𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mene ne
ingancin maganar da'ake cewa idan kana sallah iyayenka suka kiraka za ka katse
sallar ka amsa musu, dai-daine da in kana cikin banɗaki shima ka amsa musu?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد لله.
Idan Mutum
yana sallar farillah ba zai yanke sallar ba saboda kiran mahaifinsa ko
mahaifiyarsa, sai dai zai nusar da wanda yake kiransa cewa ya shagalta da
Sallah, ko dai ta hanyar tasbihi, ko daga sautin karatun sallar, da
makamantansu.
Yahalatta kuma
ya saukaka sallar tasa, idan yagama sallar sai ya Amsa kiran mahaifansa.
Bukhari ya
ruwaito hadisi (707) daka Abiy ƙatada
Allah yakara masa yarda daka Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya ce: ( Hakika
zantashi sallah inasan tsawaita ta, sai naji kukan kananun yara sai na sauƙaƙa sallar, dan tsaoran karna tsanantawa
mahaifiyar yaron).
Sauƙaƙa sallah saboda wani dalili da zai shagaltar
damai sallah ya halatta, idan sallar nafila ce idan kasan babanka ko babarka
ransa ko ranta ba zai ɓaci
ba danka karasa sallarka sannan ka Amsa musu, za ka cika sallarka, sannan sai
ka Amsa musu bayan kagama.
Amma idan
kasan iyayenka ransu zai ɓaci
idan ka ce sai ka gama sallah za ka Amsa musu, to sai ka yanke sallar ka Amsa
musu, sai ka sake sallah sabuwa. Wannan idan Sallar ta nafilace, ba farillah
ba. Babu komai Akanka. w
Bukhari (3436)
da Muslim (2550) Sun ruwaito hadisi lafazin na Muslim ne.
Daka Abu
huraira Allah yakara masa yarda daka Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya ce:(
Juraih yakasance yana bauta agurin ibadarsa, sai mahaifiyarsa tazo ta ce: Yakai
juraih nice mahaifiyarka kaimun magana, sai ta tarar da shi yana sallah, sai ya
ce: Ya Allah sallata zanci gaba ko mahaifiyata zan Amsawa, sai ya zaɓi cigaba da Sallarsa,
saita sake dawowa karo nabiyu ta ce: ya juraih nice mahaifiyarka kaimun magana,
sai ya ce: Ya Allah Sallata ko Mahaifiyata, sai ya zaɓi sallarsa saita ce: Ya Allah wannan juraih ɗanane nai masa magana
yaki Amsa mun, Ya Allah kada ka kasheshi harsai ka nuna masa jarabawa, Annabi
ya ce: datai masa addu'ar ya fitinu dasai ya fitinu arayuwarsa...).
Imamun Nawawi
yai Babi ya ce: Babin da zai magana akan gabatar da biyayyar iyaye akan sallar nafila dawaninta.
Nawawi Allah
yajikansa ya ce: " Malamai suka ce: Abunda yake dai-dai ahakkin juraih shi
ne ya Amsawa mahaifiyarsa, domin yana cikin Sallar nafilane, cigaba da yin
nafilar kuma ba wajibi ba ne, amsawa mahaifiyarsa dayi mata biyayya kuma dole
ne, saɓa mata haramun
ne kuma zai iya Sauƙaƙa sallar ya Amsa mata,
sannan yadawo yaci gaba da Sallar sa...
Duba Fat-hul
baary na Hafiz ibnu hajar, da Mausu'ah fiƙhiyyaj
(20/342) .
Yazo acikin durrul muktaar - littafin Hanafiyyah (2/54). " idan ɗaya daka cikin mahaifan mutum suka kirashi yana sallar farillah ba zai amsa ba, sai idan agaji suka nema daka gareshi."..
Shaik Usaimeen
ya ce: Baza ka amsawa ɗaya
daka cikin mahaifanka ba idan suka kiraka kana sallar farillah, koda kuwa
zasuyi fushi kaki amsa musu, sai dai idan akwai lalura kamar kaga wani koda ba
iyayenkaba zaifada halaka, kamar rijiya ko kogi, ko wuta ko wani hatsari da zai
iya faɗawa anan
wajibine kayanke sallah kowacce ce danka ceci rayuwarsa.
Sharhin
riyazul saliheena shafi na (302).
Dan haka
maganar ba haka take sakaka ba, Akwai ban-bancewar magana, idan ta nafilace za
ka yanke sallah ka amsawa iyayenka.
Idan
tafarillah ce baza ka Yanke ka Amsa musu ba.
Sannan magana
abanɗaki malamai sun
yi saɓani wasu suka
ce makaruhine.
Sahihiyar
magana idan uzuri kamar kiran iyaye ko wani uzuri daban za kai magana kana
cikin banɗaki.
WALLAHU
A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ƘARIN BAYANI
HUKUNCIN AMSA
KIRAN IYAYE YAYIN DA MUTUM YAKE CIKIN SALLAH
TAMBAYA:
Shin mutum yana iya yanke sallah
domin amsa kiran mahaifinsa ko mahaifiyarsa? Shin akwai bambanci tsakanin
sallar farilla da ta nafila a wannan yanayi? Kuma shin ya halatta a amsa musu
koda mutum yana cikin bandaki?
AMSA:
Malaman Musulunci sun yi dogon
bayani akan wannan maudu'i, inda suka rarrabe tsakanin yanayi daban-daban na
sallah:
1. Idan Ana Cikin Sallar Farilla
(Wajib): Mafi yawan malamai (ciki har da mazhabar Hanafiyya da wasu malaman
sauran mazhabobi) sun tafi akan cewa ba ya halatta mutum ya yanke sallar
farilla domin amsa kiran iyaye kawai, sai dai idan kiran na neman daukin
gaggawa ne (kamar sun fada cikin hadari, wuta, ko wani babban rashin lafiya).
