Ticker

6/recent/ticker-posts

Wakar Garin Kwaki Ta Shek Abubakar Atiku Sanka

Waƙar Kwaki ta Shaykh Abubakar Atiku Sanka da almajirinsa Shaykh Balarabe Jaruna Jega, an rubuta waƙar a shekarar 1942 lokacin wata yunwa da akai a ƙasar Kano.
1. Fana fara da sunan Jalla sarki
Tabaraka wanda shi yab bamu kwaki

2. Yasa muka zam musulmi jalla shine
Ya aiko du Ma'aaika mai saraki

3. Da tauhidi da addini kawimi
Zuwa dukkan talakka har saraki 

4. Ilahal arshi mai kudura irada
Alimun Wahidun sarkin saraki

5. Fa shine yai halitta kullihinta
Hakimun wanda yai doki da Jaki

6. Jamadun har Mala'ikku da jinnu
Kazaka mutum da dukkan masu baki 

7. Abin ruwa ne fa ko na cikin kasane
Adan ikonsa yai kura da Zaki

8. Sannan ya bukatashemu mu duk
Zuwa neman abin sawa a baki

9. Fa dabbobi ciyawa anka basu
Mutane ko ya bamu hadi da kwaki

10. Fa dabbobi ciyawa girman sarauta
Muna dada godiya da ya bamu kwaki
         
Haƙiƙaninsa

11. Fa shi dai dan sarauta ne garinsu
Adon haka bashi yawo shifa kwaki

12. Izan ya so fita kuma za shi yawo
Fa sai izni fa yazo gun yan saraki

13. Suwo izni gareshi suwo
Shiga jirgi nufi nasa kunji kwaki 
               
 Fitowarsa daga garinsu 

14. Da yayi nufin kano izini ya nema
Ya hau jirgi yana sukuwassa kwaki

15. Yazo kano ya sauka wurin Akawu
Acan a tasha ya sauka kusan fa kwaki

16. Da Talakawa da masu kudin gari du
Suna tarbansa can a tasha fa kwaki

17. Zuwansa Kano kusan yaki yazo yi
Ya kawo taimako a garemu kwaki

18. Kazo nan zan gaya maka dan uwana
Fa girman kai ka daina yiwa su rogo kwaki

19. Izan dai dukiya ce taƙamarka
Fa Ɗantatan mu yai caffa ga kwaki  

20. Izan kuma dan sarauta takamarka
Fa ga sarkin Kano ya san da kwaki

           Saukar sa a Kano

21. A zamani na Abdullahi yazzo
Cikin birnin kano babban saraki 

22. Cikin hijra alif da dari da maitan
Da sittin sai guda daya munga kwaki 

23. A zamani na Abbas yazzo fa amma
Azamani na Usman babu kwaki  

24. Ya sauka tasha yana khudba fa kullum
Kuzo ku gareni nine rogo kwaki

25. Mutane sun rijif sunje gareshi
Suna caffa suna gaisheshi kwaki

26. Da dattijai da yara yan ƙanana
Da yan mata da masu zama a jaki

27. Inyamuri har samari manya-manya
Anan a kano suna ladabi ga kwaki

28. Mutan Sabon gari da Fagge na gansu
Suna rurubi wurin gaisar da kwaki.

Halayensa da Ɗabi’unsa

29. Fa shidai walla saukin kai gareshi
Fa baya ja da kowa kunji kwaki

30. Fa domin ko talakka sayo ya cishi
Da sauki zaya cishi halinsa kwaki

31. Akan samai ruwa fa kadan a cishi
Ana ma hanfudashi kadai a baki

32. Izan kuwa anka so wahala gareshi
Fa sai yazamo abincin yan saraki

33. Akan teba dashi da miya ta kwanbo
Da man shanu da nama kanci kwaki

34. Akwai ajabi cikin gari na rogo
Abincin yan mutanan yamma kwaki [1]

35. Fa yayi musharaka da hadin kasammu
Kamar Gero da Dawa harda Wake

36. Kazalika harda shinkafa hakannan
Kamad da Alkama Doya yi kwaki

37. Ana waina da Alkaki dashi har
Akanyi Wasa-wasa dana rogo kwaki

38. Izan an rafka taushe ankasa Mai
Da nama ya zamo sai yan saraki

39. Izan anso fura nono akan sa
Adama ko da sukkar anci kwaki

40. Akanyi Tuwo dashi a gama da Gari
A tuke sai aci da Miya fa kwaki

41. Akanyi tuwo na shinkafa a tuke
Asa taushe fasai shagali da kwaki

42. Ana Dambu dashi a gama da Ganye
Akwai shi da martabobi rogo kwaki

43. Ya kanyi fushi izan an bata ransa
Barin ladabi  ka motsa fushin saraki

44. Idan ka jikashi tun baka dakata ba
Ya kumbura wanga shi ka fusata kwaki

45. Izan ka shashi lallai zaiyi illah
Cikin ciki sai ya kumbura yai na Jaki

46. Su kwaki ai saraki ne hakika
Fa wake yin irin mulkinsa kwaki ?

47. Adon hakanan da zamaninsa yazzo
Faba motsi gurin sauran saraki

48. Su Gero sun fake hakanan su Dawa
Adan sababin zuwan Babansu kwaki

49. Su Wake ba mujin motsinsu su du
Su Masra sun fake sun tsorci kwaki

50. Su Rogo su Dankali duk sunka buya
Faba'a ganinsu don tsoronsa kwaki

51. Su Zogale sai ka barsu makaryata ne
Su Tafasa du kazam ladabi ga kwaki

56. Rama ma tayi karya tun a bara
Adan haka sai ta buya da taji kwaki

57. Sarautar tasa ba Kadhi da Joji
Adon yaki yazo shi Rogo kwaki

58. Walakin dai akwai ofis gareshi
Cikin kwano yake mulkinsa kwaki

59. Kuli-kuli shi kadai ya tsayawa daga
Gurin sarkinsa shine madawaki

60. Izan an nemi sulke sai fa mansa
Akan yafa su gishirine Dawaki

61. Su Barkono kusan sune mabusa
Gurin yaki sukan zuga rogo kwaki

62. Takobi cokaline babu shakka
Da yatsu ne kibobin Rogo kwaki

63. Idan damarunsa dun a yaki
Nufinsa shigi cikin kofa ta baki

64. Izan akasa ruwa bayan hakannan
Fa bom kenan na Garin Rogo Kwaki

Daga:
Muhammad Tatuhu
Zauren Makaɗa da Mawaƙa
Wakar Garin Kwaki Ta Shek Abubakar Atiku Sanka

Post a Comment

0 Comments