Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Wanda Ya Kashe Kafiri

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As-Salaam Alaikum. Wanda ya kashe kafiri ko zai yi kaffara?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah.

Malamai sun ce: kafirai nau’i-nau’i ne: Waɗanda ake yaƙi da su da waɗanda ba haka ba. Waɗanda ba a yaƙi da su kuma nauuka uku ne: Zimmiyai da Muaahadai da kuma Mustaamanai.

1. ZIMMIYYAI su ne waɗanda aka ƙulla alƙawarin zaman tare na aminci tsakaninmu da su.

2. MU’AAHADAI su ne waɗanda aka ƙulla yarjejeniyar tsagaita wutar yaƙi a tsakaninmu da su.

3. MUSTA’AMANAI kuwa su ne waɗanda suka shigo garinmu cikin aminci domin kasuwanci ko wani aiki ko ziyarar ɗan’uwa da sauransu.

Musulunci bai yarda a kashe wani daga cikin waɗannan nau’ukan guda uku ba saboda maganarsa (Subhaanahu Wa Ta’aala) cewa

وَمَا كَانَ لِمُؤْمِنٍ أَنْ يَقْتُلَ مُؤْمِناً إِلا خَطَأً، وَمَنْ قَتَلَ مُؤْمِناً خَطَأً فَتَحْرِيرُ رَقَبَةٍ مُؤْمِنَةٍ، وَدِيَةٌ مُسَلَّمَةٌ إِلَى أَهْلِهِ إِلا أَنْ يَصَّدَّقُوا، فَإِنْ كَانَ مِنْ قَوْمٍ عَدُوٍّ لَكُمْ وَهُوَ مُؤْمِنٌ فَتَحْرِيرُ رَقَبَةٍ مُؤْمِنَةٍ، وَإِنْ كَانَ مِنْ قَوْمٍ بَيْنَكُمْ وَبَيْنَهُمْ مِيثَاقٌ فَدِيَةٌ مُسَلَّمَةٌ إِلَى أَهْلِهِ وَتَحْرِيرُ رَقَبَةٍ مُؤْمِنَةٍ، فَمَنْ لَمْ يَجِدْ فَصِيَامُ شَهْرَيْنِ مُتَتَابِعَيْنِ تَوْبَةً مِنَ اللَّهِ، وَكَانَ اللَّهُ عَلِيماً حَكِيماً

Bai kamaci mumini ya kashe wani mumini ba sai dai a bisa kuskure. To, duk wanda ya kashe mumini a bisa kuskure sai ya ’yanta baiwa mumina, da kuma diyya da za a bayar ga dangin mamacin, sai dai ko in sun yafe. Idan kuwa daga cikin mutane ne maƙiya gare ku alhali kuma shi musulmi ne, to sai ya yanta baiwa mumina. Idan kuwa yana daga cikin mutane ne da kuke da alƙawarin aminci a tsakaninku da su, to akwai diyya abin bayarwa ga iyalinsa, da kuma yanta baiwa mumina. Wanda kuma bai samu iko ba sai ya yi azumin watanni biyu a jere. Wannan hanyar samun tuba ce daga Allaah. Kuma Allaah ya kasance Masani ne Mai Hikima. (Surah An-Nisaa’: 92).

Ƙarshen wannan ayar ta nuna, wanda ya kashe kafirin da musulunci ya tsare jininsa, akwai abubuwa biyu a kansa

1. DIYYA: Wacce zai bayar ga dangin mamacin, muddin dai babu yaƙi a tsakaninmu da danginsa.

2. KAFFARA: ’Yanta baiwa mumina, ko kuma azumin watanni biyu a jere idan bai samu baiwar ba.

Wannan ce maganar malamai masu yawa.

Waɗansu sun zaɓi cewa babu kaffara a kan wanda ya kashe kafiri da kuskure, saboda abin da ya zo a farkon ayar cewa

 وَمَنْ قَتَلَ مُؤْمِنًا خَطَأً فَتَحْرِيرُ رَقَبَةٍ مُؤْمِنَةٍ

Kuma wanda ya kashe mumini a bisa kuskure sai ya ’yanta baiwa mumina. (Surah An-Nisaa’i: 92).

Suka ce: Abin fahimta daga wannan shi ne: Babu kaffara idan wanda aka kashe ba mumini ba ne.

Amma kuma hukuncin kaffara a cikin maganarsa

وَإِنْ كَانَ مِنْ قَوْمٍ بَيْنَكُمْ وَبَيْنَهُمْ مِيثَاقٌ فَدِيَةٌ مُسَلَّمَةٌ إِلَى أَهْلِهِ وَتَحْرِيرُ رَقَبَةٍ مُؤْمِنَةٍ

Idan kuwa yana daga cikin mutane ne da kuke da alƙawari a tsakaninku da su, to akwai diyya abin bayarwa ga iyalinsa, da kuma yanta baiwa mumina. (Surah An-Nisaa: 92).

Wannan magana ce Manɗuuqiya, wacce kuma ake gabatarwa a kan Mafhuumiyar maganar ayar da suka janyo.

Kuma dayake wannan kafirin da aka kashe yana da alƙawari mai ƙarfi a tsakaninmu da shi kamar yadda ayar ta nuna, to ya shiga cikin Mantuuq na ayar.

Haka kuma dayake shi ɗan Adam ne da aka kashe shi a bisa zalunci, to ya zama kamar musulmi kenan, wanda lallai a yi kaffara a kan kashe shi.

Daga cikin malaman da suka zaɓi wannan maganar akwai At-Tabariy (9/43) da Al-Qurtubiy (5/325) da Ibn Katheer (2/376) da Ibn Qudaamah a cikin Al-Mughnee (12/224).

WALLAHU A'ALAM

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Ga masu tambaya sai su turo ta WhatsApp number: 08021117734

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/Fb6qgYPXfEeHb8CD1SWAkK

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments