Ticker

6/recent/ticker-posts

Yadda Ake Miyar Gyada

Gyaɗa na ɗaya daga cikin nau’o’in abincin Bahaushe da suka danganci ƙwayoyi. Tsironta ba shi da tsayi ko girma, sannan ganyen tsiron ƙanana ne. Takan yi ’ya’ya ne cikin ƙasa. Gyaɗa na da matuƙar tasiri da muhimmanci a cikin abubuwan da Hausawa ke nomawa. Takan fito da ɓawo (kwalfa) wanda sai an ɓare ake tarar da asalin ƙwayar a ciki. Wannan ne ma ya sa Bahaushe ke da daɗaɗɗiyar waƙar gyaɗa kamar haka:

Gyaɗa mai sihiri,

A ɓare a ga ɗaya,

A murje a ga huɗu,

A tauna a ji garɗi.

Duk da cewa akai nau’o’in miya da dama da Bahaushe ke amfani da gyaɗa a matsayin kayan haɗi, a wannan miyar gyaɗar ce ke kasancewa mafi yawa daga cikin kayan haɗin.

Mahaɗin Miyar Gyaɗa 

Akwai abubuwan da za a tanda idan za a haɗa miyar gyaɗa. Abubuwan sun haɗa da:

i. Daddawa                 

ii. Gyaɗa                                             

iii. Kabewa

iv. Kayan miya           

v. Kayan Ƙamshi/ Kayan yaji            

vi. Magi

vii. Mai                        

viii. Nama ko kifi (idan da hali)        

 ix. Ruwa

Yadda Ake Miyar Gyaɗa 

Daga farko za a tafasa nama a saka albasa da magi da gishiri a ciki. Idan ya tafasa a aje shi gefe. Sannan a daka daddawa da kayan yaji da tafarnuwa a aje gefe ɗaya. Daga nan a jajjaga tarugu da albasa da tumatur da tattasai. Za a hura wuta a ɗora tukunya a saka man gyaɗa ko man ja tare da albasa. Idan ya soyu, sai a zuba jajjagen a ciki a yi ta soyawa inda daga baya za a saka daddawa a ciki. Ita ma idan ta ɗan soyu sai a yi sanwa.

Bayan wannan ya kammala, sai maganar zuba ruwa da kayan ɗanɗano nau’in su magi. Akan sanya kabewa cikin wannan miyar idan ana buƙata. Idan miyar ta dafu sosai za a ɗauko gyaɗa a daka ta sosai ta niƙu sai a zuba a ciki. Ba a rufe tukunya gaɓa ɗaya yayin da aka sanya waɗannan abubuwa. A maimakon haka, za a ɗan ɗaga marfin tukunyar ne gudun kada gyaɗar da ke ciki ta yi bori ta zube. Irin wannan nau’in miya akan ci ta da tuwon shinkafa ko masara da makamantansu, wani lokaci ma har ɗanwake ake ci da ita.

Tsokaci 

Miyar gyaɗa tana matuƙar taimaka wa ga mai juna biyu. Wannan ne ma ya sa ko a asibitoci ake ƙarfafa yin wannan miya. Ya tabbata cewa takan ƙara wa jiki kuzari. Akan samu ɗaiɗaikun mutane da wannan miya kan samar wa illa, musamman wanda ya shafi ɓacin ciki. Miya ce da ake yin ta a birni da ƙauye. 

The book “Cimakar Bahaushe” (Diets of the Hausa People) is a collection of 293 traditional and modern diets of the Hausa people. Detailed explanations of the recipes and ingredients are provided. Comments are provided on the areas of the Hausa land where specific diets are mostly found, the age categories of people that usually use it, as well as the scientific impact of some of the diets to human biology.  Data is collected from interviews with different categories of people including:  i.                    Food sellers within the Hausa land: Mainly to have an idea of recipes on the diets.  ii.                  People of older age: Mainly to have insights on traditional diets of the Hausas.  iii.               Hausa scholars: Mainly to verify and justify the validity of the information obtained as well as provide further expert explanations on the diets.  Moreover, over two hundred (200) pieces of literature were reviewed to have better insight on the topic in question as well as get scientific and professional clarifications on some key concepts relevant to the research. The pieces of literature cover major relevant phenomena such as diet and hunger. Others are on the Hausa land and the Hausas.  The book contains thirty-three (33) chapters. Chapter one is the main introduction in which a concise explanation is provided on the Hausas, their history, their land, social life, and transformations due to globalization, acculturation, and modernity. Chapter two detailly discusses the concepts of diet and food from the Hausa point of view. That includes the meaning and the usage of diets in some Hausa works of literature both verbal and written (i.e. prose, poetry, proverbs, etc.).  Chapters three and four discuss the sources of Hausa diets and their forms accordingly. Chapters five to seventeen discuss some traditional Hausa diets including hard and soft ones. Chapter eighteen concentrates on the influence of modernity and globalization on Hausa diets. It has been discovered that there have been some significant changes in the Hausa diets ranging from recipes to kitchenettes.  Chapters nineteen to thirty-two discuss modern Hausa diets. Some traditional diets are still retained with little modifications, while on the other hand, there are a lot of new ones. Chapter thirty-three discusses “hunger” from the Hausa point of view. The relationship between hunger and food is examined. Additionally, the use of hunger in various Hausa literary works is studied. It is concluded that hunger is like a disease whereby its cure is food.  7th November 2022
Citation (Manazartar Littafin): Sani, A-U. & Umar, H.A. (2022). Cimakar Hausawa. Kano: WT Press. ISBN: 978-978-984-562-9.

Get a copy:
To obtain a copy of this book, kindly send a WhatsApp message to:
+2348133529736

You can also write an email to:

Post a Comment

0 Comments