𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Warahmatullah.
Malam menene Hukuncin wa'yanda suke cewa baza su ɗauki
azumi ba sai sun gan wata da idanunsu?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam warahamtullahi
Wabarkatuh
Wannan zance ne na ɓatattu. A zahirin
gaskiya, an fi samun irin Waɗannan
mutane a cikin 'yan dariku da 'yan gargajiya. Domin duk mai irin Wannan
fahimtar ba za a kira shi da Ahlus Sunnah ba, domin fahimta ce wacce ta saɓawa sunnar ma'aiki
(Sallallahu alaihi Wasallam). Sannan mafi yawan masu wannan dabi'a za ka samu
jahilai ne, ko kuma shagalallu waɗanda
suka shagala da al'amuran duniya, dalili kuwa shi ne; Za ka samu cewa ba a cika
ɗaukan azumi tare da
su ba, domin ba a kowane gari bane ake ganin wata a ranar da ya tsaya saboda
wasu dalili, amma kuma za ka samu cewa yawancin su tare da su ake aje azumi,
koda kuwa ba su cika azuminsu ba, domin ni da idona na ga waɗanda a wancan azumin da
ya gabata, azumi 28 suka yi aka ce an ga wata, kuma suka ajiye aka yi sallah
tare da su. Wannan ze nuna maka cewa lalaci ne da shagala take sawa suke aikata
hakan. Kuma koda ma sun ci gaba da azumin, to aikin banza suka yi domin Allah
ba zai karɓa ba, don
watan Ramadan ya riga ya tafi a wannan lokacin.
Shin me Waɗannan mutane suke takama da shi ne har
girman kai ya sa suka karkace wa fahimtar Annabi (Sallallahu alaihi
Wasallam)???
Ya tabbata a hadisi cewa, Ibn
Umar (r.a) ya ce: “ Mutane sun ga wata, sai na ba Annabi (Sallallahu alaihi
Wasallam) labari cewa; lallai nima na gan shi, sai ya yi azumi, kuma ya umarci
mutane da azumtarsa". Abu Dawud ya ruwaito shi, Hakim ya inganta shi da
Ibn hibban.
Wannan ke nuna cewa, fiyayyen
halitta (Sallallahu alaihi Wasallam) ma, wanda ya fi mu daraja ta kowani fanni,
an bashi labarin ganin wata kuma ya gasgata, ya yi azumi kuma ya yi umarni a
yi. To don me kai za ka ce sai ka gani da idonka? Ko kafi Annabi hikima da
wayau ne?? Ko kuwa girman kai ne da duhun jahilci da shagala???
Da zarar an ce ina masoya Annabi
(Sallallahu alaihi Wasallam) sai ku fara bambami, ku yi ta zagaye gari kuna
bugun kirji wai duk da sunan ku masoya manzo ne. To haka ake soyayya bacin ba
ku yin koyi da shi? Wallahi duk wanda ya bi wata hanya daban saɓanin ta Annabi Muhammad
Sallallahu alaihi Wasallam to Wallahi ya bi hanyar ɓata.
Ku sani! Saɓawa Manzon Allah
Sallallahu alaihi Wasallam, tamkar saɓawa
Allah ne. Allah (ﷻ) Ya ce:_
”.... وَمَن يَعصِ اللَّهَ وَرَسُولَهُۥ فَقَد ضَلَّ
ضَلَٰلًا مُّبِينًا“
“.... Kuma wanda ya saɓawa Allah da ManzonSa, to
hakika ya ɓace, ɓata mabayyaniya.”
(Al-Ahzab 36)
Don haka, Ina kara Fadakar da
'yan uwa Musulmi a kan mu bi Allah da ManzonSa Sallallahu alaihi Wasallam. Mu
guji bijiro da wani al'amari na daban.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
ƘARIN BAYANI
SHIN AKWAI HUJJA A
SHARI'A GA MUTUMIN DA YA CE BA ZAI YI AZUMI BA SAI YA GA WATA DA IDANUNSA, KUMA
MENENE HUKUNCIN WANDA YA BIJIRE WA SANARWAR SHUGABANNI KO MALAMAN MUSULUNCI?
Tambaya:
Wannan tambaya tana tafe ne
sakamakon wata ɗabi'a
da take ƙara
yaɗuwa tsakanin wasu
mutane, inda suke nuna taurin kai wajen ƙin karɓar
sanarwar ganin watan Ramadan muddin ba su ne suka ga watan da kansu ba. Shin
wannan yana cikin koyarwar Annabi (صلى الله عليه وسلم)? Kuma wane haɗari ne yake tattare da raba kan al'umma a
lokacin ibada?
Amsa:
Kuskuren Tauye Ibadar Azumi Ga
Ganin Ido Shi Kaɗai
A koyarwar Musulunci, ganin wata
shi ne silar fara azumi, amma shari'a ba ta ce sai kowane mutum guda ɗaya ya ga watan da kansa
ba. Madadin haka, shari'a ta ginu ne a kan Shaida (Shahada) ko Labari (Khbar)
daga mutum amintacce, adali, musulmi.
1. Koyarwar Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم)
Game Da Labarin Ganin Wata
Fiyayyen halitta (صلى الله عليه وسلم)
shi ne abin koyi gare mu. Tarihi da hadisai sun nuna cewa sau da dama Annabi (صلى الله عليه وسلم)
ya karɓi shaidar mutum
ɗaya ko biyu kuma ya
sa aka yi azumi ko aka ajiye.
Daga ɗan Umar (R.A) ya ce:
تَرَاءَى النَّاسُ الْهِلاَلَ فَأَخْبَرْتُ
رَسُولَ اللَّهِ صلى الله عليه وسلم أَنِّي رَأَيْتُهُ فَصَامَ وَأَمَرَ النَّاسَ بِصِيَامِهِ
“Mutane sun
nemi ganin wata (na Ramadan), sai na ba wa Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) labari cewa lallai
ni na gan shi. Sai ya yi azumi, kuma ya umarci mutane da su azumce shi.” (Sunan
Abu Dawud: 2342).
Wannan hadisi babban raddi ne ga
masu cewa sai sun ga wata da idonsu. Idan har Annabi (صلى الله عليه وسلم) bai ce sai ya ga
wata da idonsa ba, ya dogara da shaidar Abdullahi ɗan Umar, to wane ne mu da zamu ce sai mun
gani?
2. Haɗarin Sabawa Shugabanni (Ulul Amr)
Musulunci ya umarci muminai da su
yi biyayya ga shugabanni a cikin abubuwan da ba saɓon Allah ba ne. Idan hukumomin Musulunci
(kamar Majalisar koli ta harkokin addinin Musulunci a ƙasarmu) suka tabbatar da
ganin wata bayan tantance shaidu, to ya zama wajibi ga kowane musulmi ya bi
wannan sanarwa.
Allah Madaukakin Sarki ya ce:
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا أَطِيعُوا اللَّهَ
وَأَطِيعُوا الرَّسُولَ وَأُولِي الْأَمْرِ مِنْكُمْ
“Ya ku waɗanda kuka yi imani! Ku yi
biyayya ga Allah, kuma ku yi biyayya ga Manzo, da kuma shugabanni daga
cikinku.” (Suratun Nisa'i: 59).
Raba kan al'umma ta yadda wasu na
azumi wasu na ci, alhalin an bayar da sanarwa ta hukunci, yana janyo rauni ga
musulmi da kuma nuna rashin tsari a cikin addini.
3. Illolin Wannan Fahimta Ta
"Sai Na Gani"
Mutanen da suke da wannan dabi'ar
yawancin lokuta suna faɗawa
cikin kurakurai kamar haka:
Tauye Azumi: Sau da yawa suna
fara azumi a makare, wanda hakan yana sa su yi azumi 28 maimakon 29 ko 30.
Shari'ar Musulunci ta nuna cewa watan Musulunci ba ya gaza ranaku 29.
Girmama Kai (Kibir): Yin gaba da
malamai da shugabanni da nuna kamar kai ka fi su gaskiya ko kiyayewa.
Saɓa
wa Sunnah: Kamar yadda hadisin ɗan
Umar ya nuna, bin labarin amintacce shi ne Sunnah, ƙin bin sa kuma ɓata ne.
4. Menene Hukuncin Azumin Mutumin
Da Ya Ƙi
Bin Sanarwa?
Malamai sun bayyana cewa idan
mutum ya ƙi
yin azumi bayan an bayar da sanarwa ta shari'a, to ya aikata laifi babba na saɓa wa umarnin Allah da
Manzonsa. Kuma idan ya tashi ramawa daga baya, har yanzu akwai tababa a kan karɓuwar aikin nasa domin ya
fita daga cikin tsarin jama'ar musulmi.
Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) ya ce:
الصَّوْمُ يَوْمَ تَصُومُونَ وَالْفِطْرُ يَوْمَ
تُفْطِرُونَ وَالأَضْحَى يَوْمَ تُضَحُّونَ
“Azumi
(lokacinsa shi ne) ranar da kuke azumi (baki ɗaya),
karashen azumi kuma ranar da kuke buɗe
baki (baki ɗaya),
sallah layya kuma ranar da kuke yin layya (baki ɗaya).”
(Sunan At-Tirmidhi).
Wannan yana nuna cewa ibadar
azumi da sallah ayyuka ne na Jama'a, ba na daidaiku ba.
Kammalawa
Iƙirarin cewa "ba zan yi azumi ba sai
na ga wata da idona" ba ra'ayi ne na ilimi ba, a'a, ra'ayi ne na jahilci
da kuma girman kai. Wajibi ne musulmi ya koma ga tafarkin Sunnah ta hanyar bin
labarin gaskiya daga amintattu. Idan hukumomi suka ce an ga wata, kai kuma ba
ka gani ba, to idon wanda ya gani ya isar maka, kamar yadda idon ɗan Umar ya isar wa sauran
sahabbai.
Allah ya sa mu zama masu bin
Sunnah a kowane hali, ya kuma kare mu daga girman kan da zai kai mu ga ɓata.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Du5LNx31U9hDi6RQbbrzgW
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.