TAMBAYA (82)❓
Aslm ina wuni malan ya gida matar
aurece a aximi tabiyawa kanta bukata batareda namijiba shin xata biya aximinne
ko Wanda Tasha kawai xatayi sannan xata biya aximin a wannan shekaran ko duk
lokaçinda tatashi
Yanxu Ramadan yawuce ga wani
Ramadan yaxo xata Rama bayan Ramadan din Nan kenan tahada da Wanda Tasha na
wannan Ramadan din
AMSA❗
Alhamdulillah
Na'am
Zata rama wancan ne bayan Ramadan
dinnan ya wuce
Amman kam ta fiya sakaci dayawa,
ace har azumi ya kewayo Amma batasan hukuncin wancan azumin da ta karya ba
silar masturbating din
Yin wasa da al'aura
(masturbation) haramun ne kamar yanda Malamai mafi rinjaye suka fada, kana
azumi ne ko kuma baka azumi
Idan kana azumi kuma kayi wasa da
gabanka har maniyyi ya fito to azumin nan ya karye. Idan maniyyi bai fito,
azumin ka yananan
A cikin Al-Mughni, Ibn Qudaamah
yace: "Duk wanda yake wasa da al'aurarsa to zunubi yake aikatawa. Saidai
azumin mutum yananan ko da ya aikata Istimna'i amman idan ya fitar da maniyyi,
azuminsa ya karye"
A cikin dai Al-Mughni din ya ci
gaba da cewa: ”Duk wanda ya fara azumin nafila kuma ya karyashi to ba a binsa
ramuwa duk da cewar ramawar shi yafi (Mustahabbi ne). Wanda duk ya fara azumin
nafila to ya kammala shi. Duk wanda ya karyashi to ba sai ya rama ba tunda
daman ba na farillah bane ba
Abdullahi Ibn Umar da kuma Ibn
Abbas (Radiyallahu anhum) sun taba daukan azumin nafila wata rana kuma wani
dalili yasa suka karya shi. Ibn Umar yace: "Babu laifi saidai idan mutum
yana azumin da ake binsa ne ko kuma azumin rantsuwa"
Al-Mughni: " An-Nakha'i, Abu
Haneefah, Imam Maleek since: "Duk wanda ya fara azumi to ya cika shi. Kada
ya karya shi har saidai idan akwai wani qwaqqwaran daleel (dalili) wanda zaisa
ya rama daga baya"
A karshe kuma a shawarce ta dage
da yawaita Istighfari, tayi taubatun Nasuha kuma kada ta kara kusantar duk wani
abu da ka iya zama silar karyewar azuminnata
Wallahu ta'ala a'alam
Amsawa
Usman Danliti Mato
(Usmannoor_Assalafy)
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.