• Abin da za ka yi: Idan suka
kira ka kana farilla, za ka iya kara sautin karatunka ko ka yi Tasbihi
(Subhanallah) domin su fahimci kana sallah. Idan kuma kiran ba na gaggawa ba
ne, sai ka saukaka sallar (ka gajarta ta) domin ka idar ka amsa musu.
2. Idan Ana Cikin Sallar Nafila:
Anan ne aka samu karin bayani dangane da hakkin iyaye. Idan mutum yana nafila:
• Idan ya san cewa iyayen ba za
su ji haushi ba idan ya karasa sallar, to ya karasa sannan ya amsa.
• Amma idan ya san cewa rashin
amsawa zai sanya su fushi ko radadin zuciya, to wajibi ne ya yanke nafilar ya
amsa musu. Domin biyayya ga iyaye farilla ce, yayin da ci gaba da nafila (bayan
an fara ta) matsayinta bai kai na biyayyar iyaye ba.
3. Magana a Bandaki (Toilet):
Asali ne cewa yin magana a bandaki ba tare da wani dalili ba makaruhi ne (abin
kyama). To sai dai, idan iyaye suka kira ka kana ciki, ko kuma wani abu na
gaggawa ya taso, ya halatta ka amsa musu da dan gajeren bayani (kamar kace:
"Ina ciki" ko "Ina zuwa") domin kada hankalinsu ya tashi ko
su yi fushi.
HUJJOJI DAGA HADISAN MANZON ALLAH
(SAW):
Tarihin Juraij ya kasance babban
darasi ga dukkan Musulmi game da fifikon kiran uwa akan sallar nafila:
النَّصُّ النَّبَوِيُّ: عَنْ أَبِي هُرَيْرَةَ
رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ، عَنِ النَّبِيِّ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ قَالَ:
"كَانَ جُرَيْجٌ يَتَعَبَّدُ فِي صَوْمَعَةٍ، فَجَاءَتْ أُمُّهُ... فَقَالَتْ:
يَا جُرَيْجُ، أَنَا أُمُّكَ كَلِّمْنِي، فَصَادَفَتْهُ يُصَلِّي، فَقَالَ: اللَّهُمَّ
أُمِّي وَصَلَاتِي؟ فَاخْتَارَ صَلَاتَهُ، فَرَجَعَتْ... ثُمَّ أَتَتْهُ الثَّانِيَةَ...
فَقَالَ: اللَّهُمَّ أُمِّي وَصَلَاتِي؟ فَاخْتَارَ صَلَاتَهُ، فَقَالَتْ: اللَّهُمَّ
إِنَّ هَذَا جُرَيْجٌ وَهُوَ ابْنِي وَإِنِّي كَلَّمْتُهُ فَأَبَى أَنْ يُكَلِّمَنِي،
اللَّهُمَّ فَلَا تُمِتْهُ حَتَّى تُرِيَهُ وُجُوهَ الْمُومِسَاتِ." (رواه البخاري
ومسلم)
FASSARAR HAUSA: An riwaya daga
Abu Hurairah (RA) daga Annabi (SAW) ya ce: "Juraij ya kasance yana bauta a
cikin dakin bautarsa, sai mahaifiyarsa ta zo... ta ce: 'Ya Juraij, ni ce
mahaifiyarka, yi mini magana.' Ta iske shi yana sallah, sai (a zuciyarsa) ya
ce: 'Ya Allah, mahaifiyata ko salla ta?' Sai ya zabi sallar sa. Ta dawo karo na
biyu... ya sake zaban sallar sa. Sai ta ce: 'Ya Allah, wannan Juraij dana ne,
na yi masa magana ya ki amsa mini. Ya Allah kada ka kashe shi har sai ya ga
fuskokin karuwai (ya fada cikin fitina).'"
Sharhi: Malaman hadisi (kamar
Imamun Nawawi) sun ce wannan hadisi hujja ce cewa da Juraij ya amsa wa
mahaifiyarsa da ya fi masa alheri, domin yana cikin nafila ne. Wannan ya sa
addu'ar mahaifiyarsa ta kama shi har sai da Allah ya tseratar da shi daga baya.
RA'AYIN MALAMAI (FIQHU):
Maganar Imamun Nawawi (RA):
"Malamai sun ce: Abin da
yake daidai a hakkin Juraij shi ne ya amsa wa mahaifiyarsa, domin ci gaba da
nafila ba wajibi ba ne, amma biyayya ga mahaifiya wajibi ne, kuma saba mata
haramun ne."
Maganar Sheikh Ibn Uthaymeen
(RA): Sheikh ya bayyana cewa a sallar farilla ba a amsawa, sai dai idan akwai
hadari ga rayuwa. Idan mutum ya ga makaho zai fada rijiya, ko ya ga wuta za ta
ci wani, wajibi ne ya yanke salla (ko ta farilla ce) domin ya ceci rai.
Kammalawa:
1. Sallar Farilla: Kada ka yanke,
amma saukaka ta ka idar da wuri ka amsa.
2. Sallar Nafila: Idan iyayenka suna da saurin
fushi ko kiran na da mahimmanci, yanke sallar ka amsa musu, sannan ka sake ta.
3. A Bandaki: Amsa kiran iyaye ya
halatta idan akwai bukatar hakan don kada su damu, koda kuwa kana cikin
bandaki.
WALLAHU A'ALAM
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.