𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam
Alaikum Wa Rahmatul Laah. Ina hukuncin macen da take neman miji ya sake ta
saboda ƙanƙantar
al’aurarsa, shi kuma
ya ce wai sai ta mayar masa da rabin sadakinsa da rabin kayan lefe?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus
Salaam Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.
A cikin
littafan Fiqhu (kamar Tamaamul Minnah: 3/75-78), malamai sun tabbatar da cewa
akwai wasu cututtuka ko larurori da idan aka samu ɗaya daga cikin ma’aurata da su a bayan
auren, to an bai wa abokin zama zaɓin
neman a warware auren, idan dai ba shi abokin zaman ne ya yi haƙuri,
ya amince ba.
1. Wanda yake
da yankakken azzakari.
2. Wanda ba ya
iya saduwa kwata-kwata.
3. Wanda aka
yanke masa maraina.
4. Wanda
marainansa suka tsiyaye.
5. Wadda
gabanta ya toshe.
6. Wadda wani
nama ya toho a cikin gabanta.
7. Wadda
mafitsara da gabanta suka haɗe.
8. Wadda naman
da ke tsakanin mafitsara da gabanta ya kumbura.
9. Mace ko
namijin da aka gano yana da cuta, irin: Hauka ko kuturta da makamantansu.
10. Sai kuma
cuta irin na zamani, kamar HIV AIDS da Sikila da Hanta da Kansa da makamantansu
ko mafiyansu.
Idan a bayan
tarewa aka gano abokin zaman aure yana da ɗaya
daga cikin waɗannan
larurorin, to ya halatta ya nemi a warware auren a tsakaninsu. Kuma mijin ba
shi da haƙƙin
neman a mayar masa da sadakinsa matuƙar dai ya riga ya sadu da ita. Amma idan
waliyyinta ya yaudare shi ne, ya ɓoye
masa larurar to shi ne zai biya shi sadakin.
Amma ƙanƙantar
al’aura - kodayake
wasu sun ambace shi a cikin fassarar ‘Inneen’ - amma dai sahihiyar
fassararsa ita ce: Wanda ba ya iya saduwa da mace kwata-kwata. Domin malamai
irin su - As-Shaikh Ibn Al-Uthaimeen (Rahimahul Laah) - sun yarda cewa, har
wanda ke iya saduwar ko da sau guda a shekara ma ba za a ce masa ‘Inneen’ wanda
matarsa take da ikon neman a warware aurenta da shi ba. Don haka, ƙanƙantar
al’aura ba matsala ce
irin ta mutuwar al’aurar
ba, matuƙar
dai yana iya yin amfani da ita a wurin saduwa.
Sannan kuma
wannan matsalar ba ta daga cikin larurar da za a zargi miji ko maɗaurin aurensa da laifin ɓoye shi daga matarsa,
balle a neme shi da biyan sadaki. Tun da dai kafin ɗaura aure da tarewa babu yadda shi kansa
mijin zai san cewa al’aurarsa za ta dace ko ba za ta dace da matar da zai aura
ba.
Amma idan a
bayan tarewa mace ta gano cewa mijin bai yi mata yadda take so ba, to matakin
farko dai shi ne ta yi haƙuri kawai a cigaba da zama da shi a haka har zuwa shiganmu
cikin Aljannah. Saboda hadisin Annabi (Sallal Laahu Alalihi Wa Alihi Wa Sallam)
da ya ce:
الْمُخْتَلِعَاتُ هُنَّ الْمُنَافِقَاتُ
Mata masu
neman khul’i, su ne munafukai. (Sahih Al-Jaami’: 6681)
Idan kuma ba
za ta iya jurewa ba, to tana iya ɗaukar
matakin rabuwa da shi ta hanyar khul’i. Tun da dai shari’a ta halatta mata yin
hakan a lokacin da ta ƙyamaci ɗabi’a
ko halittar mijin, kuma ta ji tsoron afkawa a cikin saɓon Allaah ta dalilin rashin yin biyayya ga
mijin.
Al-Imaam
Al-Bukhaariy ya riwaito (lamba: 5276) daga Ibn Abbaas (Radiyal Laahu Anhumaa)
cewa:
Matar auren
Thaabit Bn Qaysin Bn Shummaasin ce ta zo wurin Annabi (Sallal Laahu Alalihi Wa
Alihi Wa Sallam) ta ce: Ya Manzon Allaah! Ba na sukan Thaabit a kan sakaci da
addini ko munana wata ɗabi’a,
amma dai ina tsoron kafirci ne a bayan Imani. Sai Manzon Allaah (Sallal Laahu
Alalihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:
« فَتَرُدِّينَ عَلَيْهِ حَدِيقَتَهُ »
To, za ki
mayar masa da lambunsa?
Ta ce: E. Sai
ta mayar masa.
Kuma sai ya
umurce shi da ya rabu da ita.
Sannan malamai
sun sha bamban a kan ko zai iya karɓar
fiye da sadakin da ya ba ta? Waɗansu
sun amince, saboda ayar Surah Al-Baqarah: 229 Musamman idan ya zama babu wani
cuta a fili da yake yi mata, kuma idan ya zama a halin da sadakin aure ya yi
tsada ne.
الطَّلَاقُ مَرَّتَانِ ۖ فَإِمْسَاكٌ بِمَعْرُوفٍ
أَوْ تَسْرِيحٌ بِإِحْسَانٍ ۗ وَلَا يَحِلُّ
لَكُمْ أَنْ تَأْخُذُوا مِمَّا آتَيْتُمُوهُنَّ شَيْئًا إِلَّا أَنْ يَخَافَا أَلَّا يُقِيمَا حُدُودَ اللَّهِ ۖ فَإِنْ خِفْتُمْ
أَلَّا يُقِيمَا حُدُودَ اللَّهِ فَلَا جُنَاحَ عَلَيْهِمَا فِيمَا افْتَدَتْ بِهِ ۗ تِلْكَ حُدُودُ
اللَّهِ فَلَا تَعْتَدُوهَا ۚ وَمَنْ يَتَعَدَّ
حُدُودَ اللَّهِ فَأُولَٰئِكَ هُمُ الظَّالِمُونَ ٩٢٢
Saki sau biyu
yake, sai a riƙa da alheri, ko kuwa a sallama bisa kyautatãwa. Kuma ba ya halatta a
gare ku (maza) ku karɓe
wani abu daga abin da kuka bã su, fãce fa idan su (ma´auran) na tsõron bã zã su
tsayar da iyãkõkin Allah ba. Idan kun (danginsu) ji tsõron bã zã su tsayar da
iyãkõkin Allah ba, to, bãbu laifi a kansu a cikin abin da ta yi fansa da shi.
Waɗancan iyãkõkin
Allah ne sabõda haka kada ku ketare su. Kuma wanda ya ƙetare iyãkõkin Allah, to waɗannan
su ne azzãlumai. (Surah Al-Baqarah: 229)
WALLAHU A'ALAM
Sheikh
Muhammad Abdullaah Assalafiy
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.