𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum, malam ina da tambaya, ya zan yi ramuwar
azimin shekara uku da ban yi ba a dalilin haihuwa kuma ina da olsa kuma mai sa
ni yinwa da wuri ce?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salamu, a lokacin da Allah S.W.T. ya wajabta
yin azumin Ramadana a kan Muminai, sai ya kawo sauqi ga marasa lafiya da
matafiya a kan shan azumin, su kuma rama a wasu ranakun na daban, da kuma ya
matsa gaba sai ya ce: "Abin da ke kan waɗanda
ba sa iya azumin shi ne fidiya, ciyar da miskinai..."
يَا أَيُّهَا
الَّذِينَ آمَنُوا كُتِبَ عَلَيْكُمُ الصِّيَامُ كَمَا كُتِبَ عَلَى الَّذِينَ مِن
قَبْلِكُمْ لَعَلَّكُمْ تَتَّقُونَ
Yã ku waɗanda
suka yi ĩmãni! An wajabta azumi a kanku kamar yadda aka wajabta shi a kan waɗanda suke daga gabãninku,
tsammãninku, zã ku yi taƙawa (Suratul Bakara aya ta 183)
أَيَّامًا
مَّعْدُودَاتٍ فَمَن كَانَ مِنكُم مَّرِيضًا أَوْ عَلَىٰ سَفَرٍ فَعِدَّةٌ مِّنْ أَيَّامٍ
أُخَرَ وَعَلَى الَّذِينَ يُطِيقُونَهُ فِدْيَةٌ طَعَامُ مِسْكِينٍ فَمَن تَطَوَّعَ
خَيْرًا فَهُوَ خَيْرٌ لَّهُ وَأَن تَصُومُوا خَيْرٌ لَّكُمْ إِن كُنتُمْ تَعْلَمُونَ
Kwanuka ƙidãyayyu.
To, wanda ya kasance daga gare ku majinyaci ko kuwa yana a kan tafiya, sai (ya
biya) adadi daga wasu kwanuka na dabam. Kuma a kan waɗanda suke yin sa da wahala akwai fansa;
ciyar da matalauci, sai dai wanda ya ƙãra
alhẽri
to, shi ne mafi alhẽri a gare shi. Kuma ku yi azumi (da wahalar) ne mafi alhẽri a
gare ku idan kun kasance kuna sani. (Suratul Bakara aya ta 184)
شَهْرُ
رَمَضَانَ الَّذِي أُنزِلَ فِيهِ الْقُرْآنُ هُدًى لِّلنَّاسِ وَبَيِّنَاتٍ مِّنَ الْهُدَىٰ
وَالْفُرْقَانِ فَمَن شَهِدَ مِنكُمُ الشَّهْرَ فَلْيَصُمْهُ وَمَن كَانَ مَرِيضًا
أَوْ عَلَىٰ سَفَرٍ فَعِدَّةٌ مِّنْ أَيَّامٍ أُخَرَ يُرِيدُ اللَّهُ بِكُمُ الْيُسْرَ
وَلَا يُرِيدُ بِكُمُ الْعُسْرَ وَلِتُكْمِلُوا الْعِدَّةَ وَلِتُكَبِّرُوا اللَّهَ
عَلَىٰ مَا هَدَاكُمْ وَلَعَلَّكُمْ تَشْكُرُونَ
Watan Ramadãna ne wanda aka saukar da Alƙur'ãni a cikinsa yana shiriya
ga mutãne da hujjõji bayyanannu daga shiriya
da rarrabẽwa.
To, wanda ya halarta daga gare ku a watan, sai ya azumce shi, kuma wanda ya
kasance majinyaci ko kuwa a kan tafiya, sai ya biya adadi daga wasu kwanuka na
dabam. Allah Yana nufin sauƙi gare ku, kuma ba Ya nufin tsanani gare
ku, kuma dõmin ku cika
adadin, kuma dõmin ku
girmama Allah a kan Yã
shiryar da ku, kuma tsammãninku,
zã ku gõde. (Suratul Bakara aya ta
185)
Malamai sun yi ma wannan aya fassarori mabambanta, amma ba
za mu tsawaita bayaninsu a nan ba, kawai abin da ke kan ki shi ne kowane azumi ɗaya ki ciyar masa da
miskini ɗaya a
madadinsa. Kuma wannan shi ne hukuncin waɗanda
suka gaza yin azumi saboda tsananin tsufa, ko rashin lafiyar da ba ta da alamar
warkewa, kuma ba za ta barsu su iya yin azumi ba, kamar yadda waccan ayar ta
tabbtar.
Don neman qarin bayani sai a duba Aljámi'u Li'ahkamil Qur'an
1/668-67.
Allah ne mafi sani.
Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.