Ticker

6/recent/ticker-posts

Tsanantawa A Cikin Aure

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum. Malam dan Allh inada tambaya: Menene hukuncin auren da Al'ada da Taklifi (Tsanantawa) suka mamaye shi a Sharia?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Irin wannan auren ba za'a ce bai yiwu ba. Sai dai ace masu yinsa sun kauce ma tsari irin na sunnar Manzon Rahama (Sallallahu alaihi Wasallam).

Shaikh Dr Muhammad Bakru Isma'eel acikin littafinsa mai suna Fiqhus Sunnah, juzu'i na biyu shafi na 37 yana cewa "Duk da cewar shari'ah mai hikima (wato shari'ar musulunci) bata ajiye wani iyaka game da Qankantar sadaqi ko Qurewar yawansa ba, to amma ba'a son zurfafawa acikinsa saboda cikin yin hakan akwai tsanantawa da takurawa. Domin tsanantawa cikin sadaqi (ko dukiyar aure) shike sanya samari suna kauda kansu daga yin aure, kuma wannan shi ke haifar da abubuwan ɓarna waɗanda ba boyayyu ba, game da lalacewar dabi'a da zamantakewar jama'a".

Duk da cewar shi Malamin yana magana ne kaɗai game da tsadar sadaqi, to amma mu anan Qasar hausa bayan tsadar sadaqin ma akwai wasu miyagun bidi'o'in da mutane suka Qirkiro suka ɗora ma kansu, waɗanda harma anfi tsanantawa akansu fiye da shi kansa sadaqin ma.

Daga cikin abubuwan da zan iya tunawa ana yinsu anan Qasar hausa game da bidi'o'in aure akwai

1. Kayan "Na-gani-inaso".

2. Kuɗin Tambayar arziki.

3. Kayan Sa-rana.

4. Kuɗin Mijin-baya (wanda ake bama 'ya'yan kawunnan amaryar).

5. Kudin rigar waliyyi.

6. Kuɗin Uwar Amarya.

7. Kuɗin Sa-lallen Amarya.

8. Sa lallen Ango.

9. Party, Picnic, etc.

10. Fulani day.

11. Kauyawa day.

12. Arabian Night.

13. Rawar kalangu.

14. Cakuduwar Maza da Mata.

15. Kuɗin sayen bakin amarya.

Waɗannan kaɗan ne na zakulo. Koda ba'a yin wasu daga cikinsu ayankin da kake rayuwa, to awasu yankunan duk ana yi, ko fiye da haka ma.

Waɗannan abubuwan duk sun saɓa ma sunnar Annabi Muhammadu (Sallallahu alaihi Wasallam), wanda Shi Allah ya aiko mana kuma yace mu kwaikwayi aikinsa. Tabbas hakika Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) yayi aurarraki da dama, kuma shima ya aurar da dukkan 'ya'yansa mata. Amma ba'a ruwaito cewa an taɓa aikata koda guda ɗaya cikin Waɗannan abubuwan alokacin bikinsu ba.

Lokacin da ya auri Nana A'isha wasu mata ne 'yan tsiraru suka rakota, kuma ba'a yi wani biki ko kade-kade ba, ballantana cakudar maza da mata. Haka kuma lokacin da ya aurar da 'yarsa Fatimah wacce ita ce Shugabar dukkan matayen duniya da lahira amma ba'a yi biki ko rawa ko shagali ba.

Imamu Ahmad bn Hanbal ya karbo ta hanyar Nana A'isha (Allah ya yarda da ita) tace Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) yace "Hakika auren da yafi albarka shine wanda dawainiyarsa tafi sauki"

Awani hadisin kuma yace "Albarkar mace shine : Saukin sadaqinta, da saukin dawainiyar aurenta, da kyawun halayenta.

"Shu'umancin mace kuma yana cikin : Tsadar sadaqinta, Wuyar dawainiyar aurenta, da kuma munin halinta"

Shaikh Muhammad Bakru Isma'eel yace "Da yawa daga cikin mutane sun jahilci wannan sanarwar ta Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) shi yasa suke kauce mata suke bin hanyoyi irin na zamanin jahiliyyah cikin zurfafa sadaqi (ko dawainiyar aure) suna la'akari da Qarairayin abubuwa bayyanannu.

Sai kaga mutum yana Qin aurar da 'yarsa ga wani mutum komai matsayin ilimin mutumin ko mutuncinsa ko rikon addininsa. Sai dai (in sunga alamar cewa) mutumin zai iya biyan sadaqi mai yawa, basu damu da halin mutumin ba.... Sai kace ita yarinyar da za'a aurar ɗin ta zama wata kadara ce za'a saye ko sayarwa".

Shehu Usmanu ɗan Fodio acikin littafinsa IHYA'US SUNNAH (shafi na 123) da yazo yin bayanin bidi'o'in shaiɗanci da mutane suka kirkiro acikin lamarin aure sai yace "Yana daga cikin wannan (bidi'o'in) irin bikin walimar dake haɗe da Ɓarna kala-kala (kamar chashe rawa ko chudanyar maza da mata) wannan bidi'ah ce muharramah bisa ra'ayin dukkan malamai.

Shehu yace "yazo acikin sharhin ALMUFIDAH : Babu kokwanto cikin haramcin wannan da kuma muninsa". Muna neman tsarin Allah daga ɓacewa da taɓewa.

Yaci gaba da cewa "Zaka ga mutum (Allah ka tsaremu da saɓonka da rashin kishin iyali) kaga mutum wai farkon abinda zai buɗe dashi cikin aurensa kuma ya gina auren nasa akai shine wannan fasadin mai girma. Wanda duk mutum dake da kwayar zarrah na kishin musulunci bazai yarda da haka ba. Balle kuma wanda keda rikon addini koda Qankani ne.

Zaka ga mutum ya tara jama'a ya girmamasu (wato ya basu wuraren zama da abinci) sannan mataye daga dangin Mijin suyi ado suyi kwalliya su fito su haɗu da Waɗannan jama'ar da ya tara, sannan mutane su tattaru daga kowacce nahiya".

Sannan yace "Babu shakka duk bikin auren da ya zamto bisa wannan tsarin aka yishi, to babu albarka cikinsa kuma babu alkhairi. Kaicon shi kansa Mijin (wato angon) da kuma duk waɗanda suka taimaka masa wajen shirya wannan shu'umin taron koda da garwashin wutar kunnawa ne".

Anan nake jan hankalin matasa cewar kuji tsoron Allah ku kiyayi aikata irin waɗannan miyagun bidi'o'in idan kun tashin yin aure. Sannan iyaye ma ya zama wajibi ku sanya ido ku rika yin nasiha ga 'ya'yanku game da irin waɗannan haramtattun bidi'o'in, mutukar dai kuna so auren 'ya'yanku yayi albarka.

Sannan ku guji zurfafawa ko tsanantawa game da kayan lefe tunda babu shi acikin tsarin aure na musulunci. Al'adah ce ta kawoshi. Don haka arika sassautawa ana yin nasiha ga ɓangaren gidan maza cewar kada su matsa wa kansu, su kawo abinda ya sawwaka kawai. Kuma adena la'akari da cewar ai an kawo wa wance kaza-da-kaza, don me mu ba za'a kawo wa tamu 'diyar ba!!!

Muyi koyi da Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) tunda auren nan dai sunnarsa ne. Mu guji aikata abinda zai kwashe albarkar auren.

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments