𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘��❓
Shin ya halatta ga mace mai haila
ta shiga masallaci? Don Allah malam ka amsa mana tambayar nan domin yanzu haka
musu mukeyi da wasu mata. Sunce wai ba'a hana ba. Wai inji su Sallah ce kawai
aka hana suyi. Amma ba'a hana su shiga masallaci su zauna ba. Malam yaya abun
yake ne?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Dukkan Maluman mazhabobin nan huɗu sunyi ittifaki akan
rashin halaccin shigar mace mai haila cikin masallaci.
Duk sunce bai halatta ba. Kuma
hujjarsu anan ita ce hadisin da bukhary da muslim suka ruwaito daga Ummu Atiyyah
(rta). Tana cewa
"Manzon Allah (Sallallahu
alaihi Wasallam) ya umurcemu mu fito da 'yan mata, da matayen da suke tsari
(domin suzo masallacin Eidi.) Amma Yace masu haila su nisanci masallacin
musulmai"
(Aduba Sahihul Bukhary hadisi na
974, sahihu MusLim hadisi na 890)
Malamai suka ce Manzon Allah
(Sallallahu alaihi Wasallam) ya umurcesu suyi nesa da masallacin Eidi ne saboda
matsayinsa kamar masallacin jumu'a ne da sauran masallatai.
Acikin FATAWAL LAjNATUD DA'IMAH
juzu'I na 6 shafi na 272, an tambayi majalisar malaman sa'udiyya. Shin mace mai
haila zata iya shiga masallaci domin ta zauna ta saurari Khutbah ko wa'azi ko
karatun Alkur'ani?
Sai suka ce A'a bai halatta ba
gareta ko ga mai jinin haihuwa su shiga masallaci su zauna. Sai dai idan larura
tasa, zasu iya shiga su wuce ta cikin masallacin. Amma idan batta tsoron kada
jinin nata ya zuba ya ɓata
shimfidar masallacin yayin wucewar tata. Kamar yadda ayah ta 43 acikin suratun
Nisa'I tayi bayani
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا لَا تَقْرَبُوا
الصَّلَاةَ وَأَنْتُمْ سُكَارَىٰ حَتَّىٰ تَعْلَمُوا مَا تَقُولُونَ وَلَا جُنُبًا
إِلَّا عَابِرِي سَبِيلٍ حَتَّىٰ تَغْتَسِلُوا ۚ وَإِنْ كُنْتُمْ مَرْضَىٰ أَوْ عَلَىٰ
سَفَرٍ أَوْ جَاءَ أَحَدٌ مِنْكُمْ مِنَ الْغَائِطِ أَوْ لَامَسْتُمُ النِّسَاءَ فَلَمْ
تَجِدُوا مَاءً فَتَيَمَّمُوا صَعِيدًا طَيِّبًا فَامْسَحُوا بِوُجُوهِكُمْ وَأَيْدِيكُمْ
ۗ إِنَّ اللَّهَ كَانَ عَفُوًّا غَفُورًا
Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku kusanci sallah
alhãli kuwa kuna mãsu mãye, sai kun san abin da kuke faɗa kuma haka idan kuna mãsu janaba, fãce mai ƙetare
hanya, har ku yi wanka. Kuma idan kun kasance majinyata, ko kuwa a kan tafiya
ko kuwa wani daga cikinku, idan ya zo daga gayaɗi,
kõ kuwa kun shãfi mãtã ba ku sãmi ruwa ba, to ku nufi, fuskar ƙasa
mai kyau, ku yi shãfa
ga fuskokinku da hannuwanku. Lalle ne Allah Yã kasance Mai yãfewa
Mai gãfara. (Suratun
Nisá'i Aya ta 43)
An tambayi Shaykh Ibnu uthaymeen
game da haka shima yace Bai halatta ba. Domin hukuncin mai haila kamar na mai
janaba ne. Kuma ya kawo hujjoji akan rashin halaccin hakan.
(Aduba littafinsa mai suna
Fatawat tahaarah shafi na 273).
Idan kana son kaga qarin bayani
da kuma sauran maganganun malamai akan haka, kaje ka duba wadannan litattafan
1. ALMABSOOT juzu'I na 3 shafi na
153.
2. HASHIYATUD DASOOQEE juzu'I na
daya shafi na 173.
3. ALMAJMOO'U na Nawawy, juzu'I
na 2 shafi na 388.
4. ALMUGHNEE na ibnu qudamah,
juzu'I na 1 shafi na 195.
Ina fatan mutane zasu rika zurfafa
bincike akan manyan mas'aloli irin waɗannan.
Adena yarda da maganganu na sonrai marasa hujjoji.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/DIcJIQrWyLP0oBOMSnDi5P
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.