𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Slm malam sama da so uku ke nan ina tura tambaya amma kuma ba amsa min, malam dan Allah a taimaka a amsa min wannan, akwai wani a unguwarmu, shi dai yana yawan yin istmna'i kuma baya yin wankan janaba sama da mako guda kuma yanayin azumi, kuma yana yin sallah da janaban, munyi munyi mun kasa hanashi, yaki ya haqura, in ya tuba daga bisani sai ya fara. Toh mallam Allah ya saka maka da alkhairi
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Dukkanin Malamai sun yi Ittifaki
akan cewa duk wanda ya fitar da Maniyyi daga jikinsa da gangan, acikin ranar da
yake azumi to azuminsa ya karye.
Sauran Maluman suna ganin cewar
zai rama azumi guda ɗaya
ne. Amma Imamu Malik yace wajibi ne sai ya yi ramukon tare da kaffarah. (Wato
Azumi 61 kenan) akan kowanne azumin Ramadan guda wanda ya karya.
Idan kuma cikin dare yake yin
istimna'in, to wannan rashin tsarkin jikinsa ba zai shafi azuminsa ba. Azuminsa
yana nan.
HUKUNCIN YIN SALLAH DA JANABAH
Yin Sallah da Janabah, yana daga
cikin mafiya girman Kaba'irori. Hasali ma yin hakan da gangan kamar yin riddah
ne.
Ya zama wajibi ku gabatar da
wannan mai laifin agaban Hukumar Musulunci. ko kuma wajen Malaman Unguwarku ko
garinku.
Za'a tambayeshi dalilinsa na yin
wannan ta'asar. Idan yana yin hakan ne saboda lalaci, ba tare da sanin haɗarin dake cikin yin hakan
ba, to za'a umurceshi da tuba sannan yaje ya yi wankan Janabah kuma ya rama
dukkan sallolin da yayisu da janabar.
Idan kuma yana sane da cewa ba'a
yin sallah sai da tsarki, Kuma yasan hatamcin yin sallah da janaba, amma ya yi ne
da gangan, Ko kuma shi ara'ayinsa bai yarda da wajibcin tsarkin hadasin ba, to
ya kafirta.
Hukuma zata iya zartar masa da
haddi mutukar dai an tabbatar da cewa acikin hayyacinsa yake, shi ba Mahaukaci
bane.
Ya kamata kuyi ma shari'ah gata,
Ku ɗauki matakin
kaishi gaban manya domin ladabtar dashi.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.