𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam
Alaikum. Ba na iya lanƙwashe ƙafata saboda rashin lafiya, don haka nake yin sallah a kan kujera
da nuni, amma sai aka ce wai sai dai in yi a ƙasa saboda sujada dole ce, kuma zan iya.
Wanne ne daidai?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus
Salaam Wa Rahmatul Laahi Wa Barakaatuh.
Dokokin
Shari’ar musulunci an ɗora
su ne a kan musulmi ya aikata su da gwargwadon ƙarfi da ikonsa. Allaah Ta’aala ya ce
فَاتَّقُوا اللَّهَ مَا اسْتَطَعْتُم
Sai ku tsare
dokokin Allaah daidai iyawanku. (Surah At-Taghaabun: 16).
Kuma Manzon
Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce
« إِذَا نَهَيْتُكُمْ عَنْ شَىْءٍ فَاجْتَنِبُوهُ ، وَإِذَا أَمَرْتُكُمْ
بِأَمْرٍ فَأْتُوا مِنْهُ مَا اسْتَطَعْتُمْ »
Idan na hana
ku wani abu, to ku nisance shi. Idan kuma na umurce ku da wani abu, sai ku zo
da gwargwadon iyawarku daga cikinsa. (Sahih Al-Bukhaariy: 7288; Sahih muslim:
6259).
Wannan a dunƙule
kenan.
Amma a kan
sallah a keɓance
kuma Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya fayyace komai, a
inda ya ce
« صَلِّ قَائِمًا ، فَإِنْ لَمْ
تَسْتَطِعْ فَقَاعِدًا ، فَإِنْ لَمْ
تَسْتَطِعْ فَعَلَى جَنْبٍ »
Ka yi sallah a
tsaye, idan kuwa ba za ka iya ba, to a zaune. Idan kuma ba za ka iya ba, to a
gefen jiki (a kwance). (Sahih Al-Bukhaariy: 1117).
Sannan kuma
Abdullaah Bn Umar (Radiyal Laahu Anhumaa) ya ce
كَانَ
النَّبِىُّ - صلى الله عليه وسلم - يُصَلِّى فِى السَّفَرِ عَلَى رَاحِلَتِهِ ، حَيْثُ تَوَجَّهَتْ
بِهِ ، يُومِئُ إِيمَاءً
، صَلاَةَ اللَّيْلِ إِلاَّ الْفَرَائِضَ ، وَيُوتِرُ عَلَى
رَاحِلَتِهِ .
Annabi (Sallal
Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya kasance yana yin sallah a cikin halin
tafiya a kan taguwarsa duk ta inda ta fuskanta da shi, yana yin ishara da
kansa, a sallar dare sai dai farilla. Kuma yana yin wutri a kan taguwarsa.
(Sahih Al-Bukhaariy: 1000).
Wannan ya
nuna, idan mutum ba zai iya yin ruku’u ko sujada ba, to sai ya yi nuni da kansa
a maimakon ruku’u da sujadar.
Kamar dai
yadda Ibn Umar (Radiyal Laahu Anhumaa) ɗin
dai ya ƙara
bayanin wannan abin a cikin wata riwayarsa mai cewa
عَادَ رَسُولُ اللهِ - صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ - رَجُلًا مِنْ أَصْحَابِهِ مَرِيضًا، وَأَنَا مَعَهُ فَدَخَلَ عَلَيْهِ، وَهُوَ يُصَلِّي عَلَى عُودٍ فَوَضَعَ جَبْهَتَهُ عَلَى الْعُودِ فَأَوْمَأَ إِلَيْهِ فَطَرَحَ الْعُودَ وَأَخَذَ وِسَادَةً فَقَالَ رَسُولُ اللهِ - صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ -: «دَعْهَا عَنْكَ إِنِ اسْتَطَعْتَ أَنْ تَسْجُدَ عَلَى الْأَرْضِ، وَإِلَّا فَأَوْمِئْ إِيمَاءً، وَاجْعَلْ سُجُودَكَ أَخْفَضَ مِنْ رُكُوعِكِ»
Manzon Allaah
(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya je duba wani mutum mara lafiya daga
cikin sahabbansa, alhali ina tare da shi a lokacin. Sai ya shiga wurinsa ya
tarar da shi yana sallah a kan wata sanda, yana ɗora
goshinsa a kan sandar. Sai ya yi masa ishara, sai ya jefar da sandar. Sai kuma
ya ɗauki matashin
kai. Sai Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce: ‘Ka aje
wannan shi ma: Idan za ka iya yin sujada a kan ƙasa, ka yi. Idan kuwa ba za ka iya ba,
sai ka yi nuni (ishara). Ka sanya sujudarka ta fi ruku’unka yin ƙasa.’ (At-Tabaraaniy ya riwaito shi a cikin Al-Mu’ujamul Kabeer: 13082).
