𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Malam, wanda ya
yi alwala zai je masallaci sai wata mace kirista ta taɓa shi, kamar a hanu ko a kafaɗarsa, to yaya hukuncin ya
ke?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul
Laah.
Da farko, wajibi ne musulmi ya
kare kansa daga duk abin da ka iya zubar masa da mutunci. Bai halatta ba
musulmi baligi mai hankali ya bari har wata macen da ba muharramarsa ba ta
shafi jikinsa hakan nan ba tare da wata larura ba, kuma ko ita musulma ce ko ba
musulma ba ce. Wanda ya fi tsanani kuma shi ne mace musulma baliga mai hankali
ta bari wani namijin da ba muharraminta ba ya shafi jikinta. Dalili kuwa shi ne
maganar Allaah Ubangijin Halittu cewa
وَلَا
تَقۡرَبُوا۟ ٱلزِّنَىٰۤۖ إِنَّهُۥ كَانَ فَـٰحِشَةࣰ وَسَاۤءَ سَبِیلࣰا
Kuma kar ku kusanci zina, haƙiƙa
ita alfasha ce kuma mummunar hanya ce. (Surah Al-Israa’: 32)
Kuma Manzon Allaah (Sallal Laahu
Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce
« كُتِبَ عَلَى ابْنِ آدَمَ نَصِيبُهُ مِنَ الزِّنَى مُدْرِكٌ ذَلِكَ لاَ مَحَالَةَ ، فَالْعَيْنَانِ زِنَاهُمَا
النَّظَرُ ، وَالأُذُنَانِ زِنَاهُمَا
الاِسْتِمَاعُ ، وَاللِّسَانُ زِنَاهُ
الْكَلاَمُ ، وَالْيَدُ زِنَاهَا
الْبَطْشُ ، وَالرِّجْلُ زِنَاهَا
الْخُطَا ، وَالْقَلْبُ يَهْوَى
وَيَتَمَنَّى ، وَيُصَدِّقُ ذَلِكَ
الْفَرْجُ وَيُكَذِّبُهُ »
An ƙaddara wa kowane ɗan Adam rabonsa na zina, kuma babu makawa
sai ya riske shi. Su dai idanu zinarsu ita ce: Kallo; kunnuwa kuma zinarsu ita
ce: Sauraro; harshe kuma zinarsa ita ce: Magana; hannu kuwa zinarsa ita ce:
Kamawa; ƙafa
kuwa zinarta ita ce: Takawa, kuma zuciya ita ke sha’awa kuma take buri. Farji kuma shi ke gaskata hakan ko
kuma ya ƙaryata
shi. (Sahih Muslim: 2657)
Bayar da sunan zina ga kamawa ko
shafa jikin wanda ko wadda ba ta halatta ba da hannu ya nuna shi zunubi ne,
kodayake ba babban kaba’irin zunubi ba ne. Allaah ya kiyaye.
Kuma Annabi (Sallal Laahu Alaihi
Wa Alihi Wa Sallam) ya ce
«لَأَنْ يُطْعَنَ فِي رَأْسِ رَجُلٍ بِمِخْيَطٍ مِنْ حَدِيدٍ ، خَيْرٌ لَهُ
مِنْ أَنْ يَمَسَّ امْرَأَةً لَا تَحِلُّ لَهُ»
A soka wa mutum allura ta baƙin ƙarfe
(misilla) a tsakiyar kansa, shi ya fiye masa alheri da a ce ya shafi jikin
macen da ba ta halatta gare shi ba. (Silsilah Sahihah: 226)
Allaah ya ƙara kiyaye mu.
Amma game da hukuncin alwalarsa a
bayan hakan ya auku, akwai mahanga guda biyu
1. Idan babu wani abu da ya fito
masa kamar maziyyi ko maniyyi a sakamakon hakan, to alwalarsa ba ta ɓaci ba. Domin hadisi ya
tabbata daga A’ishah Ummul-Mu’mineen (Radiyal Laahu Anhaa) cewa, Annabi (Sallal
Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)
كَانَ يُقَبِّلُ
بَعْضَ أَزْوَاجِهِ ، ثُمَّ يُصَلِّى
وَلاَ يَتَوَضَّأُ
Ya kasance yana sumbantar wata
daga cikin matan aurensa, sannan ya yi sallah ba tare da ya sake alwala ba.
