Ticker

6/recent/ticker-posts

Shin Miji Zai Iya Bawa Matarsa Iznin Fita A Koyaushe Ba Tare Da Ta Tambaye Shi Ba?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalaamu Alaikum Wa Rahmatul Laah. Miji yana iya bai wa matarsa tabbataccen izinin fita zuwa duk inda ta san bai kauce wa ƙaidar sharia ba ko wanda ba zai ɓata masa rai ba, watau ba sai koyaushe ta tambaye shi ba?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laahi Wa Barakaatuh.

Barin mata suna fita kowane lokaci suna yawo a cikin gari bai dace da koyarwar sahihin addini ba. A ƙaidar addini mace tana fita ne kawai idan akwai larura ko buƙatar fitan. Don haka, abin ba ya rataya ne kawai ga amincewa ko rashin amincewar mijinta ko iyayenta ba. Akwai haƙƙin Allaah ma a cikin abin.

Amma idan miji ya bai wa matarsa tabbatacce ko kafaffen izini irin wannan kuma a bisa sharuɗɗan da aka ambata a tambayar, ba za a ce ya yi ba daidai ba. Tun da dai wani daga cikin haƙƙoƙinsa a kanta ne ya sauke ko ya kayar mata.

Sai dai kuma ya kamata a fahimci cewa: Yin hakan ga wata mace ba abin murna da farin ciki ba ne. Sharri ne a wurin masu fahimta da ladabi da biyayya. Domin mu ƙaddara mahaifinta ne ya gaya mata hakan a lokacin tana zaune a tare da shi a gidansa kafin aurenta, yaya za ta ɗauki wannan maganar? Wannan bai nuna kamar rashin damuwa ko rashin kulawarsa da ita ba?! Wannan bai nuna kamar ya ƙyale ta ne ta yi duk abin da take so kawai ba?!

A wurin mata masu kyakkyawar fahimta miji ya zama a duk lokacin da mace ta tambaye shi fita unguwar da ta dace ya riƙa amincewa yana yarje mata, suna ganin wannan kamar alama ce mai nuna ta fara fita a ransa! To, ina kuma ga wacce ya ce mata: Duk lokacin da kika ga ya dace kawai ki fita zuwa duk inda kika ga ya dace?!

Sannan kuma yaya miji yake ji idan misali matarsa ta tambaye shi zuwa Zariya ko Kano ko Gusau, amma kuma sai ya ji ko ya ganta a Abuja? Tsakanin da Allaah! Yaya yake ji? To ina kuma ga wacce kwata-kwata ba ta tambaye shi ba?! Sai dai kawai bugo masa waya aka yi ana gaya masa cewa, an ga matarka a wurin biki a Abuja ko Maiduguri ko Sakoto?! Don Allaah! A nan, ina ƙauna da kishin da aka san mazan musulmi da shi?!

Wannan tsantsar boko ne kawai, da koyi da ɗabi’u da halayen maciya karnuka da aladu, marasa kishi! Amma ba musulunci ne ko al’adarmu ba.

Lallai miji ya tsoron ALLAH kada ya kasance daga cikin DAYYUS domin yazo cikin hadisin da Nasa'i ya ruwaito cewa: Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce: “Mutane uku ALLAH ba zai kalle su ba aranar alƙiyama, DAYYUS yana daga ciki. DAYYUS shi ne Wanda baya kishi matarsa, baya kishin ɗiyarsa, baya kishin kanwarsa, baya kishin ahakinsa.

Hakanan kuma kada ya manta faɗin Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam cewa: “Dukkanku MAKIYAYA ne, kuma tabbas! za'a tambaye ku akan abunda aka baku KIWO.” [Bukhari da Muslim]

Miji na kwarai jagorane ga alkhairi acikin iyalansa. Yana umurtasu da kyakykyawa yana kuma hanasu mummuna, himmarsa shi ne ya tseratar da kanshi dama iyalan nasa daga fushin Allah zuwa ga yardarsa. Kamar yadda Allah Madaukaki Ya fadi :

 يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا قُوا أَنْفُسَكُمْ وَأَهْلِيكُمْ نَارًا وَقُودُهَا النَّاسُ وَالْحِجَارَةُ عَلَيْهَا مَلَائِكَةٌ غِلَاظٌ شِدَادٌ لَا يَعْصُونَ اللَّهَ مَا أَمَرَهُمْ وَيَفْعَلُونَ مَا يُؤْمَرُونَ ٦۝

Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku kãre wa kanku (da iyãlinku daga wata wuta makãmashinta mutãne da duwãtsu ne. A kanta akwai waɗansu malã´iku mãsu kauri, mãsu ƙarfi. Bã su sãɓã wa Allah ga abin da Ya umurce su, kuma sunã aikata abin da ake umunin su. [Suratu Tahrim : 6]

