Citation: Mukoshy, J.I. and Abubakar, B. (2024). Gudunmuwar Fesbuk ga Gyaran Al’umma. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 397-405 www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.050.
GUDUNMUWAR FESBUK
GA GYARAN AL’UMMA
Jamilu Ibrahim
Mukoshy
Department of
Nigerian Languages
Usmanu Danfodiyo
University, Sokoto
Bashar Abubakar
Shiyar Magaji,
Tangaza Local Government Area, Sokoto State
Abstract: This paper is aimed at identifying the
dynamics of imparting moral uprightness in the society through Facebook.
Considering the fact that, social media Technologies are today taken as avenues
of immorality, including Facebook. On the contrary, this paper argues that the
good side of Facebook cannot be overemphasized. There are numerous Facebook groups
that are aimed at moral upbringing. The paper identifies different forms in
which social media messages are broadcasted on Facebook, including text, audio,
video, and pictures. In all these categories, information is spread on morality
and uprightness to numerous group members. The paper concludes that Facebook groups
play important roles in disseminating impactful messages to the society
Fitilun Kalmomi: Kafofin Sadarwa, Fesbuk, Gyara,
Al’umma, Tarbiyya
Gabatarwa
Fesbuk ɗaya ce daga cikin kafofin sadarwa na zamani. Tana ɗaya daga cikin hanyoyin sadarwa na walwala (social network
sites). Tarihi ya nuna cewa an samar da Fesbuk tun a shekarar 2005 (Mukoshy,
2015). Tun lokacin da aka samar da wannan shafin jama’a da dama, maza da mata,
yara da manya suna amfani da shafin wajen gudanar da hira da tattaunawa da
musayar ra’ayoyi a cikin harshen Hausa. Tun daga wannan lokaci, masana da
manazarta sun shiga aiwatar da bincike-bincike da ayyuka da dama a kan wannan
kafa. Galibi ayyukan sun fi mayar da hankali ga illoli da matsaloin kafafen
sadarwa na walwala, duk da yake waɗannan kafafe suna da amfani ga
rayukan al’umma. A kan haka, wannan takarda ta bibiyi kafar sadarwa ta Fesbuk
domin lalubo wani sashe na amfaninta ga al’umma. Bayan bitar ayyuka muhimmai
masu alaƙa da
wannan bincike, takardar ta yi bayani a kan tarbiyya da hanyoyin bayar da ita.
Bugu da ƙari,
takardar ta yi bayani a kan sadarwa, ta hanyar bayar da ma’anar sadarwa da alaƙar sadarwa da tarbiyya. A ƙarshe, maƙalar ta yi bayani a kan wasu saƙonni da suke kai-komo a wayoyin
salular Hausawa waɗanda dukkaninsu na gyaran
tarbiyya ne.
1.1
Bitar Ayyuka Masu Alaƙa
da Wannan Bincike
Kawo yau, masana da manazarta
sun ba ga gudunmuwarsu ta hanyoyin daban-daban a kan abubuwan da suka shafi
intanet. Wasu fitaccin ayyuka da sun haɗa da Umar (2012) ya gudanar da
bincike a kan Saƙonnin GSM
a Wayar Salular Hausawa. Yayin da Muksohy (2015) ya yi bitar keɓaɓɓun kalmomin intanet da amfaninsu
a nazarin Hausa. Sani (2021) ya yi bincike a kan tasirin zamani a kan al’adun
Hausawa a duniyar intanet. A wani aiki na Sani da wasu (2022) sun kalli tasirin
kafafen sada zumunta ga tashintashinar Jihar Zamfara. Haka kuma, aikin Makuwana
(2011) ya waiwayi yaɗuwar harshen Hausa cikin
intanet. Shi kuwa Sani (2015) ya yi nazari a kan yadda ake saɓa ƙa’idojin
rubutun Hausa a Facebook. Muhammad (2004) ya bitar tasirin shirin game duniya
(globalization) kan harshen Hausa, yayin da Almajir (2008) ya yi aiki a kan
harshen Hausa da matsayinsa a hanyar sadarwar ta intanet. Bugu da ƙari, akwai ayyukan da aka
gudanar masu alaƙa da
bayar da tarbiyya. Daga cikinsu an ci karo da aikin Giwa (2012) wanda aka yi a
kan gurbin tarbiyya a cikin tatsuniyoyin Hausa. Sai aikin Yahaya (2018) wanda
ya kalli karin maganganun Hausa a matsayinsu na makarantar tarbiyyar Hausawa
manya da ƙanana. Shi kuwa Ahmad (2013) ya gudanar da
bincike a kan tasirin wayar salula ga taɓarɓarewar
tarbiyyar ‘ya’yan Hausawa”.
1.2
Tarbiyya da Hanyoyin Bayar da ita ga Bahaushe
Dangane da ma’anar ‘tarbiyya’,
Bargery (1993:553) ya nuna cewa, “tarbiyya ita ce ilmi ko horo zuwa ga ɗabi’u nagartattu”. Alhassan da wasu (1982:5) sun bayyana
tarbiyya da cewa, “tarbiyya ita ce renon halayen abin da aka haifa domin ya
zama nagari kuma ya iya kama kansa idan ya girma”. Bugu da ƙari, Sa’id da wasu (editoci) a Ƙamusun Hausana Jami’ar Bayero (2006:425) sun bayyana tarbiyya
da “koyar da hali nagari”.
Waɗannan
ma’anonin suna da alaƙa
da juna domin dukkansu sun nuna cewa tarbiyya ta shafi reno ko horo ga kyawawan
ɗabi’u da hani ga akasinsu.
Bahaushe yana da sanannun hanyoyin bayar da tarbiyya na kansa, waɗanda kuma su ne na gargajiya. Muhimmai daga cikin hanyoyin
na gargajiya su ne (a) Tatsuniya (b) Waƙe-waƙe (c) Iyaye da dangi, (Yahaya,
da wasu 2007).
1.3
Hanyoyin Bayar Da Tarbiyya Na Zamani
A dalilin cuɗanya da baƙin
al’ummu, Hausawa sun samu sababbin hanyoyin bayar da tarbiyya waɗanda ake kallo a matsayin hanyoyin bayar da tarbiyya na
zamani. Fitattu daga cikinsu su ne makaranta da kafafen yaɗa labarai da kuma intanet. Ga ƙarin bayani a kan su:
1.
Makaranta: Babban
reshe ne da ake koyon tarbiyya a duniya baki ɗaya.
A Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero na Sa’id da wasu (editoci)
(2006:322) an bayyana cewa: “Makaranta wuri ne da ake koyon ilmi”. Shi kuma
ilmi Hausawa suna yi masa kirari da cewa: “Shi ne gishirin zaman duniya”.
Muhimmancin ilmi ga rayuwar ɗan Adam ya fi gaban misali.
Akwai kyakkyawar dangantaka tsakanin malami da ɗalibi
wajen samar da ilmi mai amfani da kuma tarbiyya tagari. A taƙaice, gudunmawar makarantu wajen
koyar da tarbiyya sun haɗa da:
i.
Koyar da ilmi da kawar da jahilci.
ii.
Koyar da ladabi da biyayya da ɗa’a
da halaye masu kyau.
iii. Gargaɗi da biyayya ga mahaifa, girmama na gaba da son juna.
iv. Ishara da
riƙa aikata ayyuka nagari da barin
waɗanda ba su da kyau.
2.
Kafafen Yaɗa Labarai: Wani jigo ne mai tasiri a
rayuwar al’umma ta yau da kullum shi ne kafar yaɗa
labarai. Da yake an halicci ɗan Adam da son ji da kuma bayar
da labarai, sai wannan ɗabi’a ta kasance ɗamfare da kafafen yaɗa labarai (wato rediyo da
talabijin da kuma jarida) (Yakasai,
2019). Kafafen yaɗa labarai suna taka muhimmiyar
rawa wajen gyara tarbiyya. Akwai shirye-shirye daban-daban da ake yi a kafafen
yaɗa labarai waɗanda suka shafi tarbiyya. A gidajen rediyo da na talabijin
ana sanya tafsirin Alƙur’ani
da wa’azoji da karatun littafai waɗanda malamai daban-daban suke
gabatarwa. Sannan ana gabatar da shirye-shirye daban-daban waɗanda suka shafi ilmantarwa da wayar da kai tare da ba da
shawarwari kan abubuwan da suka dace a rayuwa, domin a riƙa aiwatar da su, da kuma waɗanda ba su dace ba domin a guje su. Wasu kafafen yaɗa labarai sukan ware wani lokaci domin shirya wasannin
kwaikwayo waɗanda suke ɗauke da darussan gyaran tarbiyya. Misali, Sashen Hausa na
gidan rediyon Docibelle (Deutsche Welle) suna da shirin wasan kwaikwayo mai
suna ‘Taɓa-ka-lashe’. Shiri ne na wasan
kwaikwayo mai ƙayatarwa,
domin yana wayar da kai da kuma tarbiyantarwa.
3.
Intanet: A wani
mashahurin Ƙamusu na
Ingilishi mai suna Merriam Webster
Online Dictionary (2023) an kawo kalmar intanet (internet a Ingilishi) aka
bayyanata da cewa:
Ingilishi: An electronic communications network that
connects computer networks and organizational computer facilities around the
world.
Fassara: Intanet kafar sadarwa
ce ta na’urorin lantarki wadda take haɗa hanyar sadarwa na kwamfutoci
ga manyan taskokin kwamfuta na duniya.
Ra’ayoyin masana da manazarta
irin su Muhammad (2004) da Almajir (2008) da Umar (2012) da Mukoshy (2015) da
kuma na Yakasai (2019) sun yi kunnen
doki game da ma’anar intanet. Wannan bincike ya bi sawun waɗannan ma’anoni, ya ba da ta sa gudunmawa ga ma’anar intanet
da cewa:
Intanet kafar sadarwa ce ta
zamani wadda take ba da damar taskace bayanai da kuma sadar da su zuwa ko’ina a
faɗin duniya cikin ƙanƙanin lokaci.
1.4 Waiwaye Kan Hanyoyin Sadarwa
Na Walwala
Mukoshy (2015:102-103) ya
bayyana kafafen sada zumunta da cewa, shafuka ne na intanet da tsarin na’urori
waɗanda suke ba masu amfani da su
damar sadar da bayanai tsakaninsu ta hanyar hira da tattaunawa da muhawara ko
musayar ra’ayi a kowane lokaci kuma daga ko’ina a faɗin duniya. Irin waɗannan shafuka, galibi suna ba da
damar sadarwa da aiwatar da hulɗa ko mu’amala ta musamman
tsakanin masu amfani da intanet. Bugu da ƙari,
waɗannan shafukan suna ba da damar
sadarwa da aiwatar da hulɗa ta musamman tsakanin ‘yan uwa
da abokan arziki. A wasu lokuta da ana ƙulla
dangantaka wadda dauri ta katse tsakanin tsofaffin aminai tare da ƙulla sabuwar abokantaka. Wannann
ya nuna cewa, kafafen sadarwa na walwala suna ɗaya
daga cikin hanyoyin da ake iya amfani da su wajen inganta mu’amalar al’umma. Waɗannan kafafe suna daɗa yawaita, domin ana samun ƙarin sababbi a-kai-a-kai. Wasu
daga cikin sanannu daga cikinsu sun haɗa da Fesbuk (Facebook) da
Tiwita (Twitter wanda aka sauyawa suna zuwa X) da Was’af (WhatsApp)
da Insitagaram (Instagram) da Tikitok (TikTok) da Teligiram (Telegram)
da sauransu.
Bincike-bincike da ayyuka da
dama sun fi mayar da hankali ga illoli da matsaloin kafafen sadarwa na walwala,
duk da yake waɗannan kafafe suna taka rawa
sosai wajen sadarwa da ilmantarwa da ma koyar da tarbiyya. Haka kuma, bayan
zumunci da dangantakar da suke ƙullawa,
ana sadar da bayanai daban-daban masu koyar da tarbiyya a kansu. Malamai da ɗalibai da manazarta da dama suna sadar da rubuce-rubuce masu
faɗakarwa da ilmantarwa da
tarbiyyantarwa da kuma wayar da kai a cikin waɗannan
kafafe. Irin waɗannan saƙonni da bayanai suna nan suna
zagayawa tsakanin masu amfani da irin waɗannan kafafen na sada zumunta.
Sau da yawa ana samu darussa da ilmuka a kan hukunce-hukuncen addini a sauƙaƙe a waɗannan kafafe. Wannan yana nuna
cewa idan aka yi kyakkyawan amfani da waɗannan kafafe yadda ya dace,
lallai suna taimaka wa sosai wajen koyar da tarbiyya.
Bayan
Shafukan sadarwa na walwala, akwai kuma shafuka koyarwa (Educational websites).
Shafuka ne da aka tanadar kacokan domin koyar da ilmuka daban-daban. Ilmukan
suna iya kasancewa na addini da faɗakarwa da wayar da kai da kuma zamantakewa ta yau da
kullum. Daga cikin irin waɗannan shafukan akwai shafin http://www.imzakirnaik.com ƙarƙashin kulawar “Islamic Knowledge
Center of Education”. Wannan
shafin yana kawo nasihohi a harshen Ingilishi domin wayar da kan jama’a kan haƙƙoƙin Allah (SWT) da sauran mutane. Haka kuma, ana amsa
tambayoyin da suka shafi rayuwa. Haka zalika, a zauren ana amfani da hotuna
(pictures) masu ɗauke da bayanai na Musulunci
domin inganta rayuwa. An ƙirƙiri wannan shafi a shekarar
1991, aihini daga Islamic Research Foundation (IRF) Mumbai Indiya (India). Yana
da jagorori masu kula da shi da kuma mambobi fiye da dubu ɗari shida.
Bugu
da ƙari, akwai kuma shafukan bulog: Bulog kalma ce da
aka aro daga Ingilishi aka hausantar da ita. Asalin kalmar ita ce ‘Blog’. Ga ƙarin bayanin da aka samo a kan kalmar daga http://en.m.wikipedia.org
ranar, 24-08-2023.
Ingilishi: A blog (a truncation
of “weblog”) is a discussion or informational website published on the World
Wide Web consisting ofdiscrete, often informal diary-style text entries
(posts).
Fassara: Bulog (yanki ne na kalmar “weblog”) na nufin shafin da ake
tattaunawa ko wallafa saƙonni a
kan intanet waɗanda ra’ayi ne na wani, ba bayani a hukumance ba.
Tun a
wajajen shekarar 1990 bulog ya fara bayyana a intanet, a wasu lokuta mutum ɗaya ne
ke buɗa abinsa ya kula da shi.Wasu bulog kuwa, mallakar haɗakar
jama’a ce masu manufa iri ɗaya. Shafin Wikipedia ya wallafa wani bayani ranar 16 ga
Fabrairu 2011, inda ya tabbatar da cewa an samu ƙiyasin sama da mutane miliyan 100 masu amfani da blog a faɗin duniya a wannan lokaci, (https://en.wikipedia/wiki/historyofbloggin). Misalin bulog da ake samar da
tarbiyya shi ne
Zauren
Fiƙhu. Wannan bulog ne da aka tanadar
musamman domin haɓaka ci gaban addini a zukatan
matasa da kuma haɓaka soyayyar Annabi (SAW) da
iyalan gidansa da Sahabbansa da Salihan bayin Allah, tare da biyayya da
girmamawa. Bulog na faɗakarwa da amsa tambayoyin
addinin Musulunci da wasu al’amurrun rayuwa na yau da kullum. An ƙirƙiro wannan bulog a shekarar 2013 a bisa adireshin http://www.zaurenfiƙhu.blogspot.com. Akwai fiye da mambobi 359 da
suke ziyartar wannan bulog a-kai-a-kai.
1.5
Taƙaitaccen Tarihin
Shafin Fesbuk
Fesbuk asalinsa wani ɗalibi ne ɗan ƙasar Amurka mai suna “Mark
Zuckerberg” ya ƙirƙiro shi a matsayin shafi domin
sada zumunta tsakaninsa da aminansa da ‘yan uwa da kuma abokan arziki. Ya ƙirƙiro shafin a shekarar 2005 (Mukoshy, 2015: 98) tare da
tallafin ‘yan ajinsu da suke ɗaki ɗaya a makaranta tare da goyon bayan ɗaliban Jami’ar Haɓard (wato makarantarsu).
Abokansa da suka tallafa masa wajen gina shafin su ne: Andrew McCollum da Chris
Hughes da Dostin Moskoɓite. Ya yi wannan ƙoƙari ne tun yana shekarar karatu ta biyu a Jami’a. Shafin ya
haɓaka har wasu kamfanonin ƙasashen ciki da wajen ƙasar Amurka suka saka hannun
jarinsu a cikin wannan sabon shafin mai farin jini. A taƙaice, tun kafa shafin Fesbuk har
zuwa yanzu sai daɗa bunƙasa yake yi tare da ƙirƙiro sababbin abubuwa waɗanda can farko bai fito da su
ba, (Usman, 2015).
Fesbuk kafar sadarwa ce a
intanet domin sada zumunci, wannan kafa tana ba da dama ga tsofaffi da kuma
sababbin abokai su yi zumunci (a rubuce da hotuna da bidiyo). Mafi yawan masu
mu’amala da shafin suna da bayanai da hotuna game da sunayensu da wuraren aiki
ko makaranta da abubuwan sha’awa a rayuwa. Ta haka ne, mutum kan tattauna da
abokinsa ko ƙawarta
kai tsaye (online) ko kuma a bar saƙo.
Ta haka ake ƙulla
zumunci tsakanin al’ummu daban-daban. (Yakasai, 2019:178). Saboda haka, Fesbuk
kafa ce ta mu’amala daga nesa ta hanyar hira da gaisuwa ta hanyar aika saƙonnin rubutu (texɓt messages) da hotuna (pictures) da sauti (sound) da bidiyo
(videos), (Usman, 2015).
Bayanai sun nuna cewa fiye da
rabin masu mu’amala da intanet sun mallaki shafi a Fesbuk, ciki har da kafafen
yaɗa labarai na rediyo da
talabijin. Misali: www.nta.news/facebook.com da da kuma www.rimaradio/newsroom/facebook.com da sauransu. Fesbuk ya zama
tamkar rigar zamani a sa ki a huta. Kamfanoni da masana’antu da ma’aikatu da
makarantu da jama’a da cibiyoyi masu zaman kansu duk suna shiga Fesbuk domin
yayata manufofinsu da tallata ayyukansu da hajojinsu.
1.6
Hanyoyin Bayar da Tarbiyya na Fesbuk
Fesbuk kafa ce ta sadarwa da za
iya kira “Hantsi leƙa gidan
kowa” ko kuma a kira ta “Ruwan dare game duniya”. Wannan ba abin mamaki ba ne
idan aka yi la’akari da yadda Fesbuk ta yi ruwa ya yi tsaki wajen haɗin kan al’umma masu ra’ayi ɗaya
da masu mabambantan ra’ayoyi a bisa taska ɗaya a wannan zamani. Wannan ya
nuna yadda al’umma suka rungumi kafar sadarwa ta Fesbuk a matsayin wata taska
ta adana bayanai da musayarsu tsakanin al’umma. A kan samu mutane daban-daban
masu aika saƙonni na
tarbiyyantarwa a kan Fesbuk. Bugu da ƙari,
akwai dandali-dandali masu tarin yawa a kan Fesbuk waɗanda aka tanada musamman domin tarbiyyantarwa. Kowane
dandali, akan samu wanda yake kulawa da shi (group admin). Ana iya samun
mambobi daga ɗaruruwa har miliyan a kan
dandali ɗaya, ya danganta ga irin farin
jinin dandali da manufofinsa da kuma irin bayanan da ake sakawa a cikinsa.
Akwai hanyoyi masu ɗimbin yawa da ake bi wajen inganta tarbiyya, a kan Fesbuk.Waɗannan hanyoyi sun haɗa da wa’azi daga manyan malamai
da koyar da karatun Alƙur’ani
da koyar da hadisai. Sannan akwai masana da suke faɗakarwa da wayar da kan al’umma kan zamantakewar rayuwa. Haka
kuma, akwai abubuwan da suka shafi koyon sana’o’i domin dogaro da kai da
sauransu. Duk waɗannan ana aiwatar da su ta
hanyar yaɗa bayanai da musayarsu a
samfurin hotuna da sauti da bidiyo da kuma rubutun zube. Bari mu ɗauki waɗannan ɓangarori ɗaya bayan ɗaya domin ganin irin gudunmawar da suke bayarwa wajen
tarbiyyantarwa.
1.
Hotuna
Hoto abu ne da yake ɗauke da zanen sura, (Ƙamusun
Hausa na Jami’ar Bayero, 2006). Hotuna sun kasance ɗaya daga cikin hanyoyin sadar da bayanai a kan Fesbuk. Ana
amfani da Fesbuk wajen aika saƙonni
a samfurin hotuna masu ɗauke da nasihohi da jan hankali
da faɗakarwa da kuma
hannunka-mai-sanda. Ana amfani da Fesbuk wajen aika saƙonni a samfurin hotuna da ke ɗauke da nasihohi da na jan hankali da faɗakarwa da kuma hannunka-mai-sanda. Alal misali:
Akwai
dandalin Tudun Tsira a Fesbuk. Wannan dandali ne na sada
zumunta da ake wallafa hotuna masu ɗauke da saƙon gargaɗi da tsoratarwa da faɗakarwa a lamurran rayuwa na yau
da gobe. Adireshin wannan dandali shi ne: https://facebook.com/groups/149921973635494. Dandalin yana da mambobi 75.
Jagoran da yake kula da wannan dandali shi ne Shamsudeen Muhammad Sani. An ƙirƙiri wannan dandali ranar 26 ga watan Oktoba 2015. Ga
muhimman saƙon da aka
samu mai gyaran tarbiyya a wannan dandali:
Rubutun
da yake cikin wannan hoto wata addu’a mai muhimmanci ga rayuwar kowane Musulmi.
Addu’a ce ta roƙon Allah tsari daga damuwa da ɓacin
rai da kuma cutuka. Wannan addu’a ta yi daidai da addu’ar da Manzon Allah (SAW)
ya koyar da al’umma wadda ta zo a Sahihul Bukhari 7/158. A taƙaice dai, saƙon wannan hoto yana tarbiyyantar
da al’umma kan irin muhimman abubuwan da ya kamata su roƙi Allah a duk lokacin da za su yi addu’a. Haka kuma, hoton yana nuni da
irin hali na ƙanƙantar
da kai da ya kamata ga mai roƙon
Allah.
Haka
kuma, akwai wani hoto da aka wallafa a wannan dandali mai koyar da tarbiyyanta
ga al’umma, cikin saƙo kamar haka:
Wannan
hoton yana lurar da al’umma a kan muhimmancin jajircewa da ibada a ranakun goma
na farko na watan Musulunci na Zul-hijja, kamar yadda a cikin littafin Sunan
Tirmizi 41/2. Haka kuma, hoton yana tunatar da al’umma da su nisanci aikata
munanan ayyuka a waɗannan ranaku muhimmai. A taƙaice, wannan hoton yana tarbiyyantar da al’ummar Musulmi da su kiyaye da
yin ayyuka nagari da kuma nisantar da kansu ga aikata munanan ayyuka.
Wani saƙo da aka samu a wannan dandali shi ne mai koyar da
zamantakewar aure. Ga saƙon
hoton:
Saƙon wannan hoto yana tarbiyyantar da al’ummar Hausawa ma’aurata da cewa su sutura ne tsakanin junansu. Domin kowannensu, yana rufa wa ɗan uwansa asiri a kan duk abin da ya same shi. Bugu da ƙari, hoton ya ƙara nuna cewa, ma’aurata suna rufa
wa junansu asiri ba tare da sun afka cikin ayyukan assha ba.
Wani dandalin da yake
tarbiyantar da jama’a a kafar sadarwa ta Fesbuk shi ne dandalin Mutuwa Rigar Kowa. Dandali ne da ake faɗakarwa da tunatar da al’umma a kan tuna mutuwa. An Wannan
dandalin ya kawo hotuna waɗanda suka shafi mutuwa kamar
ginar ƙabari da
yi wa mamaci salla da saka shi a ƙabari
da sauransu. Ana iya shiga wannan dandali ta adireshinsa https://www.facebook.com.postsmutuwarrigarkowa. Akwai wani hoto da aka wallafa
mai jan hankali a dandalin. Ga hoton da kuma bayanin da ke cikinsa:
Wannan
hoto yana nuna, wani mutum da ya yi sakaci da yin salla a cikin lokaci. Rubutun
cikin hoton yana cewa, mutumin ya yi alwashin yin salla gobe, mutuwa ta riske
shi yau. A taƙaice, wannan hoto yana lurar da
al’umma da su kiyaye yin salla da sauran ayyukan alheri a cikin lokaci, sannan
su nisanci jinkirta salla da ayyukan alheri.
2.
Bidiyo
Wata hanya ta aika saƙonni a kafar Fesbuk ita ce ta
amfani da bidiyo. Bunza (2018) ya
bayyana cewa ‘bidiyo’ wata na’ura ce mai ɗauke
da hoto mai magana da motsi domin isar da saƙo ga
masu ji da gani.
Ana amfani da bidiyo domin isar
da saƙo wanda ake ji kuma ake gani.
Ana aika bayanin bidiyo a kan intanet, kamar a kan Fesbuk ko imel ko a yi
musayarsa ta sauran kafofin sadarwa tsakanin wayoyi da kwamfuta da
makamantansu. A yau, Fesbuk tana cike da dandali-dandali inda akan yi musayar
bayanai a samfurin bidiyo masu tarbiyyantarwa a rayuwar Hausawa. Ga wasu daga
cikin irin waɗannan saƙonni:
Akwai dandalin Mabiya Sheikh
Aminu Ibrahim Daurawa wanda ake samu a kan adireshin https://www.facebook.com/groups/2648282428530714. Wannan dandali yana da mabiya
kimanin 765,207. An buɗe shi dandalin 30 ga Agusta
2018. An buɗe shi ne domin yaɗa darussan da Malam Aminu Ibrahim Daurawa yake bayarwa a
wurare daban-daban, kamar wuraren tattaunawa a gidajen yaɗa labarai da wuraren tafsirai da huɗubobi da sauransu. Daga cikin irin waɗannan bayanai da ake sakawa, akwai bidiyon da Malam yake
magana a kan ‘ya’ya a Musulunci. Ga saƙon
da malamin yake isarwa a ciki
A sanadiyyar ‘ya’ya mutum yana
iya tsira a gaban Allah kuma a sanadiyyar ‘ya’ya mutum yana iya taɓewa da yin hasara a gaban Allah. Duk wanda ya kyautata
tarbiyyar ‘ya’yansa ya koyar da su addini, kuma ya koyar da su sana’a suka zama
mutane nagari, kuma ya kasance sun san ciyon kansu kuma suka kasance a kan
tarbiyya ta Musulunci, to ka ga wannan ya ci jarabawar da Allah ya ba shi.
Amanar da Allah ya ba shi ta ‘ya’ya ya riƙe
ta. Duk mutumin da ya yi sakaci ya ƙyale
yaransa a hannun tauraron ɗan Adam ko talabijin ko rediyo
ko hannun kaɗe-kaɗe, ya ƙyale
wannan su ne za su yi saitin ƙwaƙwalen ‘ya’yansa, to ka ga wannan
ya ci amanar da Allah ya ba shi ta ‘ya’ya. Ba ruwansa da sun yi salla ko ba su
yi ba, kuma ba ruwansa da sun kai matakin shekarun balaga da sauran su. Haka
kuma, ba ruwansa da ‘ya’yansa sun balaga don ya san yanzu suna daga cikin
mutanen da hukunci ya hau kansu duniya da lahira. Wani ba ruwansa kawai idan ya
sa ɗansa makaranta idan yana cin
jarabawa, kuma ya ƙware da
Turanci. Amma ba ruwansa idan bai iya karatun salla ba, kuma bai iya Ahallari ko Ishimawi ba.
Wannan faɗakarwa ce mai muhimmanci ga iyaye da su inganta tarbiyyar ‘ya’yansu. Bugu da ƙari, iyaye su sani cewa ‘ya’yansu kiwo ne Allah ya ba su, kuma zai tambaye su yadda suka gabatar da wannan kiwon da ya ba su. wannan bayani na Malam daidai yake da hadisin Manzo (SAW) da yake cewa, “Dukkanku makiyaya ne, kuma Allah zai tambaye ku a kan abin da ya ba ku kiwo…”
3.
Rubutu
Rubutu dole ne ya kasance yana ƙunshe da abubuwa kamar haka: Na
farko ya kasance maƙasudin
rubutu shi ne ya waƙilci wani
abin da ake son a tuna. Na biyu ya kasance yana ba da wata ma’ana ga waɗanda suka san shi. Bunza (2002). Ana amfani da rubutu a
shafin Fesbuk wajen isar da saƙo,
wanda mabiya za su iya karantawa a duk lokacin da suke buƙata. Galibi ma, rubutu shi ne
hanyar da ake amfani da ita a kowane dandali domin sadarwa a Fesbuk. Haka kuma,
kowane mai amfani da Fesbuk zai iya aika saƙonsa a rubutuce, kuma yana iya karɓa saƙon
da aka rubutu masa ya karanta.
Akwai dandali mai suna Sakkwato
Birnin Shehu. A daidai ranar Laraba (30/08/2023) da misalin ƙarfe 5:12 na yamma dandalin yana
da kimanin mambobi 53,961. An ƙirƙiri wannan dandali ranar 7 ga
watan Agusta 2016 a kan adireshin https://www.facebook.com/groups/612407128940339. Aminu Be Mine, ya aiko da wani
saƙo mai faɗakarwa da hannunka-mai-sanda ga al’umma dangane da rayuwar
lahira. Ga saƙon:
A
Ranar Lahira
Abin da yake damuna kuma yake
sanya ni yin kukan zuci shi ne ban san yaushe ne zan mutu ba, kuma ban san a
inazan mutu ba, sannan ban san a kan wane aiki ne Allah zai karɓi rayuwata ba. Ya Allah ka sa mu yi kyakkyawan ƙarshe.
Wannan saƙon rubutu yana yi wa mutane
hannunka-mai-sanda dangane da rayuwar lahira. Idan mutum ya kasance yana aiki
da wannan saƙon zai
kasance bai ci haram kuma zai kasance mai bin umarnin Allah. Saƙon ya nuna cewa, duk wanda yake
tunawa da rayuwar lahira ya san cewa zai mutu, to za ka ga rayuwarsa daban take
da ta sauran jama’a.
Haka kuma, akwai dandalin Muryar
Matasa a kan adireshin https://www.facebook.com/groups/300316577256316. An samar da wannan dandali
ranar 27 ga Nuwamba 2018, kuma yana da mambobi kimanin 392,838 ƙarƙashin kulawar Zulaihat Ammer da Farhaf Nura da Ɗahiru Hassan. Wannan dandali
yana ƙunshe da bayanai masu tarin
yawa. Ana samun bayanai kan abin da ya shafi al’umma musamman matasa a yau.
Bangiss Gagare ya aiko wani saƙon
bidiyo a dandalin. Saƙon
yana faɗakarwa da jan hankali zuwa ga
matasa dangane da ‘yan siyasar ƙasar
nan, yana kira da cewa:
A gaskiya ya kamata mu tashi
matasa wannan zaɓe mai zuwa ya kamata mu san
wanda za mu zaɓa wato wanda zai jagorance mu
Musulmi ne ko Kirista ne wanda muka san zai taimaki iyayenmu kuma zai iya kawo
mana zaman lafiya a ƙasarmu
baki ɗaya. Ba wanda zai sayo mana ƙwaya da wiwi muna sha, muna
hauka ba, ya kamata a ce zaluncin da ake yi mana a Nijeriya yanzu kam ya ishe
mu, ya kamata mu riƙa tunani
mu san wanda za mu zaɓa. Muna zaɓar waɗanda ba za su taimake mu da
komai ba, waɗanda za su halakar da mu, waɗanda za su rushe tarbiyarmu da kuma al’adarmu, a gaskiya mu
sake tunani ‘yan uwana matasa don mu ne ƙashin
bayan kowace al’umma, idan mun tarbiyyantu ana iya sa ran al’ummar da ke tafe ƙasarmu ta zama nagartacciyar
al’umma.
4.
Sauti (audio)
A Ƙamusun
English-Hausa na
Newman (1990) an nuna cewa, “sauti shi ne amo ko ƙara”. Ƙarin
bayani a kan wannan ma’ana, shi ne sauti ƙara
ce ko amo da ake ji da kunne. Wannan bincike ya gano cewa a kafar sadarwa ta
Fesbuk akwai bayanan da ake yaɗawa domin tarbiyyantar da
al’umma. Ana samun irin waɗannan bayanai domin sauraro a
dandali.
Daga cikin dandalin Fesbuk da
ake samun bayanai domin tarbiyyantarwa akwai dandalin Ɓision FM 92.5. Wannan dandalin
an samar da shi tun ranar 8 ga Maris 2018. Zuwa lokacin gudanar da wannan
bincike, akwai kimanin mambobi 8,630 a dandalin. Za a iya shiga dandalin a kan
adireshin https://www.facebook.com/group/265699130635825. Wannan dandali yana ƙunshe da bayanai masu tarin
yawa. Ana samun bayanai kan abin da ya shafi al’umma musamman na nishaɗi da wayar da kai da tarbiyyantarwa da kuma faɗakarwa. Daga cikin bayanan akwai saƙon sauti wanda aka wallafa a
dandalin ƙarƙashin “Shirin Matasa” kashi na
biyu, wanda Aminu Ɗankaduna
Amanawa tare da Hauwa’u Ilyasu Garba suke gabatarwa. Ga wani daga cikin nau’in
bayanin da aka samu a dandali:
Damfara a kafofin sada zumunta
lamari ne da ke ci gaba da addabar masu amfani da waɗannan kafofin. A kullum masu damfara sai ƙara fitowa suke yi da hanyoyin
damfarar jama’a a kafofin sadarwa. To ta ya ‘yan damfara suke damfarar mutane?
Da ka ji an kira ka an ce maka daga bankin ka ne, ko kuma an rufe maka katin
ATM amma kuma suka nemi ka faɗa musu lambar sirrin (password)
ta katin, wai za a buɗe maka shi. To, wannan ɓarayi ne kuma ‘yan damfara ne da ke amfani da wannan damar
domin su cuci mutane.
Duk da yake wannan bayani ya
karkata ga faɗakarwa da jan hankali tare da
yin hannunka-mai-sanda dangane da wannan damfara da ta zama ruwan dare a
kafofin sada zumunta, amma bayanin yana tarbiyyantar da al’umma domin su
hankalta da wannan hanya ta damfara. Haka kuma, wannan maudu’in ya taimaka ainun
wajen fito da hanyoyin da ‘yan damfara suke bi domin yaudarar jama’a. Hausawa
na amfani da wani karin magana da ke cewa, “idan kunne ya ji gangar jiki ta
tsira”.
1.7 Sakamakon Bincike
Wannan
bincike ya gano irin rawar da kafar sadarwa ta Fesbuk take takawa a ɓangaren bayar da tarbiyya a zamanance ta waɗannan hanyoyi:
1.
Ana samar da tarbiyya a kan Fesbuk ta hanyar sauti da rubutu
da hoto da kuma bidiyo.
2.
Ana amfani da sautin wani malami ko wani da ya yi wani zance
mai hikima domin ilmantarwa ko tarbiyyantarwa a kan Fesbuk.
3.
Akan saka bidiyon wani sashe na wasan kwaikwayo mai nuna
wani abu na alheri ko sakamakon wani aiki maras kyau domin tarbiyyantarwa.
4.
Haka kuma, akan sanya bidiyo na malamai ko maganganun wasu
mutane masu nuni zuwa ga tarbiyya a kan Fesbuk.
5.
Akan samu tarbiyya kai tsaye idan aka karanta labarai na
hikima ko wa’azi ko gajeren jawabi musamman idan wani mai kaifin basira da
hangen nesa ya rubuta shi.
6. Ana ƙaruwa da faɗakar da iyaye da magabata da shuwagabanni da kuma malamai a rubuce domin ribanta a Fesbuk.
1.8 Shawarwari
Akwai shawarwari da wannan
takarda ta bayar domin ɗorewa da kuma samun kyakkyawar
tarbiyya a Fesbuk. Daga cikinsu akwai:
1.
Yana da kyau iyaye su riƙa binciken wayoyin ‘ya’yansu domin su san irin wainar da
suke toyawa, musamman a kafar sadarwa ta Fesbuk, domin ta ƙunshi kowane irin hali mai kyau
da maras kyau, wanda idan ba a bibiyar wayoyi da kwamfutocin yara sukan iya ɗaukar miyagun ɗabi’u alhali suna zaune a cikin
gidajensu.
2.
Malamai su riƙa
wayar da kan al’umma a kan illar bibiyar gurɓatattun
abubuwan da ke ƙunshe a
Fesbuk, tare da jawo hankalin jama’a kan muhimmancin bibiyar abubuwa nagari.
3.
Makarantu su riƙa
saka wasu darussa a shafin Fesbuk domin ƙara
wa al’umma ƙwarin
guiwar amfani da shafin ta hanya mai kyau.
4.
Cibiyoyin horarwa su ba da tasu gudunmawa domin ɗorewa da samar da ilimi da tarbiyya a Fesbuk, domin a yau
Fesbuk ta zama rigar zamani wanda bai sa ta an bar shi baya!
1.9 Kammalawa
Wannan bincike ya yi ƙoƙarin nazarin kafar sadarwa ta Fesbuk domin gano irin
gudunmuwar da take bayarwa a matsayin hanyar tarbiyyantarwa ta zamani. Binciken
ya yi nasarar gano hanyoyin da ake amfani da su wajen isar da saƙonni masu tarbiyantarwa ga
al’umma. Hanyoyin sun haɗa da amfani da hoto da bidiyo da
sauti da kuma rubutu. Binciken ya tabbatar da cewa Fesbuk tana da matuƙar muhimmanci ga al’umma, domin
ko bayan sadar da zumunta, ana aika saƙo
a kan kafar. Haka kuma, ana more wa kafar ta hanyar amfanar da kai da kuma
al’umma da saƙonni masu
tarbiyantarwa a cikinta.
Manazarta
Ahmad,
A. A. (2013). “Tasirin Wayar Salula a Kan Tarbiyyar ‘Ya’yan Hausa.” Kundin
digiri na ɗaya, Sashen Nazarin Harsunan
Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo
Sakkwato.
Alhassan,
H. da wasu (1982). Zaman Hausawa.
Kaduna: Islamic Publishers Bureau.
Almajir,
T. S. (2008). Hausa da Sadarwar Intanet. Harsunan Nijeriya, Ɓol. ƊƊI. CSNL - BUK, Kano, Nigeria.
Becker,
S., et al., (2010). Opportunity
for All: How the American Public Benefits from Internet Access at U.S.
Libraries. Washington, DC: Insititute of Mesuem and Library Serɓices. Retrieɓed from http://www.tascha.washington.edu/usimpact.
Bunza,
A. M. (2002). Rubutun Hausa Yadda Yake Da Yadda Ake Yin Sa Don Masu Koyo Da
Koyarwa. Lagos: Ibrash Islamic Publication Center.
Giwa,
A. A. (2012). “Gurbin Tarbiyya A Cikin Tatsuniyoyin Hausa.” Kundin digiri na
biyu, Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato.
Makuwana,
A. A. (2011). “Yaɗuwar Harshen Hausa Cikin
Intanet.” Kundin digiri na ɗaya, Sashen Nazarin Harsunan
Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo
Sakkwato.
Muhammad,
Ɗ. (2004). “Hausa a Duniyar Yau:
Tasirin Game Duniya Kan Harshen Hausa”. cikin Yalwa, L. Ɗ. da wasu (editoci) 2011. Studies
in Hausa Language Literature and Culture – Proceedings of the Siɗth Hausa International
Conference Organized by the Center for the Study of Nigerian Languages, Bayero
Uniɓersity, Kano, 15th – 17th December
2004. Zaria:
Ahmadu Bello Uniɓersity Press Limited.
Mukoshy,
J. I. (2015). “Keɓaɓɓun
Kalmomin Intanet Da Amfaninsu A Nazarin Hausa.” Kundin digiri na biyu, Sashen
Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo
Sakkwato.
Newman,
R. M. (1990). An English-Hausa Dictionary. New Haɓen: Yale Uniɓersity Press.
Sa’id,
B. da wasu (editoci) (2006). Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero. Zaria: Ahmadu Bello Uniɓersity Press.
Sani,
U. (2015). “Saɓa Ƙa’idar Rubutun Hausa a Facebook.” Kundin digiri na ɗaya, Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato.
Sani,
A-U. (2021). “Zamani Zo Mu Tafi: Al’adun Hausawa A Duniyar Intanet” Kundin
digiri na biyu, Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato.
Sani,
A-U., Maikwari, H.U., and Bazango, B. (2022). Zamani Abokin Tafiya: Tasirin
Kafafen Sada Zumunta ga Tashintashinar Zamfara. In Bakura, A.R. et al (eds). Tasambo
Journal of Language, Literature, and Culture, Vol. 1, Issue 1, p. 95-107
Umar,
M. M. (2012). “Nazarin Saƙon
GSM a Wayar Salular Hausawa.” Kundin digiri na biyu, Sashen Nazarin Harsunan
Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo
Sakkwato.
Yahaya,
A. (2018). “Tarbiyya a Karin Maganar Bahaushe.” Kundin digiri na biyu, Sashen
Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo
Sakkwato.
Yahaya,
I. Y. da wasu (2007). Darussan Hausa Don
Manyan Makarantun Sakandare
(Littafi Na Ɗaya). Ibadan: Uniɓersity Press Plc.
Yakasai,
S. A. (2019). Sanin Makamar Fassara.
Kaduna: Amal Printing Press.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.