(Sahih An-Nasaa’iy: 170; Sahih Ibn Maajah: 502).
Kuma abu ne sananne cewa, a
galibi sumba irin wannan tana tare da sha’awa ne.
2. Amma idan wani abu ya fito
masa a sakamakon shafan, to a nan ne malamai suka ce alwalarsa ta ɓaci, saboda dalilin abin
da ya fito amma ba domin shafar ba. A nan malamai sun kafa dalili ne da hadisin
Aliyu Bn Abi-Taalib (Radiyal Laahu Anhu) da ya ce: Na kasance mutum ne mai
yawan fitan maziyyi, sai na umurci wani mutum ya tambayi Annabi (Sallal Laahu
Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) a kan haka saboda matsayin ’yarsa a wurina. Sai ya ce
« تَوَضَّأْ وَاغْسِلْ ذَكَرَكَ »
Ka wanke al’aurarka, ka sake
alwala. (Sahih Al-Bukhaariy: 269; Sahih Muslim: 303)
Sannan kuma abin da ya inganta
daga Abdullaah Bn Abbaas (Radiyal Laahu Anhumaa) ya ce
الْمَنِيُّ وَالْوَدْيُ
وَالْمَذْيُ ، فَأَمَّا الْمَنِيُّ
فَفِيهِ الْغُسْلُ ، وَأَمَّا الْمَذْيُ
وَالْوَدْيُ فَفِيهِمَا الْوُضُوءُ ، وَيَغْسِلُ ذَكَرَهُ.
Maniyyi da wadiyyi da maziyyi ne.
Shi dai maniyyi shi ne wanda ake yin wanka saboda shi, su kuwa maziyyi da
wadiyyi sai ya wanke al’aurarsa ya sake alwala. (Ibn Abi-Shaibah: 989)
Amma maganar da waɗansu malamai suka yi
cewa, shafar mace yana karya alwala, saboda maganar Allaah Ta’aala cewa
أَوۡ
لَـٰمَسۡتُمُ ٱلنِّسَاۤء
Ko kuma idan kun yi shafar juna
da mata. (Surah Al-Maa’idah: 6)
Wannan ba daidai ba ne. Domin ma’anar
maganar a nan ita ce: Saduwar jima’i kawai. Haka Ibn Abi-Haatim ya riwaito ta
daga Ibn Abbaas (Radiyal Laahu Anhumaa) da wani isnadin da Al-Haafiz Ibn Hajr
(Rahimahul Laah) a cikin Fat-hul Baariy: 8/272 ya ce: Sahihi ne.
Sannan kuma a cikin (Fat-hul
Baariy: 8/158, 372) ya sake ambatowa sannan ya inganta riwayar da Abdurrazzaaq
ya kawo daga Ibn Abbaas (Radiyal Laahu Anhumaa) ɗin
dai cewa
إِنَّ اللهَ
حَيِّيٌ كَرِيمٌ يُكَنِّي عَمَّا شَاءَ ، الدُّخُولُ وَالتَّغَشِّي
وَالافْضَاءُ وَالْمُبَاشَرَةُ وَالرَّفَثُ وَاللَّمْسُ: الْجِمَاعُ
Haƙiƙa Allaah Mai Kunya ne Mai Karimci: Yana
yin kinaya a kan duk abin da ya so. Ad-Dukhuulu, da At-Taghasshiy, da Al-Ifdaa’u, da Al-Mubaasharah, da
Ar-Rafthu, da Al-Lamsu duk ma’anarsu
kenan: Saduwar Jima’i.
Haka nan kuma maganar Ubangiji
Ta’aala cewa
إِنَّمَا ٱلۡمُشۡرِكُونَ
نَجَسࣱ
Kaɗai
su mushirikai najasa ne kawai. (Surah At-Taubah: 28).
Wannan ma ba dalili ne a kan
cewa, idan kirista ya shafi jikin mutum to ya shafa masa najasa ne ba. Domin
ingantacciyar fassarar ayar a wurin malamai ita ce: Su najasa ce ta ma’ana
kawai saboda mummunar aƙidarsu, amma ba najasa ce ta haƙiƙa ba. Shiyasa ba a taɓa ji ko ganin inda Manzon
Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya yi umurni da a zuba ruwa a
wanke inda mushirikai ko Yahudawa suka zauna ko suka shafa a cikin masallacinsa
mai alfarma ba, irin yadda ya bayar da umurni da a zuba ruwa a kan fitsarin da
baƙauye
ya yi a masallacinsa. (Sahih Al-Bukhaariy: 219).
Allaah ya ƙara mana fahimta a
cikin addininmu.
HUKUNCIN SHAFAR MACE
GA WANDA YAKE DA ALWALA
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Idan namiji ya shafa
jikin mace ko ita mace ta shafa jikin namijij shin ko yin hakan yana iya karya
musu alwala? Muna neman karin bayani akan maganar da tafi inganci tare da
dalilansu:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Dangane da wannan
mas'ala ta hukuncin shafar mace ga wanda yake da alwala, an samu saɓani tsakanin Malamai
har maganganu kamar guda uku:
1. Ƙauli na farko shi ne,
ra'ayin da Imamush-Shafi'i ya tafi akansa cewa ta kowanne irin hali in dai
mutum ya shafa mace to kawai alwalarsa ta karye, shin ya shafe ta ne da nufin
jin daɗi ko a'a, shin ya
shafe ta ne da mantuwa ko da ganganci, sannan da ya yi shafar Shin ya samu jin
daɗi a dalilin hakan ko
kuma a'a, suka ce duk hukuncinsu ɗaya ne, kawai in dai har ya taɓa mace to wajibi ne
sai ya sake alwala.
Su dai Mazhabin Shafi'iyya sun kafa hujjarsu
ne da faɗin Aʟʟαн (ﷻ) inda Ya ke cewa:
"أوْلَا مَسْتُمُ النِّسَاءَ"
MA'ANA: Ko kuka shafi
mata (Suratul Nisa'i Aya ta 43).
Dan haka sai suka ce abin
da ake nufi da shafa anan shi ne shafar mace da hannu, domin idan aka ce
"Lamsu" to asalin ma'anarsa tana nufin shafa da hannu ne, kamar yadda
hakan ya zo a cikin Hadisai da yawa, kamar misalin faɗin Mαnzon Aʟʟαн (Sallallahu Alaihi
Wasallam) inda ya ce:
"واليد زناها اللمس" (رواه أحمد)
MA'ANA: Hannu zinarsa
ita ce yin shafa.
Koda yake dama dukkan
Malamai sun yarda cewa kalmar "Allamsu" ko kuma "Almassu"
idan aka faɗe ta haka a sake ba ƙaidi to ana nufin
dukkan wata shafa da ba jima'i ba, dan haka babu wata jayayya tsakanin Malamai
akan haka. Amma inda Malamai sukayi saɓani shi ne, "Allamsu" da Aʟʟαн (ﷻ) Ya faɗa a cikin waccan
"aya" shin me ake nufi da shi, jima'i ake nufi da shi ko kuma shafa
da hannu? Anan saɓanin yake.
2. Ƙauli na biyu shi ne,
ra'ayin da Mazhabin Hanafiyya suka tafi akansa na cewa shafar mace ta kowanne
irin hali ba ya karya alwala, wato su sun tafi ne akan akasin magana ta farko ke
nan, daga cikin dalilansu suka ce asali shafar mace baya karya alwala har sai
in an samu wani dalili ingantacce da ya ce shafar mace yana karya alwala, suka
ce kuma babu wani dalili ingantacce da ya nuna cewa shafar mace yana karya
alwala. Sannan suka ce akwai Hadisin Nana-A'isha wanda a cikinsa take cewa:
"كنت أنام بين يدي رسول الله (ﷺ) ورجلاي في قبلته، فإذا سجد غمزني فقبضت رجلاي، فإذا قام بسطتها" (رواه البخاري)
MA'ANA: Na kasance
ina barci a gaban Annαвι (Sallallahu Alaihi Wasallam) (ya yin da yake yin
sallar dare) kuma ƙafafu na suna (saitin) alƙiblar sa ne, dan haka
idan ya zo zai yi sujjada sai ya zungure ni (ya taɓa ni) ni kuma sai na
janye ƙafafuna, ya yin da na ji ya sake miƙewa tsaye sai na sake
shimfiɗasu (na miƙar da ƙafafuna).
