𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mutum ne ya yi zina da mace har ta samu ciki, kuma ya ce ya yarda ya karbi cikin idan ta haihu yana son ɗansa, shin a shari'ance ya halatta a jingina wannan ɗan zinar zuwaga ubansa na zinar tunda ya karba ko kuma a'a bai halatta ba?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Malamai sun ƙara wa juna sani dangane da hukuncin
jingina ɗan
zina zuwaga ubansa, da farko dai dukkan Malamai sun yi Ittifāƙi akan cewa idan Mutum ya yi zina da
Matar aure to ana jingina ɗanta ne zuwaga mijinta ba
wai wanda ya yi zinar da ita ba, ko da kuwa wanda ya yi zinar da ita ta samu
cikin ya yi da'awar cewa cikinsa ne, to ba za a yi aiki da maganarsa ba matukar
dai ta haifi yaron a cikin watanni shida ko sama da haka bayan aure, to za a
jingina wannan ɗan zuwaga mijinta ne, sai
dai idan mijin ne ya kore ɗan ta hanyar Li'āni a kotu ya
ce ba ɗansa
ba ne.
Sannan idan ya kasance matar
ba ta da aure kuma wanda ya yi mata cikin bai yarda cewa na sa ba ne, ko kuma
yaƙi yarda ya karbe shi a matsayin ɗansa,
to anan ma ƙaulan wahidan Malamai
suka ce ba za a jingina wannan ɗan zinar zuwaga wanda ya yi mata
cikin ba.
Amma idan wanda ya yi mata
cikin ya yarda cewa shi ne yayi, kuma ya yarda ya karɓi
cikin a matsayin ɗansa, to anan sai Malamai
sukayi Saɓani, mafi yawa daga cikin Malamai
cikinsu harda galibin Malaman da ke Mazhabobin nan guda huɗu na
Malikiyya, Shafi'iyya, Hanafiyya, da kuma Hanabila. Duk sun tafi ne akan cewa
ba za a riskar da ɗan zina zuwaga ubansa na
zina ba ko da kuwa uban ya karɓi cikin ya yarda cewa ɗansa
ne suka ce ba za a jingina shi zuwa gareshi ba.
Daga cikin dalilansu sun
kafa hujja da wannan Hadisin da Annαвi (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce:
الولد للفراش وللعاهر الحجر،
MA'ANA: Ɗa na mai shinfiɗa ne
(mijinta ko shugabanta idan baiwa ce) shi kuma wanda ya yi zina sai ayi masa
Hajaru (idan an samu shaidu kuma ya taɓa
aure)
Malaman da suke kan wannan
fahimta a wajensu ba za a jingina ɗan
zina zuwaga ubansa ba, hakanan babu gado tsakanin Ɗan da Uban sai dai yagaji uwarsa kawai.
To sai dai kuma a gefe ɗaya
akwai Malaman da suka tafi akan cewa ana iya jingina ɗan
zina zuwaga ubansa matuƙar
dai uban ya yi da'awar cewa nasa ne kuma ya karɓa,
Malamai da yawa kamar irin su Ibn-Taymiyya, Ibnul-Ƙayyum, Hasanul-Basariy, da wasunsu suna
ganin hakan babu laifi musamman idan ya kasance akwai wata maslaha ta rayuwa da
aka kalla, shi ya sa ma suka ce ya halatta a ɗaura
musu aure bayan ya yi mata cikin.
Daga cikin dalilan Malaman
da ke kan wannan ra'ayi sun kafa hujja da cewa asali an halicci wannan yaro ne
da ruwan maniyyin wanda ya yi zinar da ita, kuma ya yarda cewa nasa ne, sannan suka
ce ai wancan Hadisin da Annαвi (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce:
الولد للفراش وللعاهر الحجر،
Yana magana ne akan idan
mace tana da miji ne kaɗai, amma idan ba ta da miji
to zahirin Hadisin ba ya nuna cewa idan mutum ya yarda cewa ɗansa
ne kada a jingina masa shi ba, danhaka suka ce indai har mutum ya yi iƙirarin cewa ɗansa
ne to za a jingina shi zuwa gareshi sannan kuma akwai gado a tsakaninsu.
Ba ya ga haka suka ce
Malaman da suka tafi akan cewa ɗan zina ba zai gaji ubansa
ba dukkansu sun yarda cewa ɗan zai iya gadon
mahaifiyarsa, to ta yaya za a ce ɗan
zina zai iya gadon uwarsa da ta yi zina ta haife shi amma ba zai gaji ubansa ba
alhali uban ya yarda cewa ɗansa ne shi ya yi cikin kuma
yana son kayansa? Da wanne dalili suka dogara akan cewa ɗan
zina zai iya gadon uwarsa alhali itama uwar ba ta hanyar aure ta haife shi ba.
Wannan dai wata mas'ala ce
da aka samu saɓani akanta, sai dai Malamai da yawa a da
can da kuma a yanzu sun karkata zuwa ga wannan ra'ayi na ƙarshe cewa ɗan
zina zai iya gadon ubansa, musamman idan ya kasance akwai wata masalaha mai
karfi da aka yi la'akari da ita akan hakan.
*** ***
SHIN YA HALLATA JINGINA ƊAN ZINA ZUWAGA UBANSA?
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘��❓
Assalamu alaikum Malam Mutum ne yayi zina da Mace har tasamu
ciki, kuma ya ce ya yarda yakarbi cikin idan ta haihu yanason ɗansa, Shin a Shari'ance
yana halatta ajingina wannan ɗan
zinar zuwaga Ubansa na zinar tunda yakarba kokuma a'a bai halattaba??
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam warahamtullahi Wabarkatuh
Mālamai sun ƙārawa
jūna sani dangane da
hukuncin jingina Ɗan-Zina zuwaga ubansa, dafarkodai dukkan Mālamai sunyi Ittifāƙi akan cewa idan Mutum
yayi zina da Mātar
aure to ana jingina ɗantane
zuwaga mijinta bawai wanda yayi zinar da'itaba, koda kuwa wanda yayi zinar
da'ita tasamu cikin yayi da'awar cewa cikinsane, to baza'ayi aiki da
maganarsaba matukar dai tahaifi yaron acikin watanni shida ko sama dahaka bayan
aure, to za'a jingina wannan ɗan
zuwaga mijinta, saidai idan mijinne yakore ɗan
ta hanyar Li'āni a kotu.
Sannan idan yakasance Mātar bata da aure kuma wanda yayi
mata cikin bai yarda cewa nasa bane, kokuma yaƙi yarda yakarbeshi amatsayin ɗansa, to ananma Ƙaulan-Wāhidan Malamai sukace baza'a
jingina wannan Ɗan-Zinar zuwaga wanda yayi mata cikinba,
Amma idan wanda yayi mata cikin yayarda cewa shine yayi,
kuma ya yarda yakarɓi
cikin amatsayin ɗansa,
to anan sai Mālamai sukayi Sāɓānī,
mafi yawa daga cikin Mālamai cikinsu harda gālibin Malaman dake Mazhabobinnan
guda hudu, duk suntafine akan cewa baza'a riskar da Ɗan-Zina zuwaga ubansa
ba koda kuwa uban yakarɓi
cikin ya yarda cewa Ɗansane, sukace baza'a jinginashi zuwa gareshiba, daga cikin
Dalilansu sunkafa Hujja da wannan Hadisin da Annαвi( ﷺ ) Ya ce
ﺍﻟﻮﻟﺪ
ﻟﻠﻔﺮﺍﺵ ﻭﻟﻠﻌﺎﻫﺮ ﺍﻟﺤﺠﺮ ،
MA'ANA
Ɗa namai-Shinfiɗane
(mijinta ko shugabanta idan baiwace) shikuma wanda yayi zina sai ayimasa Hajaru
(idan ansamu shaidu kuma yataɓa
aure)
Malaman dasuke kan wannan fahimta awajensu baza'a jingina Ɗan-Zina
zuwaga ubansaba, hakanan babu gādo
tsakanin Ɗan
da Uban saidai yagāji
uwarsa kawai.
To Saidai kuma agefe ɗaya
akwai Mālaman da suka tafi akan cewa ana iya jingina Ɗan-Zina zuwaga ubansa
matuƙar
dai uban yayi da'awar cewa nasane kuma yakarɓa,
Malamai da yawa kamar irin su Ibn-Taymiyya, Ibnul-Ƙayyum, Hasanul-Basariy
da wasunsu suna ganin hakan babu laifi musamman idan ya kasance akwai wata
Maslaha ta rayuwa da aka kalla, shiyasa ma sukace ya halatta adauramusu aure
bayan yayi mata cikin, daga cikin Dalilan Malaman dake kan wannan ra'ayi
sunkafa Hujja dacewa asali an halicci wannan yarone da ruwan maniyyin wanda
yayi zinar da'ita, kuma ya yarda cewa nasane, sannan sukace ai wancan Hadisin
da Annαвi( ﷺ ) Ya ce
ﺍﻟﻮﻟﺪ
ﻟﻠﻔﺮﺍﺵ ﻭﻟﻠﻌﺎﻫﺮ ﺍﻟﺤﺠﺮ ،
Yana magane akan idan mace tanada mijine kaɗai, amma idan bata da
miji to Zāhirin Hadisin baya nuna cewa idan mutum ya yarda cewa ɗansane kada ajingina masa
shiba, danhaka sukace indai har mutum yāyi iƙirārin
cewa ɗansane to za'a
jinginashi zuwa gareshi sannan kuma akwai gādo atsakaninsu
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.