𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Dr muna son
karin hasken shari’ar Musulunci akan yadda sojoji ke bikin karrama matansu da
kuma yadda suke rufe Musulmi da wadanda ba musulmi ba a makabarta ɗaya.?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikum assalam, Malaman
musulunci suna cewa: Ba’a rufe musulmai da kafirai a makabarta ɗaya kuma hakan shi ne
aikin magabata tun zamanin Annabi Sallallahu alaihi Wasallam har zuwa yau daga
cikin dalilai akan haka shi ne manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam ya wuce
makabartar kafirai sai ya ce wadannan alkairi ya rigaye su, da kuma ya wuce
makabartar musulmai sai ya ce wadannan sharri ya rigaye su kamar yadda Nisa’i
ya rawaito, wannan sai ya nuna banbanci tsakanin makabartun biyu.
Idan aka rufe musulmi a
makabartar kafirai in an yi musu azaba za ta same shi, saboda aya ta: 46 a
suratu Gafir ta nuna ana yi musu azaba a kabarinsu
النَّارُ يُعْرَضُونَ عَلَيْهَا غُدُوًّا وَعَشِيًّا
ۖ وَيَوْمَ تَقُومُ السَّاعَةُ أَدْخِلُوا آلَ فِرْعَوْنَ أَشَدَّ الْعَذَابِ
Wutã, anã gitta su a kanta, sãfe
da maraice, kuma a rãnar da Sa'a take tsayuwa, anã cẽwa, ''Ku shigar da
mutãnen Fir'auna a mafi tsananin azãba.'' (Suratul Gafir Aya ta 46)
Yin bukukuwa yayin bunne musulmi
ya saɓawa ka’idojin
sharia sanannu, don haka ya kamata musulmi su jarraba amsar gawarsu mutukar
hakan zai yiwu.
Allah ne mafi sani.
Don neman Karin bayani duba
Al-mugni na Ibnu-khudaamah 2/563
DR JAMILU ZAREWA
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.