𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu
alaikum, malam shin ya halatta na sadu da ɗaya
daga cikin matana koda ba ranar kwananta bane?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus
salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
A'a bai
halatta ba. Domin hakika yin hakan yana daga cikin zalunci. Kuma Allah (SWT) ya wajabta yin
adalci ga duk wanda zai zauna da mata. Allah yace :
فَانْكِحُوا
مَا طَابَ لَكُمْ مِنَ النِّسَاءِ مَثْنَىٰ وَثُلَاثَ وَرُبَاعَ ۖ فَإِنْ خِفْتُمْ
أَلَّا تَعْدِلُوا فَوَاحِدَةً أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُكُمْ ۚ ذَٰلِكَ أَدْنَىٰ
أَلَّا تَعُولُوا
Ku auri abin
da ya yi muku dãɗi
daga mãtã; biyu-biyu, da uku-uku, da huɗu-huɗu. Sa'annan idan kun ji
tsõron bã zã ku yi ãdalci ba, to, (ku auri) guda ko kuwa abin da hannayenku na
dama suka mallaka (baiwa). Wannan shi ne mafi kusantar zama ba ku wuce haddi
ba. (Suratun-Nisa'i 3)
Wato wajibi ne
ka raba lokutanka a tsakanin matanka daidai da daidai. Kada ka sadu da wata daga
cikinsu sai aranar girkinta. Kuma wajibi ne ka basu abinci, sutura, muhalli,
bisa adalci gwargwadon damar da Allah ya huwace maka.
Haƙƙin
miji ne kar ya sadu da wata daga cikin matansa sai wacce ita ce ke da kwana, ko
kuma idan akwai amincewa da yarda daga wacce ta ke da kwanan. Yana iya shiga
wurin matarsa da ba ita ce mai girki ba da rana idan akwai larura, kamar bayar
da kuɗin cefane, ko
binciken lafiyarta, ko warware wata matsala da makamatan haka. Bai halatta ya
sadu da wacce ba kwananta ko girkinta ba a lokacin da ya shiga wurinta don wata
buƙata
daga cikin buƙatun da ambatonsu ya gabata. Haƙƙin mata ne kar ta yarda mijinta ya sadu
da ita idan dai ba kwananta ba ne, ko in ba da izinin wadda ta ke da kwanan ba.
Idan har kasan
ba zaka iya yin adalci atsakaninsu ba, to bai halatta ka Qara auren ba. Domin
hakika Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yace: "Wanda ya kasance
yana da Mata biyu, sai ya karkata zuwa ga ɗayar
cikinsu, to zai zo aranar Alqiyamah alhali tsagin jikinsa ya karkace (wato ya
shanye, yana tafiya a tazgade). Tirmidhiy da Nisa'iy da Abu Dawud da Ibnu
Maajah ne suka ruwaitoshi.
A’ishah
Ummul-Mu’mineen (Radiyal Laahu Anhaa) ta ce
كَانَ رَسُولُ اللَّهِ - صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ - لاَ يُفَضِّلُ بَعْضَنَا عَلَى بَعْضٍ فِى الْقَسْمِ ، مِنْ مُكْثِهِ
عِنْدَنَا ، وَكَانَ قَلَّ
يَوْمٌ إِلاَّ وَهُوَ يَطُوفُ عَلَيْنَا جَمِيعًا ، فَيَدْنُو مِنْ
كُلِّ امْرَأَةٍ مِنْ غَيْرِ مَسِيسٍ ، حَتَّى يَبْلُغَ
إِلَى الَّتِى هُوَ يَوْمُهَا ، فَيَبِيتُ عِنْدَهَا
Manzon Allaah
(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya kasance ba ya fifita sashenmu a kan
sashe wajen rabon-kwana, a iya zamansa a cikinmu; kuma da ƙyar
wani yini guda ke wucewa face kuwa ya kewaya mu gaba-ɗaya, kuma ya kusanci kowace mace amma ba
tare da saduwa ba, har sai ya kai ga mai girki a ranar, sai ya kwana a wurinta.
(Abu-Daawud: 2137 ya riwaito shi).
Don haka
mazaje masu yin irin wannan zalunci ga matayensu ana ji masu tsoron faɗawa cikin irin wannan
mummunan hali, saboda Allah ba ya zalunci, kuma ya haramta a yi zalunci, don
haka mu ji tsoron Allah mu yi adalci a tsakanin iyalanmu. Allah ya shiryar da
mu hanya madaidaiciya.
WALLAHU
A'ALAM.
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Fb6qgYPXfEeHb8CD1SWAkK
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.