Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Rike Alqur'ani A Lokacin Da Liman Yake Karatu A Sallah

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Malam idan liman Yana karatu a sallar tarawihi ko tahajjud muna bayansa muna riqe Alqur'ani (Mus-haf) muna dubawa ana sallah, shin yin haka ya halasta?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Yafi dacewa ga mai koyi da liman (Mamu kenan) a sallah kar ya riqe Qur'an a lokacin da liman yake karatu a sallah. Yafi kyau mamu ya natsu ya riqa sauraren karatun liman.

An miqa tambaya ga babban malami Shaykh bin Baaz (rahimahullah) cewa "Meye hukuncin mutum dake bin liman sallar taraweeh amma yana riqe da Al-qur'ani yana dubawa?"

Sai Shaykh bin Baaz (rahimahullah) ya amsa da cewa; Ban san wani asali (na Sunnah) ba ga yin hakan. Yafi dacewa ya natsu ya samu khushuu'i a sallar, kar ya riqe Qur'ani (Mus-haf), sannan ya dora hannunsa na dama akan na hagu akan qirjin sa domin yin hakan Sunnah ne. Wannan shi ne ra'ayi mafi kyau. Amma riqe mus-haf (Qur'ani) zai hana shi aiwatar da wannan Sunnah. Kuma idonsa da zuciyarsa zasu riqa kallon rubutun dake a shafukan mus-haf ɗin, yin haka zai hana shi sauraron karatun liman. Abinda nake tinani shi ne rashin riqe Qur'ani ga mamu shi yafi dacewa da sunnah, sannan ya yi sauraron karatun liman da kyau ba tareda ya riqe Mus-haf ba. Idan yanada ilimin Qur'ani, zai yiwa liman gyara idan ya yi kuskure a karatu. Idan kuma shi baida hadda mai karfi toh wasu mutane (sauran mamu) zasu yiwa liman gyara idan ya yi kuskure a karatu. Idan kuma aka rasa Wanda zai yiwa liman gyara idan ya yi kuskure, toh babu laifi. Daman kuskure acikin fatiha shi ne matsala, sabida Fatiha rukuni ce acikin sallah kuma sallah bata inganta saida cikar Fatiha. Idan aka bar ayah acikin karatun matuqar ba acikin suratul Fatiha bane, toh babu laifi idan babu mai iya gyara masa acikin mamu.

Idan acikin mamu babu wanda zai iya yiwa liman gyara idan ya yi kuskure ko tsallake acikin karatu, toh anan babu laifi mutum ɗaya ya riqe Qur'ani (Mus-haf) domin ya riqa yiwa liman gyara saboda larura ne. Amma idan kowane Mamu ya riqe Qur'ani (Mus-haf) toh wannan ya saɓawa Sunnah.

An sake tambayar Shaykh Bin Baaz (rahimahullah) akan cewa; "Wasu daga cikin jama'a (Mamu kenan) suna buɗe Qur'ani (Mus-haf) suna bibiyar karatun liman a sallah, shin akwai laifi a hakan?"

Sai ya amsa da cewa; Abinda ya bayyana agareni shi ne kar suyi hakan. Yafi kyau su maida hankalisu su kuma natsu ga sallah. Su dora hannayen su a qirjin su. Sannan suyi sauraron abinda liman ke karantawa. Saboda fadar Allah acikin Alqur'ani;

وَإِذَا قُرِئَ الْقُرْآنُ فَاسْتَمِعُوا لَهُ وَأَنصِتُوا لَعَلَّكُمْ تُرْحَمُونَ.

Kuma idan an karanta Alqur'ãni sai ku saurara gare shi, kuma ku yi shiru; Tsammãninku, anã yi muku rahama. (Suratul A'araaf Aya ta 204).

ﻗَﺪْ ﺃَﻓْﻠَﺢَ ﺍﻟْﻤُﺆْﻣِﻨُﻮﻥَ. ﺍﻟَّrﺬِﻳﻦَ ﻫُﻢْ ﻓِﻲ ﺻَﻼﺗِﻬِﻢْ ﺧَﺎﺷِﻌُﻮﻥَ.

Lalle ne, múminai sun sãmi babban rabõ. Waɗanda suke acikin sallar su mãsu tawãli'u ne. (Suratul muuminun aya ta 1-2).

ﻭقال ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ: ‏ﺇِﻧَّﻤَﺎ ﺟُﻌِﻞَ ﺍﻹِﻣَﺎﻡُ ﻟِﻴُﺆْﺗَﻢَّ ﺑِﻪِ ﻓَﺈِﺫَﺍ ﻛَﺒَّﺮَ ﻓَﻜَﺒِّﺮُﻭﺍ ﻭَﺇِﺫَﺍ ﻗَﺮَﺃَ ﻓَﺄَﻧْﺼِﺘُﻮ

Kuma Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) yace; An sanya muku liman domin kuyi koyi dashi, idan ya yi kabbara kuyi kabbara, idan yana karatu kuyi shiru (Kuyi sauraron karatun sa). (Majmu'ul Fataawa na Al-Shaykh Ibn Baaz, 11/340-342).

WALLAHU A'ALAM

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments