TAMBAYA (121)❓
Assalamu Alaikum. Mlm mai hukuncin Wanda ya nema maganin
kasuwa
AMSA❗
Waalaikumussalam, Warahmatullahi, Wabarakatuh
✍️AMSA A TAQAICE:
(Duk wanda ya zo shiga kasuwa sai yace: "Laa ilaaha ill-allaahu waḥdahu laa shareeka lah, lah-ul-mulku wa lahul-ḥamdu, yuḥyee wa yumeetu wa huwa ḥayyun laa yamootu, bi yadi-hil-khayru, wa huwa ‛alaa kulli shay’in qadeer". Allah (Subhanahu wata'ala) zai rubuta masa lada miliyan daya (1,000,000), zai kankarewa mutum zunubbai miliyan daya (1,000,000) sannan a daga darajar sa sau miliyan daya (1,000,000). Idan kuma a gida kike business din sai ki dinga karanta: "Allahumma Arzuqni, warfa'ani, wahdini, wajburni" bayan kin dago daga Sujuda ta farko kafin ta biyu)
Bismillaahir Rahmaanir Raheem
Maganin kasuwa ko kuma neman albarkar kasuwanci, yin hakan
ba haramun bane ba matuqar an yi koyi da yanda Annabi (Sallallahu alaihi
wasallam) ya koyar
Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) yace: Duk wanda zai
shiga kasuwa sai yace: "Laa ilaaha ill-allaahu waḥdahu laa shareeka lah,
lah-ul-mulku wa lahul-ḥamdu, yuḥyee wa yumeetu wa huwa ḥayyun laa yamootu, bi yadi-hil-khayru, wa
huwa ‛alaa kulli shay’in qadeer"
Ma'ana:
"Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi daya tilo,
ba tare da abokin tarayya ba, Mulki gareShi yake, godiya ta tabbata gareShi.
Shi Ne mai rayawa, mai kashewa, rayayyeNe kuma baya mutuwa. A hannunSa dukkan
alkhairai suke kuma Shi ga dukkan komai mai Iko Ne"
Duk wanda ya fadi haka, Allah (Subhanahu wata'ala) zai
rubuta masa lada miliyan daya (1,000,000), zai kankarewa mutum zunubbai miliyan
daya (1,000,000) sannan a daga darajar sa sau miliyan daya (1,000,000)
A wata riwayar kuma za'a ginawa mutum danqareren katafaren
gidan bene a Aljannah
(At-Tirmidhi ne ya rawaito a hadisi mai lambata ta # 3428 da
kuma 3429; Ibn Majah # 2235 da sauran su. Haka ma a cikin Sahih Al-Kalim
Al-Tayeb lamba ta # 230)
Don Allah mene ne yafi wannan? Shi yasa wasu magabata a
cikin tabi'ai musamman fa suke daukar kafa su tafi kasuwa alhalin ba siyayya
zasuyi ba, suna zuwa ne don kwadayin samun wadannan tarin ladaddaki masu yawa
Don haka sai ki yi kokari ki haddace wannan addu'a domin
dacewa da samun ladan. Amman dangane da abin da wasu suke aikatawa na shirka,
kamar irinsu rataya qaho ko laya a saman shagon kasuwa don neman ribar
kasuwanci wannan duk shirka ne, sai a guji aikata hakan
Ina yan kasuwa masu neman lada? Ka samu shugabannin kasuwa
ka ce musu su samo allon qarfe su rubuta wannan addu'ar a jiki ta yanda duk
wanda yazo shiga kasuwa zai dinga karantawa domin kuwa wasu sun iya addu'ar
amman shaidan yana mantar dasu idan sun zo shiga kasuwa domin kuwa kamar yanda
masallachi shine dakin Allah anan duniyar to haka kuma kasuwa itace inda
shaidan yafi so shiyasa waje mafi sharri a wajen Allah anan duniyar shine
kasuwa. Wallahi duk wanda yazo shiga kasuwa indai ya karanta ta to kaima zaka
samu ladan can da za'a bashi. Kaga kenan ko ba ka yi cinikin kaya a wannan
ranar sosai ba to zaka samu gidan bene for free a Aljannah
Wannan itace shawarar da na bawa wani Attajiri dake Kasuwar
Dawanau ta jihar Kano. Allah kadai yasan adadin miliyoyin ladan da kaima zaka
samu idan har ka zama silar saka wannan addu'ar a kofar shiga kasuwarku
Idan kuma kasuwancin naki a gida kike yi to sai ki nesanta
da siyan kayan haram, ki katange kanki daga cin riba (kudin ruwa) sannan ki
yawaita karanta addu'ar da Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya koyar bayan
kin dago daga Sujjadar farko kafin ki koma Sujjada ta biyu. Zaki ce:
"Allahumma Arzuqni, warfa'ani, wahdini, wajburni"
(Duba littafin Sifatu Salatin Naby na Shaikh Muhammad
Nasiriddin Al-Albaany, Rahimahullah)
Wallahu ta'ala a'alam
Amsawa:
Usman Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.