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

ƘARIN BAYANI

SHIN MIJI ZAI IYA BA WA MATARSA IZININ FITA A KOWANE LOKACI BA TARE DA TA RIƘA TAMBAYARSA BA?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalaamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuh. Malam ina tambaya: shin ya halatta ga miji ya ba wa matarsa izini na dindindin cewa tana iya fita duk lokacin da take so zuwa wurin da ba ya saɓa wa shari’a, ba tare da sai ta riƙa tambayarsa a duk lokacin da za ta fita ba? Wato ya ce mata ta samu cikakken izini idan har fitan ba ta saɓa wa ƙa’idodin addini ba kuma ba za ta ɓata masa rai ba.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam wa Rahmatullahi wa Barakatuh.

A tsarin shari’ar Musulunci, mace mai aure tana ƙarƙashin kulawar mijinta a gidan aure, kuma daga cikin haƙƙoƙin mijin akwai a nemi izininsa kafin mace ta fita daga gida. Wannan yana daga cikin tsarin da Musulunci ya tanada domin kiyaye mutunci da tsari a rayuwar aure.

Manzon Allah ya nuna muhimmancin izinin miji wajen fitan mace, musamman ma a wani hadisi da ya shafi zuwa masallaci. Annabi ya ce:

« إِذَا اسْتَأْذَنَتِ امْرَأَةُ أَحَدِكُمْ إِلَى الْمَسْجِدِ فَلَا يَمْنَعْهَا »

Ma’ana:

Idan matar ɗayanku ta nemi izininsa domin ta je masallaci, to kada ya hana ta.”

(Sahih Al-Bukhari da Sahih Muslim)

Daga wannan hadisi malamai suka fahimci cewa tun da ma zuwa masallaci — wanda shi ne daga cikin wuraren da Allah Ya fi so — sai mace ta nemi izini daga mijinta, to sauran wuraren fita ma sun fi dacewa a nemi izininsa.

Sai dai idan miji ya ba wa matarsa izini na gaba ɗaya cewa tana iya fita zuwa wuraren da suka halatta ba tare da sai ta tambaye shi a kowane lokaci ba, malamai sun bayyana cewa hakan yana iya zama halal idan an yi shi cikin wasu sharuɗɗa. Domin haƙƙin da ake magana a kai haƙƙin mijin ne, kuma idan ya sauke ko ya sassauta shi, babu laifi a shari’a.

Amma duk da haka, abin da ya fi dacewa da kyakkyawar tarbiyya da tsarin Musulunci shi ne mace ta riƙa sanar da mijinta idan za ta fita, domin hakan yana ƙara tabbatar da amana, girmamawa, da kyakkyawar mu’amala tsakanin ma’aurata. Musulunci ya gina zamantakewar aure ne a kan mutunta juna da kiyaye hakkin juna.

Haka kuma miji yana da alhakin kula da iyalinsa da jagorantar su zuwa alheri. Annabi ya tunatar da wannan alhaki a cikin hadisi inda ya ce:

« كُلُّكُمْ رَاعٍ وَكُلُّكُمْ مَسْؤُولٌ عَنْ رَعِيَّتِهِ »

Ma’ana:

Dukkanku makiyaya ne, kuma dukkanku za a tambaye ku game da abin da aka ba ku kulawa.”

(Sahih Al-Bukhari da Sahih Muslim)

Saboda haka miji mai hankali yana kula da al’amuran gidansa da iyalinsa domin ya tabbatar da cewa suna tafiya a kan hanyar da ta dace.

Haka kuma Allah Ya umarci muminai su kula da kansu da iyalansu daga abin da zai jefa su cikin azaba. Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce:

يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا قُوا أَنْفُسَكُمْ وَأَهْلِيكُمْ نَارًا وَقُودُهَا النَّاسُ وَالْحِجَارَةُ

Ma’ana:

Ya ku waɗanda kuka yi imani! Ku kare kanku da iyalanku daga wuta wadda makamashinta mutane da duwatsu ne.”

(Surat At-Tahrim: 6)

Saboda haka, idan miji ya ba da irin wannan izini na gaba ɗaya ga matarsa, hakan ba lallai ba ne ya zama haram idan fitan tana cikin abin da shari’a ta halatta kuma ba ta kawo wata fitina ba. Amma abin da ya fi dacewa shi ne a riƙa samun sadarwa da izini a tsakanin ma’aurata domin kiyaye mutunci, girmamawa da zaman lafiya a cikin gidan aure.

Wallahu A’lam.

Zauren Fatawoyi Bisa Alƙur’ani Da Sunnah.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments