Ticker

6/recent/ticker-posts

Mace Mai-Ciki Ko Mai Shayarwa Zata Iya Ajje Azumi?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Shin wai gaskiyane cewa duk Mace Mai-Ciki ko Mai Shayarwa zata iya ajje azumi ta ciyar kawai amadadinsa kokuma ya abin yake??

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Ko Shakka bābu cewa wannan magana ba gaskiya bace domin kuwa bahaka Shari'a tace ayiba, danhaka dai da farko yana dakyau musani cewa bawai haka kawai dan saboda kasancewar Mace tana da Ciki ko tana Shāyarwa hukuncin yin azumi yafāɗi akantaba, domin dayawa daga cikin 'Yan'uwa Mātā sunyiwa wannan hukunci mummunar fahimta, kodai wasu saboda Jāhilcinsu ko saboda son zuciya kokuma saboda ƙarancin bayani daga wajen su Mālaman da suke basu fatawa akan hakan, domin dayawa daga cikin Ɗāliban-Ilimi zaka samu suna bada fatawane kawai akan cewa Mai-Ciki da Mai Shāyarwa zasu ciyarne kaɗai amadadin azuminsu, wanda kuma bahaka hukuncin yake a Sake ba Ƙaidi ba.

idan Mai-Ciki ko Mai Shāyarwa kokuma Maras lāfiya sunājin ƙarfin jikinsu yadda zasu iyayin azumi batare da sun galabaita irin galabaitar da ta sāɓāwa yadda akasaba gani abisa al'āda ba, to wajibine akansu suyi wannan azumin, idan kuma sukaƙiyi to susani cewa sunbar wani wājibi da Aʟʟαн() Ya wajabta musu suyi, kuma Sai Aʟʟαн() Yākamasu da laifin hakan domin Shidai Aʟʟαн() baza'a iya yimasa ƙarya ko wayoba, amma idan yakasance Mutum yana cikin laulayin da idan yayi azumi zai tagayyara irin tagayyarar da yawuce na al'ada, kamar misalin Mutum yafita daga hayyacinsa ko yariƙa suma saboda wahala ko wani abu makamancin haka, kokuma yin azumin zai iya ƙāra cutar datake dāmunsa ko tayi jinkirin warkewa kokuma yakamu da wata sabuwar rashin lafiyar adalilin azumin dayayi, to anan sai Shari'a tayimasa rangwame akan cewa zai iya cin abincinsa, daga baya kuma idan yawarke sai yarama adadin azumin da yasha, amma ba dalili bane wai kaji Mace tace wai azumi yana bata wahala danhaka bari tasha ruwa itama bayan Sallah sai taciyar, wannan wasane da addini kawai, domin kuwa ana maganane akan irin wahalar da ta sāɓāwa irin wahalar da aka saba ji a al'ada, amma inba hakaba ai koma waye zaiyi azumi dole sai yaji ajikinsa

Danhaka kuskurene babba Mutum yarika wasa da lamarin addininsa, Sannan wasu daga cikin Mutāne kuma sukayi wani wāyo na son zuciya, yāyin da akace Mālamai sunyi Saɓāni akan wata Mas'ala ta Fiƙhu, to kawai sukan dubane suga wanne ɓangarene yafi sauƙi sai su ɗauka suyi amfani dashi, ko shakka babu wannan kuskurene babba, domin kuwa idan Mālamai sukayi Saɓāni to anasone Mutum yaɗauki ɓangaren da yake da Dalilai da Hujjoji masu ƙarfi koda kuwa shine ɓangaren da yafi wahala ɗin, Aʟʟāн() Ya gānar damu gaskiya ya bāmu ikon aiki da'ita Āmīn-Yā-Rabbi.

шαʟʟαнυ-тα'αʟα α'αʟαмυ

AMSAWA

      Mυѕтαρнα Uѕмαn

       08032531505

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam


Post a Comment

0 Comments