TAMBAYA (129)❓
ance matan da basa rufe jikinsu ko kamshi aljanna bazasuji ba sukuma maxan da basa dage Wanda mai hukuncin su
AMSA❗
Alhamdulillah
A cikin Mi'ati Hadith (Hadisai sahihai guda 100) da malaman
hadisai suka tattara
Abu Hurairah (Radiyallahu anhu) ya rawaito hadisi sahihi
cewar Annabi (Sallallahu alaihi) yace: "Ma'asfalu Minal Ka'abaini, Minal
Izari Fin Naari"
(Bukhari da Muslim)
Fassara
Duk wanda yabar tufarsa qasa da idon sahu, ragowar za a saka
a cikin wuta
(Muttafaqun alaihi)
Kinga kenan duk namijin da ya take wandonsa da gadara, don
ya nuna shi mai wadata ne to daga kan idon sahu zuwa inda ya take a wuta za'a
babbake wannan wajen
Shi yasa zaki ga malaman Ahlus Sunnah suna taka tsantsan
basa bari wandonsu ya wuce idon sahu, a maimakon yan bidi'a da suke dinka wando
suna taka shi da duga-duginsu
Allah ya sa mu dace
Wallahu ta'ala a'alam
Subhanakallahumma
wabi hamdika ash-hadu anla'ilaha illa anta astaghfiruka wa'atubi ilayk
Amsawa
Usman Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.