𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum. Malam shin ya halatta na sadu da ɗaya daga cikin matana ko da ba ranar kwananta ba ne?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam wa
rahmatullahi wa barakatuhu.
A'a bai halatta ba. Domin
hakika yin hakan yana daga cikin zalunci. Kuma Allah (SWT) ya wajabta yin
adalci ga duk wanda zai zauna da mata. Allah ya ce:
فَانْكِحُوا مَا طَابَ لَكُمْ مِنَ النِّسَاءِ مَثْنَىٰ وَثُلَاثَ وَرُبَاعَ ۖ فَإِنْ خِفْتُمْ أَلَّا تَعْدِلُوا فَوَاحِدَةً أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُكُمْ ۚ ذَٰلِكَ أَدْنَىٰ أَلَّا تَعُولُوا
Ku auri abin da ya yi muku daɗi
daga mata; biyu-biyu, da uku-uku, da huɗu-huɗu.
Sa'annan idan kun ji tsoron ba za ku yi adalci ba, to, (ku auri) guda ko kuwa
abin da hannayenku na dama suka mallaka (baiwa). Wannan shi ne mafi kusantar
zama ba ku wuce haddi ba. (Suratun-Nisa'i 3)
Wato wajibi ne ka raba
lokutanka a tsakanin matanka daidai da daidai. Kada ka sadu da wata daga
cikinsu sai aranar girkinta. Kuma wajibi ne ka basu abinci, sutura, muhalli,
bisa adalci gwargwadon damar da Allah ya huwace maka.
Haƙƙin miji ne kar ya sadu da
wata daga cikin matansa sai wacce ita ce ke da kwana, ko kuma idan akwai
amincewa da yarda daga wacce ta ke da kwanan. Yana iya shiga wurin matarsa da
ba ita ce mai girki ba da rana idan akwai larura, kamar bayar da kuɗin
cefane, ko binciken lafiyarta, ko warware wata matsala da makamatan haka. Bai
halatta ya sadu da wacce ba kwananta ko girkinta ba a lokacin da ya shiga
wurinta don wata buƙata
daga cikin buƙatun da ambatonsu ya
gabata. Haƙƙin mata ne kar ta
yarda mijinta ya sadu da ita idan dai ba kwananta ba ne, ko in ba da izinin
wadda ta ke da kwanan ba.
Idan har kasan ba za ka iya
yin adalci a tsakaninsu ba, to bai halatta ka Ƙara
auren ba. Domin hakika Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce:
"Wanda ya kasance yana da Mata biyu, sai ya karkata zuwa ga ɗayar
cikinsu, to zai zo aranar Alƙiyamah
alhali tsagin jikinsa ya karkace (wato ya shanye, yana tafiya a tazgade).
Tirmidhiy da Nisa'iy da Abu Dawud da Ibnu Maajah ne suka ruwaitoshi.
A’ishah Ummul-Mu’mineen (Radiyal
Laahu Anhaa) ta ce:
كَانَ رَسُولُ اللَّهِ - صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ - لاَ يُفَضِّلُ بَعْضَنَا عَلَى بَعْضٍ فِى الْقَسْمِ ، مِنْ مُكْثِهِ عِنْدَنَا ، وَكَانَ قَلَّ يَوْمٌ إِلاَّ وَهُوَ يَطُوفُ عَلَيْنَا جَمِيعًا ، فَيَدْنُو مِنْ كُلِّ امْرَأَةٍ مِنْ غَيْرِ مَسِيسٍ ، حَتَّى يَبْلُغَ إِلَى الَّتِى هُوَ يَوْمُهَا ، فَيَبِيتُ عِنْدَهَا
Manzon Allaah (Sallal Laahu
Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya kasance ba ya fifita sashenmu a kan sashe wajen
rabon-kwana, a iya zamansa a cikinmu; kuma da ƙyar
wani yini guda ke wucewa face kuwa ya kewaya mu gaba-ɗaya,
kuma ya kusanci kowace mace amma ba tare da saduwa ba, har sai ya kai ga mai
girki a ranar, sai ya kwana a wurinta. (Abu-Daawud: 2137 ya riwaito shi).
Don haka mazaje masu yin
irin wannan zalunci ga matayensu ana ji masu tsoron faɗawa
cikin mummunan hali, saboda Allah ba ya zalunci, kuma ya haramta a yi zalunci,
don haka mu ji tsoron Allah mu yi adalci a tsakanin iyalanmu. Allah ya shiryar
da mu hanya madaidaiciya.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Fb6qgYPXfEeHb8CD1SWAkK
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.