𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalaamu
Alaikum Wa Rahmatul Laah. Miji yana iya bai wa matarsa tabbataccen izinin fita
zuwa duk inda ta san bai kauce wa ƙa’idar
shari’a ba ko wanda ba
zai ɓata masa rai
ba, watau ba sai koyaushe ta tambaye shi ba?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus
Salaam Wa Rahmatul Laahi Wa Barakaatuh.
Barin mata
suna fita kowane lokaci suna yawo a cikin gari bai dace da koyarwar sahihin
addini ba. A ƙa’idar
addini mace tana fita ne kawai idan akwai larura ko buƙatar fitan. Don haka,
abin ba ya rataya ne kawai ga amincewa ko rashin amincewar mijinta ko iyayenta
ba. Akwai haƙƙin Allaah ma a cikin abin.
Amma idan miji
ya bai wa matarsa tabbatacce ko kafaffen izini irin wannan kuma a bisa sharuɗɗan da aka ambata a
tambayar, ba za a ce ya yi ba daidai ba. Tun da dai wani daga cikin haƙƙoƙinsa
a kanta ne ya sauke ko ya kayar mata.
Sai dai kuma
ya kamata a fahimci cewa: Yin hakan ga wata mace ba abin murna da farin ciki ba
ne. Sharri ne a wurin masu fahimta da ladabi da biyayya. Domin mu ƙaddara
mahaifinta ne ya gaya mata hakan a lokacin tana zaune a tare da shi a gidansa
kafin aurenta, yaya za ta ɗauki
wannan maganar? Wannan bai nuna kamar rashin damuwa ko rashin kulawarsa da ita
ba?! Wannan bai nuna kamar ya ƙyale ta ne ta yi duk abin da take so
kawai ba?!
A wurin mata
masu kyakkyawar fahimta miji ya zama a duk lokacin da mace ta tambaye shi fita
unguwar da ta dace ya riƙa amincewa yana yarje mata, suna ganin wannan kamar alama ce
mai nuna ta fara fita a ransa! To, ina kuma ga wacce ya ce mata: Duk lokacin da
kika ga ya dace kawai ki fita zuwa duk inda kika ga ya dace?!
Sannan kuma
yaya miji yake ji idan misali matarsa ta tambaye shi zuwa Zariya ko Kano ko
Gusau, amma kuma sai ya ji ko ya ganta a Abuja? Tsakanin da Allaah! Yaya yake
ji? To ina kuma ga wacce kwata-kwata ba ta tambaye shi ba?! Sai dai kawai bugo
masa waya aka yi ana gaya masa cewa, an ga matarka a wurin biki a Abuja ko
Maiduguri ko Sakoto?! Don Allaah! A nan, ina ƙauna da kishin da aka san mazan musulmi
da shi?!
Wannan
tsantsar boko ne kawai, da koyi da ɗabi’u
da halayen maciya karnuka da aladu, marasa kishi! Amma ba musulunci ne ko
al’adarmu ba.
Lallai miji ya
tsoron ALLAH kada ya kasance daga cikin DAYYUS domin yazo cikin hadisin da
Nasa'i ya ruwaito cewa: Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce: “Mutane uku
ALLAH ba zai kalle su ba aranar alƙiyama,
DAYYUS yana daga ciki. DAYYUS shi ne Wanda baya kishi matarsa, baya kishin ɗiyarsa, baya kishin
kanwarsa, baya kishin ahakinsa.
Hakanan kuma
kada ya manta faɗin
Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam cewa: “Dukkanku MAKIYAYA ne, kuma tabbas!
za'a tambaye ku akan abunda aka baku KIWO.” [Bukhari da Muslim]
Miji na kwarai
jagorane ga alkhairi acikin iyalansa. Yana umurtasu da kyakykyawa yana kuma
hanasu mummuna, himmarsa shi ne ya tseratar da kanshi dama iyalan nasa daga
fushin Allah zuwa ga yardarsa. Kamar yadda Allah Madaukaki Ya fadi :
يَا أَيُّهَا
الَّذِينَ آمَنُوا قُوا أَنْفُسَكُمْ وَأَهْلِيكُمْ نَارًا وَقُودُهَا النَّاسُ وَالْحِجَارَةُ عَلَيْهَا مَلَائِكَةٌ غِلَاظٌ شِدَادٌ لَا يَعْصُونَ اللَّهَ مَا أَمَرَهُمْ وَيَفْعَلُونَ مَا يُؤْمَرُونَ ٦
Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku
kãre wa kanku (da iyãlinku daga wata wuta makãmashinta mutãne da duwãtsu ne. A
kanta akwai waɗansu
malã´iku mãsu kauri, mãsu ƙarfi. Bã su sãɓã wa Allah ga abin da Ya
umurce su, kuma sunã aikata abin da ake umunin su. [Suratu Tahrim : 6]
WALLAHU A'ALAM
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.