Ticker

6/recent/ticker-posts

Ba Zan Dauki Azumi Ba Har Sai Na Ga Wata Da Idanu Na

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum Warahmatullah. Malam menene Hukuncin wa'yanda suke cewa baza su ɗauki azumi ba sai sun gan wata da idanunsu?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salam warahamtullahi Wabarkatuh

Wannan zance ne na ɓatattu. A zahirin gaskiya, an fi samun irin Waɗannan mutane a cikin 'yan dariku da 'yan gargajiya. Domin duk mai irin Wannan fahimtar ba za a kira shi da Ahlus Sunnah ba, domin fahimta ce wacce ta saɓawa sunnar ma'aiki (Sallallahu alaihi Wasallam). Sannan mafi yawan masu wannan dabi'a za ka samu jahilai ne, ko kuma shagalallu waɗanda suka shagala da al'amuran duniya, dalili kuwa shi ne; Za ka samu cewa ba a cika ɗaukan azumi tare da su ba, domin ba a kowane gari bane ake ganin wata a ranar da ya tsaya saboda wasu dalili, amma kuma za ka samu cewa yawancin su tare da su ake aje azumi, koda kuwa ba su cika azuminsu ba, domin ni da idona na ga waɗanda a wancan azumin da ya gabata, azumi 28 suka yi aka ce an ga wata, kuma suka ajiye aka yi sallah tare da su. Wannan ze nuna maka cewa lalaci ne da shagala take sawa suke aikata hakan. Kuma koda ma sun ci gaba da azumin, to aikin banza suka yi domin Allah ba zai karɓa ba, don watan Ramadan ya riga ya tafi a wannan lokacin.

Shin me Waɗannan mutane suke takama da shi ne har girman kai ya sa suka karkace wa fahimtar Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam)???

Ya tabbata a hadisi cewa, Ibn Umar (r.a) ya ce: “ Mutane sun ga wata, sai na ba Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam) labari cewa; lallai nima na gan shi, sai ya yi azumi, kuma ya umarci mutane da azumtarsa". Abu Dawud ya ruwaito shi, Hakim ya inganta shi da Ibn hibban.

Wannan ke nuna cewa, fiyayyen halitta (Sallallahu alaihi Wasallam) ma, wanda ya fi mu daraja ta kowani fanni, an bashi labarin ganin wata kuma ya gasgata, ya yi azumi kuma ya yi umarni a yi. To don me kai za ka ce sai ka gani da idonka? Ko kafi Annabi hikima da wayau ne?? Ko kuwa girman kai ne da duhun jahilci da shagala???

Da zarar an ce ina masoya Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam) sai ku fara bambami, ku yi ta zagaye gari kuna bugun kirji wai duk da sunan ku masoya manzo ne. To haka ake soyayya bacin ba ku yin koyi da shi? Wallahi duk wanda ya bi wata hanya daban saɓanin ta Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallam to Wallahi ya bi hanyar ɓata.

Ku sani! Saɓawa Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam, tamkar saɓawa Allah ne. Allah () Ya ce:_

.... وَمَن يَعصِ اللَّهَ وَرَسُولَهُۥ فَقَد ضَلَّ ضَلَٰلًا مُّبِينًا

.... Kuma wanda ya saɓawa Allah da ManzonSa, to hakika ya ɓace, ɓata mabayyaniya.” (Al-Ahzab 36)

Don haka, Ina kara Fadakar da 'yan uwa Musulmi a kan mu bi Allah da ManzonSa Sallallahu alaihi Wasallam. Mu guji bijiro da wani al'amari na daban.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/Du5LNx31U9hDi6RQbbrzgW

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments