𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalaamu Alaikum Wa Rahmatul Laah. Malam Mene ne hukuncin mutanen da suke barin wayoyinsu a buɗe a cikin masallaci, kusan kullum sai waya ta yi ƙara ana cikin sallah.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul
Laahi Wa Barakaatuh.
Ya kamata kowannenmu ya san cewa
1. Masallaci ɗakin Allaah ne. Masallaci
shi ne wurin da Allaah ya fi so duk a cikin duniya. Masallaci wuri ne da Allaah
ya keɓe domin bayinsa
su ziyarce shi sau biyar a kowace rana. An gina masallaci ne kaɗai don ayyukan bauta, kamar
Sallah da Tilawa da Zikiri da sauransu.
2. Wajibi ne a kawar da duk abin
da zai iya ɗauke
hankalin bayin Allaah a cikin masallaci. Mai ɗauke
hankalin nan ko, jin sa ake yi ko gani
ko shaƙe ko makamantan haka, duk ɗaya
ne.
3. Sallah ita ce mafificiyar
ibadar da Allaah Maɗaukakin
Sarki ya halicce mu domin ta. Sallah ita ce aikin da za a fara yi wa bawan
Allaah hisabi a kanta a ranar Ƙiyama.
4. Wajibi ne mu riƙa
natsuwa a cikin sallah, mu nisanci duk abin da zai ɗauke hankali a cikin sallah.
5. Wayar GSM ce ta fi ɗauke hankalin bayin Allaah
a cikin masallacin Allaah a yau! Ta
hanyar GSM ake cutar da bayin Allaah a cikin ibadarsu ga Allaah a cikin
masallacin Allaah. Don yawancin sautukan da mutane suke sanyawa a cikin wayar
GSM muryoyin sheɗan
ne. Muryar sheɗan ita
ce: Busa da goge da kiɗa
da tafi da ƙwarya
da shantu da sauransu. Haka ma sautukan
waƙe-waƙen
addini, waɗanda ake
amfani da komfuta kafin a fitar da su. Alƙur’ani
da Sunnah da Haɗuwar
Malamai duk sun nuna haram ne sauraron
muryar sheɗan. Har Alƙur’ani ba a yarda a buɗe shi ta yadda zai cutar da
masu sallah ba, ina kuma ga muryar sheɗan.
Shigar da muryar sheɗan
cikin masallaci alamar sako-sako da addinin Allaah ne.
6. Dole ne musulmi ya kashe
wayarsa kafin ya shiga masallaci, ko da babu muryar sheɗan a cikinta. Idan kuma ya manta, to sai ya yi
gaggawar kashewa da zaran ya tuna ko an tuna masa. Kamar idan ya ji wayar wani
ta yi ƙara,
shi ma sai ya tuna, kuma ya ɗauki
matakin rufe tasa. Kuma ko da ana cikin sallar ne ya tuna, ko kuma ya ji ta yi ƙara,
to sai ya yi gaggawar kashe ta. Kashewa murus ya wajaba ya yi, ba wai ya sanya
ta a ‘silence’ ko a ‘vibration’ kawai ba. Ba daidai ba ne
ya kashe na ɗan lokaci
ba kawai, ta yadda idan ta sake ƙara ya sake kashewar. Fitarwa da kashewar
ba za ta jawo wa mai sallah wani abu ta fuskar sujadar rafkanuwa ba! Wannan
matakin shi ya fi da a ƙyale wayar ta cigaba da yin ƙara, tana ta cutar da masallata.
7. Daidai ne a tuna wa masallata
tun kafin a fara sallah, cewa su kashe wayoyinsu, kuma lallai su bi wannan
umurnin. Waɗansu sukan
ce, sun manta da kashe wayoyin ne tun kafin su shiga masallacin Allaah! Amma ba su yin irin wannan
mantuwar wurin shiga ofisoshin tsaro da sauransu! Don me?! Ko sun fi ganin
girman waɗannan
wuraren ne fiye da Masallatan Allaah Maɗaukakin
Sarki? Mutum ba ya shiga wurin duk mai matsayi a idonsa a duniya da wani abin
da ba ya so. Amma yau ga mutane suna shiga masallaci da abubuwan da suka
tabbatar Allaah ba ya so! Sannan kuma wai sun je neman ya biya musu buƙatunsu
na duniya da barzahu da lahira ne!
8. Waɗansu kuma ba su kashe wayoyin ne, wai gudun
kar a neme su, ba a same su ba! Wai shin ko daga Lahira ce za a kira su don a
gaya musu cewa takardar Aljannarsu ta fito?!! Watau ba za su iya bayar da
mintoci goma zuwa sha-biyar don Sallar da Allaah ya halicce su dominta ba! In
kuwa haka ne to, don Allaah ina cikan imani da musulunci da taqawa a irin
wannan halin?! Shin wayar da suke yi a lokacin ta fi Aljannar da suka zo nema
muhimmanci ne a lokacin?!
9. Wajibi ne mu san cewa duk
yadda harkokin duniya su ke ba su isa a wulaƙantar da sallah saboda su ba. Dole duk
mai neman mu ta waya ya san cewa: Ba za mu taɓa
ɗaukar wayarsa a
lokacin sallah ba. Kuma lallai mu san cewa: Alhaki na kan duk wanda ƙarar
wayarsa ta ɗauke wa
wani hankali a cikin sallah.
Laa Haula Walaa Quwwata Illaa Bil
Laah.
WALLAHU A'ALAM
Sheikh Muhammad Abdullaah
Assalafiy
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.