Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Wanda Yake Sallar Dare Amma Bai Samun Sallar Asubahi

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum warahmatullah. Mallam meye hukunci mutumin da yake sallar dare (Qiyamul layli) sai barci yake hanashi samun sallar asubahi? Allah ya saka ma da gidan aljannah, ya gafartawa mahaifanka, ya sadamu da shugabanmu Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi Wasallam)

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Gaskiya wannan ya munana ma kansa, Kuma ya cuci kansa. A garin aikin Mustahabbi ya tozartar da ayyukan farilla.

Yin sallar Asubahi acikin jam'i kuma akan lokacinta wajibi ne. To amma shi Qiyamul Layli (Tahajjud) Sunnah ce ta Mustahabbi. Kuma yinta agida yafi lada fiye da yinta a masallaci. Sannan yinta kai kaɗai yafi lada fiye da yinta cikin jam'i.

Don haka ya kamata samari su kula. Babu abinda Ubangiji yafi Qauna daga gareka fiye da yaga ka bauta masa kamar yadda ya umurceka kuma ka fara bama farilla hakkinta kafin nafilfili.

Kuma Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) ya kwadaitar da al'ummah sosai game da halartar sallah cikin jam'i. Musammab asubah da kuma isha'i.

To wannan kuma idan dagewa tsayuwar dare da rasa sallar asubahi shine dabi'arsa to lallai yakamata a jajanta masa domin kuwa yana yin babbar hasara sabida nassoshi ingantattu sun tabbatar cewa Duk wanda ya samu Sallar asubahi a cikin jam'i To kamar ya kwana yana sallah a wannan daren ne. Sayyadina umar Allah ya kara masa yarda cewa yayi: wand duk ya halarci sallar asubahi a cikin jam'i shine yafi masa soyuwa ya kwana yana sallar dare.

Sabida haka sallar dare idan ka cire sallar farillah babu sallar da tafi ta kuma yana daga mafi soyuwar ayyukan manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam sabida haka tana da matukar muhimmanci kwarai dagaske. Amma kuma idan mutum ya mayar da dabi'arsa tsayuwar dare Amma kuma baya samun sallar asubahi cikin jim'i to wannan kuma yana sakaci sabida gwara ace ya kwana yana bacci Amma kuma ya samu sallar asubahi a cikin jam'i

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments