Ticker

6/recent/ticker-posts

Nayi Karyar Mafarkin Annabi ﷺ

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Salam, Ina Rokon Allah ya kare mana malam tare da iyalansa malam Allah yasa daga cikin yayanka a samo wanda zai gaji taimakon da kake amin. Malam nine nayi karyar mafarkin Annabi shin meye hukuncina kuma zan iya tuba? Allah ya bada ikon ansawa.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaykumus Salam, Ina rokon Allah ya shirya mana zuri'armu duka, babu shakkah Karya tana daga cikin manyan aibukan harshe, it ace kuma matattarar kowane sharri.

Har ma Allah (swt) a cikin Alqur'ani Yana Cewa

إِنَّمَا يَفْتَرِي الْكَذِبَ الَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ بِآيَاتِ اللَّهِ وَأُولَٰئِكَ هُمُ الْكَاذِبُونَ 

Abin sani kawai waɗanda ba su yin ĩmani da ayoyin Allah, sũ ne suke ƙirƙira ƙarya. Kuma waɗannan sũ ne maƙaryata. (Suratul Nahl aya ta 105).

Bayan Haka Imamu Bukhari da Imamu Muslin sun Ruwaito wani hadisi wanda Annabi Sallallahu alaihi Wasallam Ke gaya mana cewa karya takan kai mutum a wuta.

Annabi Sallallahu alaihi Wasallam yana cewa, “Ku kiyayi karya, domin ita karya tana jan mutum zuwa Saɓon Allah, shikuwa Saɓon Allah yana kai mutum zuwa ga wuta, hakika mutum ba zai gushe ba

yana karya har sai an rubuta shi a wajen Allah cewa shi makaryaci ne”. (Imamu Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi).

Qarya babban zunubi ce wadda ayoyi da hadisai sukayi magana akan haramcinta da kuma narkon azabar da za ayiwa makaryaci. Musamman ma yiwa Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam) Qarya.

An Ruwaito hadisi Cewa, Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam) yana Cewa, “Duk wanda ya yi mini karya da gangan, to ya tanadi mazauninsa a cikin wuta” (Bukhari da Muslim).

A wani hadisin kuwa Cewa, yayi “Duk wanda ya fadi mafarkin karya, to za a tilasta masa daya

daura tsakanin siraran gashi guda biyu, kuma ba zai taɓa iyawa ba”, (Bukhari ne ya ruwaito shi).

Hakika ka aikata babban kuskure wanda kuma da ka mutu a Cikin wannan halin da zaka tarar da abinda baka so a gobe qiyama.

Don haka ka tashi tsaye wajen tuba ga Allah (swt) domin Allah yana Cewa

وَمَا كَانَ اللَّهُ لِيُعَذِّبَهُمْ وَأَنتَ فِيهِمْ وَمَا كَانَ اللَّهُ مُعَذِّبَهُمْ وَهُمْ يَسْتَغْفِرُونَ

Kuma Allah bai kasance Yana yi musu azaba ba alhali kuwa kai kana cikinsu, kuma Allah bai kasance Mai yi musu azaba ba alhali kuwa suna yin istigfari. (Suratul Anfal ayata 33).

Ina Rokon Allah ya yafema ya yafe mana.

Daga karshe, muna jan hankalin Masu ganin Rubutu game da Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam) suna haɗawa ba tare da sanin sahihancin sa ba. Domin Shima Yiwa Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam) Karyane.

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments