𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam Alaikum. Ya nemi alfasha da ita, ta ce sai ya biya
ta. Ya ba ta dubu goma. Amma ta ki yarda su haɗu
kuma ta kashe kuɗin,
ina hukuncin haka?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah.
Tun farko dai, bai halatta mace ta keɓance ko ta kaɗaita
da wanda ba muharraminta ba, har kuma ta yi magana da shi a kan irin wannan
mummunan al’amarin ba. Domin hanya ce mai kusantarwa ga aikata zina wannan kuma
haram ne. Allaah Ta’aala ya ce
وَلَا
تَقْرَبُوا الزِّنَا إِنَّهُ كَانَ فَاحِشَةً وَسَاءَ سَبِيلً
Kuma kar ku kusanci zina. Haƙiƙa ita alfasha ce, kuma mummunar hanya ce.
(Surah Al-Israa’: 32).
Sannan kuma kamar yadda malamai suka nuna, wannan
yarjejeniya ce ɓatacciya
a kan ɓarna. Bai
halatta a ƙulla
shi a tsakaninta da shi ba. domin yarjejeniya a kan zina haram ne kuma abin da
aka bayar ko aka karɓa
da wannan manufar duk haram ne. Ya tabbata a cikin hadisin Annabi (Sallal Laahu
Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce
« ثَمَنُ
الْكَلْبِ خَبِيثٌ وَمَهْرُ الْبَغِىِّ خَبِيثٌ وَكَسْبُ الْحَجَّامِ خَبِيثٌ
»
Kuɗin
kare ƙazanta
ne, kuma kuɗin
karuwa ƙazanta
ne, kuma kuɗin mai
yin ƙaho
ma ƙazanta
ne. (Sahih Muslim: 1568).
Wannan kuɗi
da ta ci zai iya shiga cikin maganar Ubangiji Tabaaraka Wa Ta’aala cewa
يَاأَيُّهَا
الَّذِينَ آمَنُوا لَا تَأْكُلُوا أَمْوَالَكُمْ بَيْنَكُمْ بِالْبَاطِلِ
Ya ku waɗanda
suka yi imani! Kar ku ci dukiyoyinku a tsakaninku da ɓarna. (Surah An-Nisaa’: 29).
Kuma kuɗin
haƙƙi
ne da ba nata ba, kuma amana ce a wuyarta da ya wajaba ta sauke kafin zuwa
ranar tsayuwa a gaban Ubangijin Halittu. Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa
Alihi Wa Sallam) ya ce
« لَتُؤَدُّنَّ
الْحُقُوقَ إِلَى أَهْلِهَا يَوْمَ الْقِيَامَةِ »
Lallai za a mayar da haƙoƙƙi ga masu su a ranar ƙiyama.
(Sahih Muslim: 2582).
Don haka lallai ta mayar masa da kuɗinsa, kuma ta tuba ga Allaah da sharuɗɗan tuban na yin nadama a
kan aikata wannan abin, tare da ƙulla aniya mai ƙarfi cewa ba za ta sake
aikata irin wannan ko ma wani zunubi ba a iya tsawon rayuwarta. Sannan kuma ta
yawaita neman gafarar Allaah a kan abin da ta gabata.
Allaah Ta’aala nake roƙo ya gafarta mata, kuma ya gyara
zuciyarta, kuma ya tsare mata matuncinta daga alfasha.
WALLAHU A'ALAM
Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy
Ga masu tambaya sai su turo ta WhatsApp number: 08021117734
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/BSA30hdZD7V3WSJF8WVwUj
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.