𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu
Alaikum. Hadisai sun yi bayanin a kan Istighfaarin Annabi (Sallal Laahu Alaihi
Wa Alihi Wa Sallam): Waɗansu
sun ce a kullum fiye da saba’in (70), waɗansu
kuma ɗari (100) suka
ce yana yi. To, ko mutum zai iya yin fiye da ɗari?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam
warahmatullahi Wabarkatuh
Abin da aka
rawaito Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam yana istigfari sau saba'in a rana
kamar yadda ya zo a hadisi kuma yana yin guda ɗari
hadisi ne sahihi
Abin da
malamai sukace shi ne idan mutum lissafawa zai yi, sai yayi koyi da sunnar
Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam yayi yadda Annabi yayi, amma idan mutum ba
lissafawa zai yiba ba'a iyakance masa adadin dazai yiba sai yayi sama da ɗari har dubu ko sama da
hakama abune budadde Ku nemi gafarar ubangijinku Ku nemi tsarinsa don haka
mutum zai iya yin adadi dayawa amma basai ya lissafaba saboda kada riya ta
shiga kuma gururi ya shiga cewa shi yakai wani.
Addini dai a
asali shi ne addinin Allaah wanda Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi
Wa Sallam) ya zo da shi, kuma ya koyar da shi ga Sahabbai (Radiyal Laahu
Anhum). A kan shi ya wajaba kowane musulmi ya tsaya babu ƙari
a kansa kuma babu ragi. Kuma shi ake koyarwa da karantarwa ga mutane ban da duk
abin da ba shi ba.
Amma bayan
tabbatar da haka da kuma yin aiki da hakan idan wani mutum shi ga kansa ya ga
yana da karsashi da sha’awa a kan wani aikin alkhairi, kamar yawaita nafilolin
sallah ko azumi ko tilawa ko zikiri da makamantansu, don haka sai ya ƙara
wa kansa fiye da yadda ya ke a cikin nassi, to babu laifi, in shaa’al Laah. Matuƙar
dai bai ci karo da wani hani da ya zo kai-tsaye a kan hakan ba, kuma wannan
aikin bai shagaltar ko ya sa aka tawaye wata farilla ba, kuma bai ɗauke shi muhimmin abin da
yake ƙoƙarin
shaharta shi da yayata shi a cikin jama’a,
kamar ta koyar da shi gare su ba, ta yadda daga baya zai zama kamar kishiya ga
koyarwar Sunnah ba.
Domin an samu
waɗansu daga cikin
malamai a da sun yi irin waɗannan
ayyukan ga kansu, kamar yadda wani daga cikinsu ya sauke Alqur’ani a cikin
ranaku uku ko biyu ko ɗaya.
Wani ma an ce a tsakanin Azahar da La’asar ya sauke, wani kuma a tsakanin
Maghriba da Isha’i. (Dubi: An-Nawawiy a cikin At-Tibyaan Fee Adaabi Hamalatil
Qur’aan, shafi: 59-60)
Bayan kuwa duk
mun san maganar Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) cewa:
« لَمْ يَفْقَهْ مَنْ قَرَأَ الْقُرْآنَ فِى أَقَلَّ مِنْ ثَلاَثٍ »
Duk wanda ya
karance Alqur’ani a ƙasa da kwanaki uku, to bai fahimce shi ba. (Sahih Ibn Maajah:
1458)
Haka kuma an
samu wanda yake yin sallah a cikin dare ba da lissafin adadin raka’o’inta ba.
Sai ya yi ta zubawa kawai, idan ya gaji ko idan Asubah ta yi sai ya yi raka’a
guda a matsayin Wutri. Duk kuwa da hadisai sahihai sun zo suna tabbatar da
cewa:
مَا كَانَ رَسُولُ اللَّهِ - صلى الله عليه وسلم - يَزِيدُ فِى رَمَضَانَ وَلاَ فِى غَيْرِهِ عَلَى إِحْدَى عَشْرَةَ رَكْعَةً
Ko a Ramadan
ko ba a Ramadan ba, Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ba ya ƙarawa
a kan raka’o’i goma sha-ɗaya. (Sahih Al-bukhaariy:
1147)
Wani daga
cikinsu kuma a kullum Azumin nafila yake yi, in ban da ranakun Idi.
(Al-Mustadrak: 3/353)
Duk kuwa da
hadisin da Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya faɗi cewa:
« أَحَبُّ الصَّلاَةِ إِلَى اللَّهِ صَلاَةُ دَاوُدَ - عَلَيْهِ السَّلاَمُ - وَأَحَبُّ الصِّيَامِ إِلَى اللَّهِ صِيَامُ دَاوُدَ ، وَكَانَ يَنَامُ
نِصْفَ اللَّيْلِ وَيَقُومُ ثُلُثَهُ وَيَنَامُ سُدُسَهُ ، وَيَصُومُ يَوْمًا
وَيُفْطِرُ يَوْمًا »
Mafi soyuwar
sallah a wurin Allaah ita ce sallar Annabi Daawud (Alaihis Salaam), kuma mafi
soyuwan azumi a wurin Allaah shi ne azumin Annabi Daawud (Alaihis Salaam). Ya
kasance yana yin barcin rabin (1/2) dare, kuma ya tsaya sallah na sulusin (1/3)
dare, kuma ya yi barcin sudusin (1/6) dare. Kuma yana yin azumin yini guda,
kuma ya ajiye azumin yini guda. (Sahih Al-Bukhaariy: 1976)
Duk waɗannan ayyuka ne na ɗaiɗaikun malamai a za munan da suka shuɗe, wanda kowannensu ya yi
ne ga kansa, amma ba tare da yin kira ga jama’a cewa a yi koyi da shi a cikinsu
ba.
Maƙalƙale
wa irin waɗannan
ayyukan na malamai, da koyar da su ga mabiya, da ƙoƙarin kafewa a kansu ban da Sunnah, shi ya
kai ga yaɗuwar
wurudodi na bidi’a da mabiya ɗariƙoƙi su
ke a kansu a yau. Kuma kowa yana ganin yadda suka fi fifita su a kan bin abin
da Sunnah Sahihiya ta koyar.
Don haka,
nasiha kyakkyawa ta gaskiya ga al’umma ita ce, maimakon nacewa da zaƙewa
da wuce wuri a kan irin waɗannan
zikirorin gara mutum ya tsare, kuma ya kafe kansa da jama’arsa a kan abin da
Sunnah Sahihiya ta koyar kawai. Ya kiyayi zaƙewa ko wuce-iyaka a cikin hakan.
Malamai sun
nuna cewa: Duk lokacin da Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya
koyar da wani aikin alkhairi a Sunnah, to akwai hanyoyi biyu da sheɗan yake bi don janye
mutane daga bin wannan Sunnar:
(i) Wanda sheɗan ya ga mai lalaci da
ragwanci ne, sai ya ja shi ga kasala da nauyin jiki wurin aikin, ta yadda zai
hana shi kai wa ga cika abin yadda ake so.
(ii) Wanda
kuma ya gan shi mai karsashi da ƙwazo ne sai ya zuga shi, ya ƙara
masa ƙaimi,
ta yadda zai riƙa ganin sai ya wuce inda Sunnah ta tsayar da shi.
Don haka, dole
kowannenmu ya riƙa taka-tsantsan, kuma ya yi hankali kar a shige cikin ƙullin
yaudara da makircin sheɗan.
A taƙaice
dai, kowane musulmi ya riƙa tuna wasiyyar Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa
Sallam) wadda ya riƙa yi wa sahabbansa kusan a kowace ranar Jumma’a da kuma farkon kowane
jawabinsa gare su, cewa:
« إِنَّ أَصْدَقَ الْحَدِيثِ كِتَابُ اللَّهِ ، وَأَحْسَنَ الْهَدْىِ
هَدْىُ مُحَمَّدٍ ، وَشَرَّ الأُمُورِ
مُحْدَثَاتُهَا ، وَكُلَّ مُحْدَثَةٍ
بِدْعَةٌ ، وَكُلَّ بِدْعَةٍ
ضَلاَلَةٌ ، وَكُلَّ ضَلاَلَةٍ
فِى النَّارِ »
Haƙiƙa,
mafi gaskiyar labari shi ne: Littafin Allaah, kuma mafi kyawun shiriya shi ne:
Shiriyar Annabi Muhammad (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam), kuma mafi
sharrin al’amura shi ne: Ƙirƙirarrunsu, kuma kowace ƙirƙira bidi’a ce, kuma kowace bidi’a ɓata
ce, kuma kowace ɓata
tana cikin wuta. (Sahih An-Nasaa’iy: 1578) Allaah Ta’aala ya tsare mu daga duk
aikin da ke kai wa shiga Wuta.
WALLAHU A'ALAM
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.