𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mene ne hukuncin Azumin wanda yayi
mafarki da rana har Maniyyi yafito masa??
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Dangane da hukuncin Fitar Maniyyi
ga wanda yake azumi mafi yawan Malamai cikinsu harda Mazhabobin nan guda huɗu wato
1. Malikiyya
2. Shafi'iyya
3. Hanafiyya
4. Hanabila
Dukkansu suntafine akan cewa
fitar da Maniyyi da gangan ta hanyar da ba jima'i ba yana lalata azumi, danhaka
idan Mai-Azumi yayi Istimna'i, ko ya rungumi Matarsa, ko yayi wasa da'ita,
hartakai ga yafitar da Maniyyi to azuminsa ya lalace, danhaka Malamai sukace
dukkan Mutumin da yasan cewa Sha'awarsa tana da ƙarfin da indai zaiyi wasa da Matarsa
Maniyyi zaifito masa to haramunne agareshi yayi hakan da'ita, idan kuwa yayi
har Maniyyi yafita to wajibine sai yarama wannan azumin, amma idan yakasance
Maniyyin yafitane ta hanyar mafarki kokuma tunani ko kallon Mace batare da yayi
wasa da'itaba, mafi yawan Malamai sukace azuminsa bai lalace ba saidai wajibine
yayi wankan janaba, amma Mazhabin MALIKIYYA sukace koda mafarki yayi dolene sai
yarama wannan azumin.
Danhaka Malamai sunyi Saɓani dangane da yanayin
ramuwar azumin da Mutum zaiyi, Mafi yawan Malamai suntafine akancewa zai rama
azumi guda ɗayane
kawai batare da yayi wata Kaffara ba, domin Nassin yin Kaffara yazone akan
wanda yayi Jima'i da Matarsa da rana, Saidai Mazhabin MALIKIYYA suntafine
akancewa idan Mutum yayi Mafarki har yafitar da Maniyyi to azuminsa ya lalace
kuma dolene sai ya rama batare da kaffaraba, amma idan wasa yayi da Mace ya
rungumeta ko ya Shafata ko yayi Istimna'i har yafitar da Maniyyi, to wajibine
sai yayi ramuwa tare da Kaffara, domin sunyi Ƙiyasine akan hukuncin wanda yayi Jima'i
da Matarsa da gangan da rana.
Amma. Mazhabin ZAHIRIYYA
suntafine akan cewa wanda yafitar da Maniyyi da gangan ta dukkan wata hanyar da
ba Jima'i yayi da Matarsa ba, sukace azuminsa yana nan bai lalace ba, domin
babu wata Hujja afili Ƙarara daga cikin Al-Ƙur'ani ko Hadisi datace azuminsa ya
lalace, to amma Saidai maganar Malaman da sukace azuminsa ya lalace tafi Ƙarfi.
Amma maganar da tafi inganci
wacce mafi yawan Malamai sukafi rinjayar da'ita shine, fitar Maniyyi ta hanyar
mafarki baya karya azumi, domin Ɗan-Adam bashi da wani iko na ya'iya hana
kansa yin mafarki alokacin da yake barci ba, hakanan magana mafi inganci fitar
Maniyyi ta hanyar tunani ko kallo shima baya karya azumi, amma duk dahaka
ba'ace Mutum yarika sanya irin wannan tunanin acikin Zuciyarsa ba, amma fitar
Maniyyi dagangan tahanyar wasa tsakanin Ma'aurata, ko tahanyar Istimna'i,
wannan kam yana lalata azumi, kuma za'ayi ramuwane kaɗai batare da Kaffaraba, amma idan Mutum yayi
jima'i da Matarsa da gangan da rana, tofa koda baikawo Maniyyiba ramuwa da
Kaffara sunhau kansa.
шαʟʟαнυ-тα'αʟα α'αʟαмυ
Doмυп пεмαп ƙαяıп вαчαпı sαı αdυвα шαɗαппαп ʟıтαттαғαı καмαя нακα:
HUKUNCIN FITAR MANIYYI DA AZUMI:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu
Alaikum. A cikin Azumi sha’awa tana takura min har da fitar maniyyi, kuma ban
san ana wanka domin hakan ba. Shi ne nike tambaya wai yaya zan yi a kan
sallolinna da azuminna?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus
Salaam Wa Rahmatul Laah.
Azumi lokaci
ne da musulmi ke yankewa daga bin sha’awoyin ciki da farji da sauran gaɓoɓin jiki. Lokaci ne
da yake ƙara kusantar Allaah Ta’aala da kyawawan ayyuka, kuma ya
yi nesa da dukkan ayyukan sheɗan na zalunci da cutar kai da cutar sauran jama’a.
Wajibi ne ga
mai azumi ya nisanci duk abin da ya san zai motsar masa da sha’awar jima’insa,
ta hanyar nisantar kallon fima-fimai ko karatun labarum batsa a cikin litaffan
soyayya ko keɓancewa da wanda ko wacce ba muharrama ba, da sauransu.
Wanda ya yi
sakaci har ya janyo aukuwan abin da ke ɓata azumin ta irin waɗannan hanyoyin da
makamantansu to ya sani cewa azuminsa ya ɓaci, kuma dole sai ya rama shi, tare da tuba ga Allaah da
neman gafararsa.
Haka ma
wanda ya bar yin sallah a tsawon lokacin da janaba ta same shi, wajibi ne ya
rama duk sallolin da ya yi sakaci a kan su kafin zuwan rasuwarsa, tare da tuba
da istighfari ga Ubangiji Ta’aala, musamman idan ya yi hakan a sakamakon sakaci
ne wurin neman ilimi.
Wajibi ne
kowane musulmi ya koyo ilimin abin da addininsa ba ya ingantuwa ko gyaruwa sai
da shi, kamar a babin Aqeeda da Tauhidi da Tsarki da Sallah da Azumi da
Mu’amalar Aure da Kasuwanci da Maƙwabtaka da sauransu.
Janaba tana
samuwa ga mutum ne idan ɗaya daga cikin waɗannan abubuwan ya auku:
1. Fitar
maniyyi daga namiji ko mace ta hanyar babbar sha’awa a barci ko a farke.
2. Fitar
maniyyi ta hanyar yin wasa da al’aura daga namiji ko mace.
3. Ɓacewar kan al’auran namiji (hashafa) a cikin farjin mace
kamar a lokacin saduwa, ko da kuwa ba su yi maniyyi ba.
Duk lokacin
da ɗaya daga cikin waɗannan abubuwan ya
auku, to janaba ta samu. Babu abin da ya rage ga mutum a lokacin sai dai ya yi
shirin kawar da ita, ta hanyar yin wankan da ake kira Wankan Janaba.
Daga cikin
hukunce-hukuncen da suka shafi Janaba da mai Janaba akwai:
1. Fitar
maniyyi ne yake jawo janaba amma ba fitar maziyyi ba a wurin namiji ko mace.
2. Sai dai
wajibi ne ga wanda maziyyin ya same shi ya wanke dukkan al’aurarsa gaba ɗaya, kuma ya sake
alwala.
3. Idan kuma
maziyyin ya shafi tufa ne to shari’a ta yi sassauci in aka ɗebi ruwa aka jiƙa wurin da ya shafan kawai, ya yi.
4. Yadda
mace za ta yi wankan Janaba daidai ne da yadda za ta yi na Haila. Sai dai ba
dole ne a janaba ta warware kitson kanta ba.
5. Wanda ya
yi mafarkin saduwa kuma da ya farka sai bai ga maniyyi ba, to janaba ba ta same
shi ba.
6. Wanda ya
farka daga barci kuma ya ga maniyyi a jikinsa alhali bai tuna yin wani mafarki
ba, duk da haka dai janaba ta same shi, namiji ne shi ko kuwa mace ce, ba
bambanci.
7. Wanda
maniyyi ya gangaro masa ba da sha’awa ba sai dai saboda rashin lafiya ko sanyi
ko dai makamancin haka, yawancin malamai sun ce janaba ba ta same shi ba.
8. Haɗuwa ko shafar
al’auran namiji da farjin mace ba tare da shigewa ciki ba wannan bai jawo musu
janaba ba. Amma in ɗayansu ya fitar da maniyyi, to shi ne ya yi janaba.
9. Idan
namiji ya sadu da mace: Ya shigar da abin da bai kai ‘hashafa’ watau kan
al’aurarsa ba, sai dai kuma maniyyinsa ya samu gangarawa cikin farjinta, sannan
ita kuma ba ta fitar da maniyyi ba, to a nan mijin ne kaɗai ya yi janaba ban
da matar.
10. Idan
kuma mace ta ƙare wankan janaba bayan saduwa sai kuma daga baya
maniyyin mijin ya gangaro ya fito mata, to a nan ba za ta sake yin wanka ba.
11. Amma ko
za ta sake alwala? Malamai sun saɓa wa juna. Mafi kyau dai shi ne: Ba za ta sake ba. Wal
Laahu A’lam.
Muhimman
mas’alolin da suka wajaba a kula da su sosai a ɓangaren wanka:
1. Siffar
yadda ake yin wankan janaba daidai yake da wankan Haila ko Nifaasi, sai dai a
wurin ɗaura niyya da
warware kitson gashin kai kawai.
2. Kar ki yi
fitsari a wurin da kike yin wanka, sai fa in shafaffe ko daɓaɓɓe ne kuma sai in
kin wanke shi sosai kafin fara yin wankan.
3. Ya
halatta ki yi wanka a tsirara matuƙar dai kina cikin rufaffen wurin da ba
wani mai iya ganinki ne.
4. Amma ki
kula da yin addu’ar Sunnah da ambaton sunan Allaah kafin shiga wurin ko kafin
tuɓe tufafin, domin
kare kanki daga idanun shaiɗanu.
5. Idan ba
ki samu rufaffen wuri ba sai wata ko wani muharraminki kamar miji ya kare ki da
labule tun daga farko har ƙarshen wankan.
6. Wadda
wankan Janaba da Haila suka hau kanta sai ta yi kowanne a matsayinsa kuma da
niyyarsa. In kuma ta haɗa su da niyya guda, waɗansu malaman sun
ce: Ya yi.
7. Ya
halatta miji ya kewaya dukkan matansa da yin wanka ɗaya. Sai dai ya yi
wanka ga kowace ɗaya ya fi.
8. Abin da
ya fi shi ne mai janaba ya yi wanka kafin ya yi barci, in kuwa bai samu dama ba
sai ya yi alwala ko taimama. In ya farka daga baya ya yi wankan.
9. Haka kuma
mai janaba ba zai ci abinci ba har sai bayan ya yi wanka ko kuma alwala.
10. Ya
halatta miji da mata su yi wanka tare a wuri ɗaya kuma su riƙa ɗiba daga ƙwatarniya ko bokiti ko baho ɗaya.
11. Ya
halatta su kalli al’aurar junansu a kowane lokaci. Da sauransu.
WALLAHU
A'ALAM
Sheikh
Muhammad Abdullaah Assalafiy
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
"المغني لإبن قدامة"
الشرح الممتع"
(6/234)
"المجموع للنووي"
(6/349)
AMSAWA
Mυѕтαρнα Uѕмαи
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.