce gonata da irina ba,

Inda Sarkin Kudu nat tsaya.

Gindin Waƙa: Farin cikin Musulmin duniya.

(Faru: Waƙar Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo)

Sa’idu Faru bai taɓa yi wa talakka waƙa ba, komai tarin dukiyarsa. Hasali ma shi da kansa ya yi nuni da haka, a inda yake cewa:

Ban zo gidan Ɗanbita niy yi roƙo ba,

Ko ya raba lafiya ba ruwana.

A wannan ɗiyan waƙar ya fito ƙarara ya tabbatar wa al’umma cewa shi bai taɓa yi wa talaka waƙa ba. Ya jaddada cewa ba zai yi haka ba ko da mutumin yana samar da kowane irin jin daɗi da ingancin jiki da kawar da ciwo daga jikin ɗan’adam. Shi bai damu da duk wannan ba, ballantana ya yi masa kiɗa da waƙa. Kalmar ɗanbita a nan tana nufin leburan da ke aikin gyaran hanyar mota. A daidai wancan lokacin, sarakuna ne ke bayar da waɗanda za su yi aikin hanya. Sukan zaɓo waɗanda suka dace da aikin hanyar daga cikin talakawansu. A daidai wancan lokacin akan ji tsofaffi na maganar aikin diga da ke nuni da aikin hanya. A sakamakon irin wannan aikin talakawa da dama sun tara abin duniya.

Malamin waƙa ɗin ya bayyana dalilan da suka sa ba ya yi wa talaka waƙa da kiɗa kamar yadda Gusau (1996 p. 121) ya ruwaito su cewar:

a.      Ba wata hanya da zai bi ya ɓata wa talaka rai. A lokacin da talaka ya wulaƙanta makaɗi, to sai dai makaɗin ya yi na mai bara (haƙuri).

b.      Yayin da Sarki ko jinin sarauta ya yi wa makaɗi abin da ya ɓata masa rai, sai ya rama a cikin waƙa ta hanyar yi masa zambo ko habaici. Ba wani sarki ko jinin sarautar da yake son makaɗi ya yi masa su.

Za a iya samun wasu rukunin al’umma su ce, idan haka ne wane dalili ne ya sa Makaɗa Sa’idu Faru ya yi wa Alhaji Shehu Kangiwa waƙa? Amsa a nan ita ce, an yi waƙar ne a shekarar 1976 bayan an naɗa shi Turakin Kangiwa. Sarauta ce da Masarautar Argungu ta ba shi, a ƙarƙashin Shugabancin Maimartaba Sarkin Kabin Argungu, Alhaji Muhammadu Mera. Ya zama ɗaya daga cikin jigajigan masarautar. Don haka, an yi masa waƙar ne a matsayinsa na ɗaya daga cikin masu riƙe da sarautun gargajiya a Msarautar Argungu. Idan aka yi la’akari da ma’anar makaɗan sarauta da lokacin da aka aiwatar da waƙar, za a iya tabbatar da cewa Makaɗa Sa’idu Faru bai taɓa yi wa talaka waƙa ba. Shi makaɗin sarauta ne tsantsa.

4.3 Ƙananan Turakun Waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru

4.3.1 Yabo

Makaɗa Sa’idu Faru a cikin waƙoƙinsa yakan yabi ubangidansa ta haujin ambaton asalinsa. Yakan kuma danganta shi da asalinsa ta hanyar bayyana cewa ya gaji gidansu. Ta haka ne ya yabi Sarkin Kudu Macciɗo da irin wannan sigar a inda yake cewa:

Allah ya ba ka albarkar nan ta Alu Babba,

Ka gama da kyau cikin sa’a mun yi roƙon Allah,

Allah shi ba ka albarkar nan ta Shehu, Amin.

Ka gama da kyau cikin sa’a mun yi roƙo Allah.

Allah shi ba ka albarkar nan ta Bello, Amin.

Ka gama da kyau cikin sa’a mun yi roƙon Allah.

Allah ya ba ka albarkar nan ta Bubakar na farko.

Ka gama da kyau cikin sa’a mun roƙon Allah.

Allah shi ba ka albarkar Bubakar na biyu,

Ka gama lafiya da imani mun yi roƙon Allah.

Allah ya ba ka albarkar nan ta Aliyu Babba,

Ka gama da kyau da imani mun yi roƙon Allah.

Allah ya ba ka albarkar nan ta Alu ƙarami,

Ka gama da kyau cikin sa’a mun yi roƙon Allah.

Allah shi ba ka albarkar Abdullahi,

Ka gama da lafiya da imani mun yi roƙon Allah.

Allah shi ba ka albarkar nan ta Hassan Dattijo.

Ka kammale, ka ɗibo jama’arka.

Duk ka shirya mu gaban Ma’aikin Allah,

Mu yi farin ciki,

Mu ji daɗin da yaf fi daɗi daɗi na Annabi.

Mu ji ƙamshin da yaf fi ƙamshi, ƙamshi na Bubakar,

Allah shi sa ka samun martabar kakanka.

Yayin da aka dubi waɗannan ɗiyan waƙar, za a ga cewa, Sa’idu Faru na yi wa ubangidansa Sarkin Kudu Macciɗo fatan Allah ya ba shi albarkar waɗannan kakanni nasa ya kasance tamkarsu tare da samun martaba irin tasu.

Ba nan kawai ya tsaya ba. Har ma ya yabi Sarkin Kudu Macciɗo ta haujin iya gudanar da mulki, a inda yake cewa:

Shugaban duniya Alhaji Bello Sarkin Kudu,

Jan damishi Shehu Sarkin Gabas,

Baban su Alƙali.

Gadangadan Shehu Sarkin duniya,

Ba mai riƙo na ba.

Ai! Ina ba magana ba ce yanzu gidan Bani,

Ba mai kamar Macciɗon Hausa.

Girmanka ya kai muƙaminka ya kai,

Riƙon duniya wada Abubakar yak kai,

(Sa’idu Faru: Waƙar Sarkin Kudu Macciɗo).

A nan mawaƙin ya bayyana cewa, Macciɗo zai iya gudanar da mulkin wannan duniya sakamakon ƙwarewarsa a fagen mulki.

Ta fuskar addini ma, ya yabi ubangidansa a inda yake cewa:

Gindin Waƙa: Bajinin gidan Bello Mamman na Yari,

Sarkin Kudu Macciɗo ci maraya.

 

Jagora: Tsari gaskiya Bello kai Shefu yac ce,

‘Yan Amshi: Bari masu son dus su maishe ka yaro,

Duk kyauta da ilmi da neman dalili,

Da gode ma Allah da istingafari,

Da su Bello ɓello ɗan Shehu yat tcarma kowa,

Ka kai kamab Bello,

Ka gadi Moyi,

Saura ka kai inda mai Hausa yak kai.

Yayin da aka dubi ɗiyan da suka gabata, za a ga yadda wannan turken ya ƙara tabbatar mana da kasancewar mawaƙin a gurbin makaɗin sarauta. Makaɗan fada ne suka yi fice wurin yabon uwayen gidansu ta fuskar addini. Hakan na faruwa ne kasancewar sarakunan ƙasar Hausa su ne shugabannin addinin Musulunci tun kafin jahadin Shehu. Jagorancin nasu ya ƙara bunƙasa ne bayan tabbatuwar jahadi. Da irin wannan yabon ne sarakuna suke alfahari da makaɗansu.

A nan ya bayyana wasu siffofin da suka keɓanta ga sarakunan ƙasar Hausa, wato, kasancewarsu masu alheri ga alummarsu, da zamansu malamai masana dangogin ilmomin zaman rayuwar duniya, domin su ne tushen samun kyakkyawar makoma gobe kiyama. Ya kuma ƙara kawo abu da ya kasance tamkar ruwa da gishiri a fagen sarrafa abinci da sauran lamurran rayuwar duniya. A nan ya yi masa hannunka mai sanda ne da ya lizimci nuna godiya a kan ni’imomin da Allah ya yi masa da dagewa ga yin tuba game da kuskuren da yake aikatawa, domin ta haka magabatansa suka tsere tsara. Idan ya nace a kan haka, zai kai ga samun matsayin da Sarkin Musulmi Abubakar Sadik yake a kansa.

4.3.2 Zuga

A wannan haujin kuwa, Sa’idu Faru yakan harzuƙa ko tunzura sarkin da yake yi wa waƙa, ta hanyar kambama darajarsa. Dubi yadda yake cewa a waƙarsa da ya yi wa Sarkin Kudu Macciɗo mai take:

Gindin waƙa: Kana shire baban ‘yan ruwa.

 

Jagora: Wani taro da an ka zo Ikko na bariyac can,

Da Turawa da kuma ministoci had da kansiloli,

Sarkin Musulmi da Amdu Bello sun zo wurin dus sun ziyar tai,

Tafawa Ɓalewa ya sauka ga Lamiɗo Barno,

Nan kudu Shehu Talba,

Sarkin Bidda ya sauka ga Sarkin Ilori,

Kulluhinsu sarakunan majalisa sun taru Ikko,

Muhammadu Bello jikan Hassan kai sun ka zaɓa,

Don ka hi su kyawon shirin kawo dalillai.

Idan aka dubi kwayar turken wannan ɗan waƙar, za a ga ya fito ne ƙunshe da zuga Sarkin Kudu Macciɗo tare da fifita shi a kan waɗanda suka halarci taron. A ɗaya ɓangaren kuwa, ya taskace tarihin taron da aka aiwatar a Ikko tare da fito da maigidan nasa fili domin waɗanda ba su san shi ba su san shi. Irin wannan zugar ke ƙara tabbatar wa masu nazari gurbin da mawaƙin ya kasance.

4.3.3 Habaici

A cikin waƙoƙinsa akwai wuraren da yakan yi wa abokan adawar ubangidansa habaici ba tare da faɗa masa wata muguwar magana ba. Wannan kan iya kasancewa a cikin sigar jifa a kasuwa ko kuma ya san da wanda yake. Hasali ma makaɗan fada sun fi shahara ta fuskar amfani da habaici domin ƙasƙantar da abokin hamayyar sarkinsu ko muzanta shi a bainar jama’a a fakaice. Misali Sa’idu Faru yana cewa:

Zaki mai zama ga hilin Allah ga shi ga hili,

To wak ka san ya far mashi,

Kafin maza su shirya Mamman na Ali ya shirya.

Sun dai yi ɓaɓɓakar dutsi,

Sun yi gyangyaɗar dutsi,

‘Yan hannuwansu sun gaza.

Na Audu ko da ƙarfin Allah kana shiga gidan.

Na ce mai kama da ƙot,

Haka nij ji gun Badakkare.

Dogon sarki yana da ban sha’awa,

Ko da anka zo taro ya fi kyau da riguna,

Duk wanda ag gajere a aje shi gun rabon dawo,

Shi kai ma wanga dunƙule.

Aw wurin da mata ciki,

Har tuman gada yakai.

(Sa’idu Faru: Waƙar Sarkin Tudun Falale).

Da duban waɗannan ɗiyan waƙar za a fahimci Sa’idu Faru ya yi wa wasu ‘ya’yan sarki habaici ne a kaikaice, domin ya fahimci suna son su yi jayayya da ubangidansa.

4.3.4 Zambo

A nan ma akan samu inda yakan yi wa abokan hamayyar ubangidansa wata mugunyar magana. Misali a cikin waƙar da ya yi wa Sarkin Kudu Macciɗo yana cewa:

Gindin Waƙa: Gogarman gidan Moyi ci fansa niƙatau,

Mai babban rabo ginshiƙin Sarkin Shariffai.

 

Jagora: Na ishe dale tai ƙawa ga jamaat ta ba ƙawa.

‘Yan Amshi: Ya murɗe su duy ya zuba dogon akwati,

Rana ta kewayo ya naɗe ya kai Ilori,

Dac can yas sawo man kishe,

Ya sai tabarau.

Yayin da aka nazarci wannan ɗiyar za a ga cewa, ya yi wa wani ɗan sarki zambo ne ta hanyar siffanta shi da wata tsuntsuwa da ake kira dale. Ita dale akan gan ta ne lokacin kaka. Ta kasance nau’i biyu. Akwai ja mai baƙi-baƙi ga kai, akwai kuma mai launin ɗorawa da baƙi-baƙi ga kai. Ita dalen ba a ganin ta sai lokacin da amfanin gona ya kai. Saboda halayyarta ne ya kamanta ɗan sarkin da ita, domin bai amfana wa kowa komai. Hasali ma idan wani abun alheri ya zo da ya kamata ya ba al’ummarsa, sai ya yi sama-da-faɗi da shi.

4.3.5 Roƙo

Akan sami wasu ɗiyan waƙoƙinsa da Sa’idu Faru yakan yi bara ko ya roƙi ubangidansa wani abu kai tsaye cikin hikima. Wannan wata azaliyya ce da ta keɓanta ga makaɗan sarauta, wato su bayyana abin da suke so daga ubangidansu kai tsaye ba tare da wani sakaye-sakaye ba. Shi ma Malamin Waƙa ya aiwatar da shigen wannan a inda yake cewa:

Manyan ma’aikatan gwamnati,

Manyan ma’aikatan N.A.,

Almajirinku na aike,

Don bisa gare ku Allah ya shiya mana asiri,

Na roƙe ku in da hali,

Ku zam shirya muna kujera mui Haji.

Na yi mafarki nai sallah Makka nai ɗawafi,

Kuma na rungumo hirami

Da makaru a fuskoki,

An ce mani Alhaji baitul fasali kake,

Wanga mafarki ya Allah ya nufa a shirya shi,

Ya zam haka.

(Sa’idu Faru: Waƙar Sarkin Kudu Macciɗo).

A waɗannan ɗiyan waƙar, za a ga mawaƙin ya fito ƙarara ya nuna buƙatarsa tare da ayyana dalilinsa wanda ya kasance mafarkin da ya yi da yake son a taimaka masa ya zama gaskiya. Za a iya cewa, ma’aikatan gwamnati da ya roƙa ai suna cikin rukunin talakawa. Lamarin a wancan lokacin ba haka yake ba. A daidai lokacin ‘ya’yan ahalul falala ake damƙa wa aikin hukumar En-e da na gwamnati.

4.3.6 Koɗa Kai

Sa’idu Faru fasihin makaɗan fada ne, musamman idan aka yi la’akari da wuraren da yakan wasa kansa ta hanyar nuna ƙwarewarsa wajen tsara waƙa fiye da sauran makaɗan fada. Kuma yakan yi hakan ne a ciki ɗiyan waƙoƙin da ya ƙulla wa maigidansa Sarkin Kudu Macciɗo. Kasancewar sa makaɗin fada, ya shahara wajen amfani da wasu halaye da siffofi na ɗan’adam, ya ƙaga su ga wani abu wanda ba mutun ba, wato abin da ake kira mutuntarwa. A waƙar da ya yi wa Sarkin Kudu macciɗo cewa ya yi:

Nan na bi Gusau sai niw wuce,

Kuma nab bi Kwatarkwashi niw wuce,

Kuma nib bi ta Tcahe ina gudu,

Can na kusa kai wa Zariya,

Sannan Daudu ni kau sai nit tsaya.

Sai Sarkin Zazzau nig ga nay,

Ya ce man Muhamman Sarkin Kudu.

Sai nis saki hanya nig gabas.

Can na taɓa ‘yar tafiya kaɗan,

Sai ni ishe suda na kiwo,

Tana barka Sarkin Kudu,

Allah rai ya daɗe Sarkin Kudu,

Allah sabbinane na Ahmadu,

Allah shi ƙara mai nasara.

Na ce suda waƙa akai,

Ta ce lalle waƙa ni kai,

Waƙar Mamman Sarkin Kudu,

Waƙar nan da Ɗan’umma ya yi mashi.

Baicin uwar tsuntsaye nike,

In da kamar mulkina nikai,

Da nai mai wasiƙa ya yi min kiɗi,

San nan ni kau sai niw wuce,

Can na taɓa ‘yar tahiya kaɗan,

Sai ni iske burtu na kiwo,

Yana barka Sarkin Kudu,

Rai ya daɗe Sarkin kudu,

Allah sabbinane na Amadu,

Allah shi ƙara mai nasara,

Na ce burtu waƙa akai,

Ya ce lalle waƙa nakai,

Waƙar Mamman Sarkin Kudu,

Waƙar nan da Ɗan’umma ya yi mashi.

In na yi ta za ni wurin kiwo,

In na so abinci sai na rufe.

A cikin waɗannan ɗiyan waƙar, za a fahimci cewa mawaƙin ya yi amfani da adon harshe ne domin jaddada cewa ba ya yi wa kowa kiɗa da waƙa sai sarakuna da waɗanda ke da alaƙa da fada. Ga shi har da tsuntsaye sun san da haka. A ɗaya ɓangaren kuwa yana ɗaukaka waƙar da ya yi wa Sarkin Kudu, wadda sakamakon yadda ta tsaru ta yi armashi, har tsuntsaye na maganar waƙar.

Waƙar da ya yi wa Sarkin Sudan Na Wurno Alhaji Shehu Malami, ita ma wata hujja ce mai ƙarfi da ke tabbatar da kasancewarsa makaɗin sarauta ne na gani-da-faɗa wanda sauyin zamani bai juya shi ba. A wasu ɗiyan waƙar, yana cewa:

Gindin Waƙa: Muzakkarin sarki ɗan Audu,

Abin biya Shehu na Ali.

 

Jagora: Ɗan talakka komai yac cika huska,

Sa’idu ni ba ni kiɗa mai, .

Jagora: Ɗan talakka komai ya aje ƙarhe,

Sa’idu ni ba ni kiɗa mai.

Da duban waɗannan ɗiyan waƙar za a ga ya fito fili yana jaddada cewa shi ba makaɗin talakawa ba ne, kuma komai bajintarsu da ƙwazo da kuma uwa-uba mallakar tamani (jikkunan kuɗaɗe) ba zai yi musu kiɗa da waƙa ba.

4.4 Sarrafa Harshe a Cikin Waƙoƙin Saidu Faru

4.4.1 Ƙarangiya ko Gagara-gwari

Makaɗan fada, musamman waɗanda suka fito daga yankin da ke cikin farfajiyar tsohuwar Daular Zamfara, wato yakin da ke cikin Masarautar Bakura da Zurmi da abin da ya gangara Sabon Birnin Gobir har zuwa Dacaɗi da sauransu, sun fi takwarorinsu da ba ‘yan asalin yankin ba ne wajen mallakar harshen Hausa da iya sarrafa shi. Sa’idu Faru ya yi wa takwarorinsa da suka yi zamani ɗaya da shi fintinƙau ta fannin sarrafa sautukan Hausa masu bugun juna ta hanyar maimaita su a cikin ɗiyan waƙa domin nuna ƙwarewarsa a harshen da yake waƙa da shi (Hausa). Ana kyautata zaton cewa, sukan yi amfani da wannan hikimar ne domin kawar da wani lamarin da ke ci wa sarki tuwo a ƙwarya ta yadda zai koma ga hayyacinsa har ya yi ƙoƙarin fahimtar yadda aka yi luguden kalmomin da fahimtar ƙunshiyarsu. A duba misalin inda Sa’idu Faru ke cewa:

Yaro in taƙamar salon magana kaka yi,

Ce tsare tsara,

Ta hi tsantsamin tsantsara,

Ko tsattsame tsari,

Tsaf ga tsamiya.

Tunkuɗa tunku cikin tukar rukuɓu,

Tukuɗin Tumba yai tuɓus,

Tumba taho yau da ke da taɓo,

Da taɓo da’yat tuɓus..

(Sa’idu Faru: Waƙar Sarkin Kiyawa na Ƙaura).

Yayin da aka duba waɗannan ɗiyan waƙar za a tarar cewa Sa’idu Faru ya yi luguden sautukan Hausa kamar: tsa, tu, ɓa, ɓo, ɓu, ɗa, ɗi, da kuma ɗu, domin ya nuna ya naƙalci harshen Hausa da yake waƙa da shi. Mai nazari zai iya yin tambaya game da hujjar kawo wannan dalili? Hujja ita ce, tun lokacin da addinin Musulunci ya shigo ƙasar Hausa, a fada ya soma zama da kafa harsashe. Wannan ne ya sa Sarakunan ƙasar Hausa suka kasance malamai musamman bayan jahadin Shehu. Hasali ma sun kakkafa makaratun ilimi (zaure) inda ake koyar da fannonin addini da luggar Larabci da ake fassarawa cikin harshen Hausa. Wannan ne ya sa har gobe tsofaffin kalmomi da hikimomin Hausa sun yanke cibiya a makarantun zaure, ta la’akari da irin hikimomin da ke ƙunshe cikin Muƙamatul Hariyri.

4.4.2 Dangantakar Kalmomi

Ta wannan haujin za a ga cewa makaɗan sarauta sun sha bamban da na jama’a ta fuskar zaɓen kalmomin da suka dace da ke da dangantaka da juna tare da tsara su wuri ɗaya cikin waƙarsu. Makaɗa Sa’idu Faru shi ne kan gaba a wannan fagen. Allah ya ba shi basira da hikimar zaɓen kalmomi masu dangantaka da juna. Yakan kuma tsara su a wuri ɗaya cikin waƙarsa. Misali, yana cewa:

Ihihiya da kunkuru shawara guda sukai.

Bushiya da beguwa shawara guda sukai.

Kurciya da hasbiya shawara guda sukai.

Bubukuwa da jinjimi shawara guda sukai.

(Sa’idu Faru: Waƙar Muhammadun Muhammadu).

Ta la’akarida waɗannan ɗiyan waƙar za a ga cewa ya kawo jerin halittu da suke da dangantaka da juna ta siffofin yanayin halittarsu.

5.1 Sakamakon Bincike

Daga abin da ya gabata dangane da wannan nazari, ya fayyace mana tabbatuwar Makaɗa Sa’idu Faru a matsayin sahihantaccen makaɗin sarauta na gwadi da ya tsayu wajen kiɗan sarauta da sarakuna a manyan gidaje sarauta har ma da ƙananansu da ke farfajiyar ƙasar Hausa. Sauye-sauye zamani da ɓullowar siyasar dimokuraɗiyya da kwaɗayin neman tara abin duniya bai sa ya bar turbar iyaye da kakanni ba.

Irin wannan dogiya tasa, da ra’ayin mazan jiya sun bambanta shi da takwarorinsa da suka yi zamani tare har ya zamanto bai taɓa yi wa wani mutun waƙa ba idan ba jinin sarauta ba ne. Hasali ma ko jinin sarauta sai wanda ke riƙe da wani muƙamin sarautar gargajiya. Ya bambanta da mawaƙa irin su Alhaji Musa Ɗanƙwairo da suka kasance cikin zango guda da shi, wanda ya koma yana karɓar gayyatar jama’a domin rera musu waƙoƙi.

Haka kuma, an fahimci sarakuna na rungume da makaɗansu ne sakamakon yadda suke tsara musu waƙoƙi, wanda ke zama sanadin daɗa ɗaukakuwarsu a idon duniya. Wannan kan auku ne, ta hanyar yadda makaɗan ke ambaton su da kyawawan halaye da ɗabi’u, waɗanda kan fito da sunayensu fili fiye da kima. Da haka ne sukan sami ƙwarin guiwar gudanar da harkokinsu na mulki ba tare da kasala ko tsoro ba, sakamakon zuga da kirarin da mawaƙansu ke yi musu, tare da tunatar da su tarihin iyaye da kakanninsu, musamman dangane da kyawawan halayensu kamar kyauta, haƙuri, ƙwazo da juriya.

5.2 Kammalawa

Waƙoƙin fada sun kasance wata maƙerar sarrafa harshe da luguden kalmomin fasaha. Haka kuma, suna mazaunin wata makaranta da ke koyarwa ko cusa waɗansu halayen ƙwarai da kuma ƙarfafa guiwa ga waɗanda ake yi wa waƙoƙin, da ma sauran masu sauraro. A ɓangare guda kuwa, suna da matsayin rumbun adana al’ada da tarihi. Makaɗa Sa’idu Faru ya shahara a waɗannan lamura a matsayinsa na makaɗin fada na yankan shakku. Hasali ma, shi ne babban misali lamba ta ɗaya idan ana batun kiɗan sarauta.

Manazarta

Abba, M. da Zulyadaini, B. (2000). Nazari Kan Waƙar Baka Ta Hausa. Zaria: Gaskiya Corpora-Tion LTD.

Abubakar, A.T. (2015). Ƙamusun Harshen Hausa. Zaria: Northern Nigerian Publishing Company Limited.

Ammani, M.C. (2019). Nazarin Awon Baka Da Aiwatarwa Da Harshen A waƙoƙin Nafi’u Yakubu

Baba Katsina. Juzu’i Na Biyu. (Ratayen Matanonin Waƙoƙin Da Aka Yi Nazari A Kansu). Kundin Bincike Da Aka Gabatar Domin Cikasa wata Ƙa’ida Ta Neman Digiri Na Adabin Hausa, A Sashen Harsunan Nijeriya Jami’ar Bayero Kano.

Bango, A. & King, A.B. (1986). “ An Introduction to Life and Works of Abubakar Akwara (C. –1876-1962)”. Seminer Paper. Zaria: Ahmadu Bello University.

Bello, G. (1976). “Yabo, Zuga da Zambo a WaƘoƙin Sarauta”. Harsunan Nijeriya, Vol. VI: 21-34.

Bunza, A.M. (2009). Narambaɗa. Lagos: Ibrash Islamic Publication Centre LTD.

Bunza, A.M. (2014). In Ba ka San Gari Ba Saurari Daka: Muryar Nazari Cikin Tafashen Gambo. Cairo: Elkods Printing House.

Ɗangambo, A. (1984 ). Rabe-Raben Adabin Hausa da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Kano: Trimph.

Funtuwa, A.I. da Gusau, S. M. (edt) (2011). Waƙoƙin Baka Na Hausa. Kano: Century Research And Publishing Limited.

Gital, G. M. (1984). “Adabin Baka”. Maƙalar da aka gabatar a Kwalejin Kimiyya da Fasaha, Bauchi.

Gusau, S. M. (1988). “Waƙoƙin Makaɗan Fada: Sigoginsu Da Yanayinsu, Musamman A Ƙasar Sakkwato. Juzi’i Na Ɗaya Da Sharhi. Kundin Binciken Da Aka Gabatar Domin Samun Shaidar Digiri na Ɗaya.

Gusau, S. M. (1993). Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Kaduna: Fisbas Media Services.

Gusau, S. M. (1996). Makaɗa Da Mawaƙan Hausa Na 1. Kaduna: Ɗab’in Fisbas Media Services.

Gusau, S. M. (2002). Salihu JankiɗI Sarkin Taushi. Kaduna: Baraka Publishes Limited.

Gusau, S. M. (2008). Waƙoƙin Baka A Ƙasar Hausa: Yanaye-Yanayensu da Sigoginsu. Kano: Benchmark Publishers Limited.

Gusau, S. M. (2009). Diwanin Waƙoƙin Baka: Zaɓaɓɓun Matanoni na WaƙoƘin Baka na Hausa.Kano: Century Research and Publishing Limited.

Gusau, S. M (2011). Adabin Hausa A Sauƙaƙe. Kano: Century Research and Publishing Limited.

Gusau, S. M. (2014). Diwanin Waƙoƙin Baka, Juzu’i Na Biyu. Kano: Century Research and Publishing Limited.

Gusau, S. M. (2014). Waƙar Baka Bahaushiya (The Hausa Oral Song). Kano: Published for Bay-Ero University.

Gusau, S. M. (2015). Audu Karen Gusau. Kano: Century Research and Publishing Limited.

Gusau, S. M. (2016). Makaɗa Da Mawaƙan Hausa. Littafi Na Biyu. Kano: Century Research and Publishing Limited.

Gusau, S. M. (2018). Diwanin Waƙoƙin Baka: Matanonin Wasu Waƙoƙin Alhaji (Dr.) Mamman Shata Katsina. Kano: Century Research and Publishing Limited.

Gusau, S. M. (2019). Diwanin Waƙoƙin Baka, Juzu’i Na Huɗu: Wasu Waƙoƙin Alhaji Musa

Ɗankwairo Maradun (1909-1991) Sarkin Kiɗan Sarkin Maradun Jahar Zamfara. Kano: Century Research and Publishing Limited.

Gusau, S. M. (2020). Diwanin Waƙoƙin Baka Juzu’i Na Biyar: Matanonin Wasu Zaɓaɓɓun Waƙoƙin Makaɗan Baka. Kano: K.d.G.

Ibrahim, M.S. (1983). Kowa Ya Sha Kiɗa. Ibadan: Longman Nigeria.

Sa’id, B (edt) (2006). Ƙamusun Hausa. Kano: Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Yahaya, A. B. (1997). Jigon Nazarin Waƙa. Kaduna: FISBAS MEDIA SERVICE.

Yahaya, A. B. (2001). Salo Asirin Waƙa. Kaduna: FISBAS MEDIA SERVICE.



[1] Kotso abin kiɗa ne na makaɗan sarauta. Ya so ya yi kama da kalangu, amma shi fuska ɗaya kawai ake rufewa, a kuma kaɗa shi da hannu. Sa’idu Faru yana daga cikin sahun makaɗan da suka fi gwanancewa wajen kiɗan kotso. Ƙwararru kuwa sun haɗa da Ibrahim Narambaɗa da  Musa Ɗankwairo.

[2] [Keɓantacciyar tattaunawa I. Muhammad, 14 ga watan Yuli, 2024] (A lokacin yana matsayin Ɗanmadamin Birnin Magaji)

Sa'idu Faru

Post a Comment

0 Comments