Anan sai Malamai suka
ce muhallish-shahid ɗin da ke cikin wannan
Hadisi shi ne gashi dai Annαвι (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya na cikin sallah
amma ya taɓa jikin matarsa
A'isha kuma ya ci gaba da sallarsa ba tare da yana sake alwala ba.
Sannan akwai waɗansu Hadisan da dama
waɗanda a zahiri suke
nuna cewa Mαnzon Aʟʟαн (Sallallahu Alaihi
Wasallam) ya taɓa jikin mace, kuma da
a ce hakan yana ɓata alwala to da
Annαвι (Sallallahu Alaihi Wasallam) ba zai ci gaba da yin sallarba har sai ya
sake wata alwalar. Sai dai Shafi'iyya sun yi tawili akan ire-iren waɗannan Hadisan, inda suka
ce wataƙila Annαвι (Sallallahu Alaihi
Wasallam) yana taɓa saman tufafin
A'isha ne, to amma Malamai suka ce ko shakka babu cewa wannan tawili ne mai
rauni wanda ba zai iya zama karɓaɓɓe ba.
Sannan suka ce akwai
ruwayar Hadisin da ta ce Annαвι (Sallallahu alaihi Wasallam) Ya kan sumbaci (Kiss)
ɗaya daga cikin
matansa kuma ya fita zuwa masallaci a haka, duk da cewa akwai Malamai da yawa
da suka ce wannan Hadisi bai inganta ba, sannan akwai Malaman da suka ce ya
inganta, daga cikin wadanda suka ce ya inganta kuwa harda (Albaniy).
3. Ƙauli na uku shi ne,
ra'ayin da Mazhabin Malikiyya da kuma Hanabila suka tafi akansa cewa hukuncin
shafar mace yana buƙatar a yi masa tafsili (rarrabewa) akansa, dan haka suka
ce idan mutum ya shafa mace da nufin jin daɗi, to ko ya ji daɗin ko bai ji daɗin ba alwarsa ta
karye, haka nan idan ya yi shafa ba da nufin jin daɗi ba amma kuma sai ya
ji daɗin to shi ma alwalarsa
ta karye.
To amma magana mafi
inganci a cikin zantukan da Malamai sukayi ita ce ƙauli na biyu wanda
Mazhabin Hanafiyya suka tafi akansa cewa shafar mace ba ya karya alwala, domin
ko da a cikin waccan "aya" da Aʟʟαн (ﷻ) Ya faɗi "Allamsu" to ana nufin jima'i ne
bawai shafa da hannu ba, domin akwai "ayoyi" da yawa a cikin
Alkur'ani waɗanda idan Aʟʟαн (ﷻ) zai yi magana akan
jima'i ba ya fitowa fili ƙarara ya ambaci jima'i sai dai ya yi kinaya ya sakaya
sunan, shiyasa a wata ayar sai a ce "KU RUNGUMESU" a wata ayar kuma a
ce "IDAN KUKA SHAFESU" amma duk ana nufin jima'i ne.
Dan haka ke nan
dukkan wani wasa ko shafar juna da rungumar juna da ma'aurata za su yi a
tsakaninsu, to hakan ba zai karya musu alwalarsu ba, ko da kuwa sun yi hakanne
da nufin sha'awa kuma sukaji daɗi. Sai dai in wani abu ne ya fito daga gaban mutum a
dalilin hakan kamar maziyyi ko maniyyi, to anan alwala ta warware ne a sababin
fitar wancan ruwa ne bawai saboda shafar da a ka yi ba, idan kuma babu abin da
ya fito daga gaban mutum shi ke nan alwalarsa tana nan tsaf.
шαʟʟαнυ-тα'αʟα α'αʟαмυ
Mυѕтαρнα Uѕмαи
08032531505
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
WALLAHU A'ALAM
Sheikh Muhammad Abdullaah
Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.