𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum dan Allah tabbaya nake unguwar danake ne ba ajin qiran sallar magariba sakamakon masallacin da dan nisa shi ne nakeso afadamin dai-dai Lokacin shan ruwa (Buɗa baki) Allah qara basira.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikis Salaam: Lokacin shan
ruwa (buɗa baki) yana
tabbata ne da zarar rana ta faɗi.
Allah maɗaukakin sarki
cewa yayi
ۖ
ثُمَّ أَتِمُّوا الصِّيَامَ إِلَى اللَّيْلِ ۚ
Mu cika azumi izuwa dare kamar
yadda aya ta 187 ta cikin suratul Baqara tayi bayani
Shikuma dare yana farawa daga
lokacin da rana ta faɗi
wannan ita ce fahimtar dukkan malamai. Sabida haka lokacin shan ruwa ga me
azumi yana farawa daga sadda rana ta faɗi,
kenan matukar dai rana ta faɗi
mutum yasha ruwan to azuminsa ya yi in Shã Allahu koda kuwa masallacin da yake
kusa dasu basu kira sallah ba.
Ba sharaɗi bane koda rana ta faɗi kuma ace dole sai an kira sallah sannan
mutum zaiyi buɗa baki,
a'a sharaɗin kawai shi
ne faɗuwar ranar.
Abinda Zakiyi Shi ne Ki Tura
Mijin Ki Ya Tambaya Muku Shin Karfe Nawa ne Suke Yin Kiran Sallah ko Suke Yin
Buɗa-Baƙi a
Wannan Unguwan, ko Kuma ki Nemi izini ki je Ki Tambaya Shin Karfe Nawa ne Rana
Yake Faɗuwa?
Tunda Ke Ba Jin Kiran Sallah a
Masallaci. Idan Ladan Ko Wakilan Masallacin Sun Gaya Miki Lokacin da Rana take
Faɗuwa Sai Kiyi Amfani
da Agogon Wayar Ki Wajen Yin Buɗa-Baƙin ki.
Idan Kuma Hakan Bai yi ba Sai Ki Duba da Kanki Shin Karfe Nawa ne Rana take Faɗuwa? Idan Kin Gani Kin
Tabbatar da Time naki Sai Kike Amfani da Lokacin Faɗuwar Rana wajen yin Buɗa-Baƙin ki.
Domin Annabi Muhammad Mai Tsira
Da Amincin Allah Su Tabbata Agare Shi, Yana Cewa Ku Jinkirta Yin sahur Ku
Gaggauta Yin Buɗa-Baƙi a
Lokacin da Rana ta Faɗi.
Sabida haka da Zarar Rana ta Faɗi
kin Tabbatar da Faɗuwar
ta, toh ko ba ki Ji Kiran Sallah na Ladan ba Za kiyi Buɗa-Baƙin ki Kuma Azumin ki Yayi.
Sa'annan Mu Kara Kula da Time
Namu, Domin Ana Cikin Damina ne a Wasu Jihohin, Wani Lokacin Zaki ga An Yi
Ruwan Sama daga Karfe 5:00pm zuwa 6:00pm Sai Ki ga Gari ya yi Duhu Bayan Ruwa
ya Ɗauke
ki ɗauka Cewa ai Rana
ta Faɗi Magriba ya yi don
Haka bari Ki Sha Ruwa Yanzu.
Idan Kin yi Haka da Ganganci kika Sha a Cikin
Rana to Azumin Ki ya Lalace na Wannan Yinin Sannan Zakiyi Kaffara. Idan a
Rashin Sani Kika yi Shikenan kin dai Wuni da Yinwa da Kishin Ruwa Saura kan
Kiyi Buɗa-Baƙi sai
kika Karya Azumin ki, Saboda haka bayan Sallah zaki Rama 1.
Misalin a Garin Ku Ana yin Buɗa-Baƙi Kullum Karfe 5:50pm,
Yau Sai Aka Yi Ruwan Sama aka Ɗauke Ruwan Sai Gari ya yi Duhu, Sai irin
Karfe 5:30pm kika ce ai Yanzu Rana Ya Faɗi
domin ga Duhu Saboda haka bari Kiyi Buɗa-Baƙin ki
yanzu bayan Kuma ga Yadda Kika yi Buɗa-Baƙi a
jiya Karfe 5:50pm. Toh Kisani Azumin ki ya Lalace Domin Kin Yi Buɗa-Baƙi ne a Cikin Rana, Ranan
bata gama Faɗuwa ba ki
Yi Buɗa-Baƙin ki.
Sabida Haka Muke Yin Amfani da
Time na Agogon Wayar mu Wajen Yin Buɗa-Baƙi koda
An Yi Ruwan Sama ne a Lokacin Duhu ya Sauka kada Muyi Gaggawan Yin Buɗa-Baƙi Alhalin Rana bai Faɗi ba.
Duk Wanda ya Kuskura ya yi Buɗa-Baƙi rana bai faɗi ba, Azumin sa ya Lalace.
Idan da Ganganci ya yi Sai ya yi Kaffara, idan Kuma a Rashin Sani ne Azumin shi
na Yinin Ya ƙarye
Bayan Sallah zai Rama 1. Da Ganganci Shi ne Ace Mutum ya ga Irin Wannan
Tunatarwan sa'annan ya San cewa Rana ba ta Fadi ba ya Ƙi Amfani da shi ya Bi Son
Zuciyar sa. Toh Kaffara zai Kama Shi.
Idan da Rashin Sani Shi ne Ke Ba
ki San Lokacin da Rana take Faɗuwa
ba sai kika yi Gaggawan Shan Ruwa a Lokacin da kika ga Duhu kuma Alhalin Rana
bai Faɗi ba. Toh babu
Kaffara a kanki Kawai biyan 1 zakiyi.
Haka Nan a Lokacin Sahur Muke Yin
Amfani Lokacin Fitowar Alfijir, idan Yau Alfijir Na Garin Ku Ya Fito Sai ki
Duba Karfe Nawa ne? Idan Kin gani Sai Kiyi Amfani da Time ɗin. Saboda Haka Kowa Abinda
Yakamata ya yi Kenan ayi Amfani da Time na Agogon Wayar Mu, Ki bada Ratar Minti
30/20 Tsakanin ki da Fitowar Alfijir.
Shi Kuma Shan Ruwa Kuma Rana tana
Faɗuwa ko Ladan bai yi
Kira ba Ki Gaggauta Yin Buɗa-Baƙin ki.
WALLAHU A'ALAM
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.