A cikin
Al-Silsilatus Saheehah: (323) Al-Albaaniy ya ce
هَذَا إسْنَادٌ صَحِيحٌ رِجَالُهُ كُلُّهُمْ ثِقَاتٌ
Wannan isnadi
sahihi ne, mazajensa dukkansu amintattu ne. (As-Saheehah: 1/577).
Shi kansa Ibn
Umar (Radiyal Laahu Anhu) ɗin
ya yi aiki da wannan hadisin a lokacin da ya shiga wurin Hafs Bn Asim don duba
shi a kan rashin lafiyar da ke tare da shi, kuma ya tarar ya shimfiɗa wani ƙyalle
a kan matashin kai yana yin sujuda a kansa, sai ya ce
يَا ابْنَ أَخِي لَا تَصْنَعْ هَذَا ، تَنَاوَلِ الْأَرْضَ
بِوَجْهِكَ ، فَإنْ لَمْ
تَقْدِرْ عَلَى ذَلِكَ ، فَأَوْمِئْ بِرَأْسِكَ
إيمَاءً
Ya kai ɗan gidan ɗan’uwana, kar ka aikata
haka. Ka shafi kan ƙasa da goshinka, idan kuma ba za ka iya ba sai ka yi ishara da
kanka. (Musnad Abi-Awaanah: 2/338).
Al-Albaaniy a
cikin As-Saheehah ya ce
سَنَدُهُ صَحِيحٌ عَلَى شَرْطِ الشَّيْخَيْنِ
Isnadinsa
sahihi ne a kan sharaɗin
Al-Bukhaariy da Muslim.
Saboda waɗannan hadisai da atharai
ne wataƙila
malamai suka ce:
إِذَا تَعَذَّرَ عَلَى الْمُصَلِّي صِفَةٌ مِنْ صِفَاتِ صَلَاةِ الْعَلِيلِ الْوَارِدَةِ، أَتَى بِالصَّلَاةِ عَلَى صِفَةٍ أُخْرَى مِمَّا وَرَدَ، ثُمَّ يَفْعَلُ مَا قَدَرَ عَلَيْهِ وَدَخَلَ تَحْتَ اسْتِطَاعَتِهِ.
Idan mai
sallah ya kasa yin sallah a kan wata siffa daga cikin siffofin sallar mara
lafiya da suka zo a cikin riwayoyi, sai ya aikata sallar a kan wata siffa daga
cikin waɗanda aka
kawo a hadisai. Sai kuma ya aikata abin da yake da iko a kansa, kuma abin da ya
shiga ƙarƙashin
iyawarsa. (At-Ta’aleeqaatur
Radiyyah: 1/312).
A ƙarƙashin
waɗannan nassoshi da
bayanai a taƙaice, za mu iya cewa ya halatta ga wanda ba ya iya lanƙwanshe
ƙafarsa
ya yi sallarsa ko dai a zaune a kan ƙasa, kamar yadda hadisin wanda aka hana
shi sujada a kan matashin kai ya nuna. Ko kuma ya yi sallar a zaune a kan
kujera, kamar yadda hadisin sallarsa (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) a
kan taguwa ya nuna. A duk waɗannan
halayen yana duƙawa da yin ishara ne da kansa a maimakon ruku’u da sujada.
Kodayake
sallar nafila ce kaɗai
a halin tafiya hadisin yin sallah a kan taguwa ya nuna, amma dai malamai sun
yarda cewa, idan larura ta kama mutum yana iya yin farillar ma a kan abin
hawar, kamar idan ya ji tsoron ficewar lokaci, ko tsaron rasa abokan tafiya, ko
kuma salwantar rayuwa ko dukiya idan ya tsaya don yin sallar a ƙasa.
Idan haka ne
kuwa, ashe wanda larurarsa ta fi hakan, watau kamar wanda ba ya iya lanƙwashe
ƙafarsa,
watau wanda ba ya iya yin sujada daidai alhali yana zaune da ƙafarsa
a miƙe,
ko wanda ba ya iya zaman sallah daidai sai dai ya miƙe a kan gwiwoyinsa da
ya kafa su a kan ƙasa, irin wannan shi ma ba za a hana shi yin sallarsa daga
zaune a kan kujera ba, yana mai yin nuni da bayansa da kansa a maimakon ruku’u da sujada, in shà Allâh.
Yin sallar a
kan kujera kamar yadda muka bayyana a sama, shi ya fi kama da surar sallar da
Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya yi a kan raƙumi.
Wannan kuwa shi ya fi miƙewa a kan gwiwoyinsa a wurin zama a tsakanin sujuda biyu da
zaman tahiya, kamar yadda yawancinsu suke aikatawa a masallatai.
Allaah ya ƙara
mana fahimta a cikin addininmu.
WALLAHU A'ALAM
6
Sheikh
Muhammad Abdullaah Assalafiy
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.