𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam. Yaya Mace
Za Ta Yi Sallar Tarawihi A Cikin Gidanta?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam Warahmatullahi
Wabarkatuhu
Sallar Mace a gidanta ta fi tayi
a masallaci, Sallar farilla ko ta nafila ciki har da Tarawihi.
Za tayi sallar Tarawihi a gidanta
gwargodon abin da ya samu, za ta iya raka'a 11 ko yadda taso raka'a biyu-biyu,
sannan tayi witri a ƙarshen sallarta. Sai dai idan ya kasance a kwai mata a cikin
gidan, sai su yi sallar tare cikin jam'i dukkansu su tsaya a tsakiya waje guda.
Idan kuma yin sallar yafi mata a masallaci, sai taje babu laifi.
Domin Ya halatta mata su halarci
Sallar Tarawihi a Masallaci, idan babu tsoron za a fitinu da su, saboda Annabi
(Sallallahu alaihi Wasallam) Ya ce: “Kada ku hana bayin ALLAH mata zuwa
Masallatan ALLAH.” [Bukhari:900, Muslim:442]
Amma wajibi ne mace ta cika sharuɗan zuwa masallacin, ta zo
cikin hijabi, ba tare da bayyana ado ko tsiraici ba, ba tare da shafa turare ko
daga murya ba, saboda ayar
وَقُل لِّلْمُؤْمِنَاتِ يَغْضُضْنَ مِنْ أَبْصَارِهِنَّ
وَيَحْفَظْنَ فُرُوجَهُنَّ وَلَا يُبْدِينَ زِينَتَهُنَّ إِلَّا مَا ظَهَرَ مِنْهَا
وَلْيَضْرِبْنَ بِخُمُرِهِنَّ عَلَىٰ جُيُوبِهِنَّ وَلَا يُبْدِينَ زِينَتَهُنَّ إِلَّا
لِبُعُولَتِهِنَّ أَوْ آبَائِهِنَّ أَوْ آبَاءِ بُعُولَتِهِنَّ أَوْ أَبْنَائِهِنَّ
أَوْ أَبْنَاءِ بُعُولَتِهِنَّ أَوْ إِخْوَانِهِنَّ أَوْ بَنِي إِخْوَانِهِنَّ أَوْ
بَنِي أَخَوَاتِهِنَّ أَوْ نِسَائِهِنَّ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُهُنَّ أَوِ التَّابِعِينَ
غَيْرِ أُولِي الْإِرْبَةِ مِنَ الرِّجَالِ أَوِ الطِّفْلِ الَّذِينَ لَمْ يَظْهَرُوا
عَلَىٰ عَوْرَاتِ النِّسَاءِ وَلَا يَضْرِبْنَ بِأَرْجُلِهِنَّ لِيُعْلَمَ مَا يُخْفِينَ
مِن زِينَتِهِنَّ وَتُوبُوا إِلَى اللَّهِ جَمِيعًا أَيُّهَ الْمُؤْمِنُونَ لَعَلَّكُمْ
تُفْلِحُونَ
Kuma ka ce wa mũminai mãta su
runtse daga gannansu, kuma su tsare farjõjinsu kuma kada su bayyana ƙawarsu
fãce abin da ya
bayyana daga gare ta, kuma su dõka
da mayãfansu a kan
wuyan rigunansu, kuma kada su nũna
ƙawarsu
fãce ga mazansu ko
ubanninsu ko ubannin mazansu, ko ɗiyansu,
ko ɗiyan mazansu, ko
'yan'uwansu, ko ɗiyan
'yan'uwansu mãtã, kõ mãtan ƙungiyarsu, ko abin da hannãyensu na dãma suka mallaka, ko mabiya
wasun mãsu bukãtar mãta daga maza, kõ jãrirai waɗanda.
bã su tsinkãya a kan al'aurar mãtã. Kuma kada su yi dũka da ƙafãfunsu dõmin a san abin da suke ɓõyẽwa daga ƙawarsu.
Kuma ku tũba zuwa ga
Allah gabã ɗaya, yã ku mũminai!
Tsammãninku, ku sãmi babban rabo. (Suratul Nur Aya ta 31)
ALLAH shi ne mafi sani.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/BSA30hdZD7V3WSJF8WVwUj
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.