Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Dawowar Jinin Haila Bayan Ta Dauke

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Wasu matan jini ba ya ɗauke musu sai na kwana biyu ko uku kawai sai ya sake dawowa, meye hukuncin azumin mace da sallanta a irin wannan yanayin??

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Abunda yake sananne ne awurin mafiya yawan malamai shine idan mace tana al'ada sai tayi tsarki to zatayi wanka ta cigaba da Sallah da azumi, amma abinda zata gani bayan kwana biyu ko uku ba haila bane, domin mafi ƙarancin tsarki awurin waɗannan malaman kwana goma sha uku ne.

 Wasu malaman kuma sukace: aduk lokacin da mace ta ga jini to haila ne, idan taga tsarki to tsarkine, koda kuwa tsakanin hailan farko da ta biyun bai kai kwana goma sha ukun ba"

Dawowar Jinin Al'ada

TAMBAYA (151)

Assalamu alaikum Malam Ina yini ya aiki. Allah ya taimaka Malam dan Allah wata yar tambaya gare ni.

Nayi alada ne sati 4 da suka wuce har na fara sallah nah Kawai Sai satin da ya gabata jini ya dawo min Amma ba jini din nan dai da muka sani bani wannan wani brown ne haka yau sati daya kenan yaki tafiya ni kuma nayi wanka nah Ina sallah toh bansan ya matsayin sallar nawa take bah

AMSA

Waalaikumus salam warahmatullahi wabarakatuhu

Anan Zaki duba nau'in jinin ne. Idan nau'insa yayi kama da na haila to zaki dakatar da Ibadah ne saboda wannan alamu ne na cigaban al'ada amman idan nau'insa ba na haila bane to zaki dauke shi ne a matsayin jinin Istihadha sannan Kuma zaki ci gaba da ibadarki saidai zaki dinga sabunta alwala a tsakanin kowacce sallah

(Sahihul Bukhari [Arabic-English] Vol. 1 page 149 - Hadith #228)

Wallahu taala a'alam

Subhanakallahumma wabi hamdika ash-hadu anla'ilaha illa anta astaghfiruka wa'atubi ilayk

Amsawa

Usman Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa


ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments