𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salamu
Alaikum, ’Yar makaranta ce, suna tare da saurayinta yau kusan shekaru uku, sai
kuma aka ce za a yi mata haɗi
da wani danginta. Mahaifiyarta ma ba ta amince ba. Bayan wannan sai kuma yayar
mahaifiyarta ta bugo waya cewa, ta yi mata miji, za ta turo shi su gaisa! Shi
ne take neman shawara: Idan ta amince, ba ta bi son-zuciya ba? Ba ta zalunci
saurayinta na-farko ba? Kuma ba ta zama maciyar-amana ba? Tana neman a taimake
ta da mafita.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah.
[1] Da farko
ya kamata iyaye su san cewa, ba a yi wa yarinya budurwa aure a addini sai da
amincewarta da yardarta, kuma da wanda take so. Dalilai a kan haka suna da
yawa, kamar wannan:
Abu-Sa’eed
(Radiyal Laahu Anhu) ya ce: Wani mutum ne ya zo wurin Manzon Allaah (Sallal
Laahu ’Alaihi wa Alihi wa Sallam) da wata ’yarsa, ya ce: Wannan ’yar tawa ta ƙi
yarda ta yi aure!
Sai Annabi
(Sallal Laahu ’Alaihi wa Alihi wa Sallam) ya ce: Ke kuwa ki bi maganar
mahaifinki mana!
Sai ita kuma
’yar ta ce: A’a! Har sai ka gaya mini: Menene haƙƙin miji a kan matarsa!
Ya ce: Haƙƙin
miji a kan matarsa: Ko da yana da ƙazzuwa a fatar jikinsa sai ita kuma matar
ta sa harshenta duk ta lashe shi, ko kuma ko da wata tsutsa ko jini yana
gangarowa daga cikin hancinsa, sai ita kuma ta sa harshenta ta lashe shi, to da
kuwa ba ta biya haƙƙinsa ba!
Da ta ji haka
sai ’yar ta ce: Na rantse da wanda ya aiko ka da gaskiya! Ba zan yi aure ba!
A nan ne sai
Manzon Allaah (Sallal Laahu ’Alaihi wa Alihi wa Sallam) ya ce:
لَا تُنْكِحُوهُنَّ إِلَّا بِإِذْنِهِنَّ
Kar ku aurar
da su sai da yardarsu.
(Ibn Abi-Shaibah: 17116 ya riwaito shi kuma
Hasan ne, in ji mai littafin Sahih Fiq-his-Sunnah: 3/71).
Wannan ya
nuna:
1. Ba dole ne
sai mace ta yi aure ba, matuƙar dai ta iya kare kanta daga alfasha.
2. Ba a yarda
iyaye su tilasta yarinya a kan yin aure ba.
3. Ba a aurar
da yarinya sai da yardarta.
Don haka, idan
aka samu iyaye ko wani maɗaurin
auren mace ya nemi takura mata a kan sai ta auri wanda ba shi take so ba, to
bai yi daidai ba. Ya saɓa
wa irin waɗannan
nassoshin na addini.
Matakin ɗauka a nan shi ne: Alƙalin
kotun musulunci mai adalci ya fitar mata da haƙƙinta, a lokacin da dukkan hanyoyin sulhu
suka gagara.
Amma kuma abu
ne mummuna a wurin jama’armu ’ya ta kai ƙaran mahifinta kotu a kan komai. Saboda a
al’ada - ba a addini
ba - an ɗauka wulaƙanci
da cin-mutunci mafi girma shi ne: Ka kai mutum ƙara kotu! Don har yana aukar da gaba tun
daga kakanni har zuwa ga iyaye da ’ya’ya da jikoki!
Shiyasa a nan,
dole ita mace ta yi taka-tsantsan a kan wannan al’amarin, don kar kilu ta jawo
bau!
[2] Sannan
dole ita ma yarinyar ta tambayi kanta: Shin wannan saurayin da suka yi shekaru
uku suna tare iyayenta sun san da shi? Ta kawo shi wurinsu a matsayin wanda za
ta aura? Iyayen sun amince kuma sun yarda da halayensa da ɗabi’unsa a matsayin miji
na-gari ga ’yarsu? Ko kuwa dai ita ce kaɗai
da wasu ƙawayenta
suka san wannan ƙullin soyayyar a tsakaninsu? Idan haka ne, to gaskiya ba za a
zargi iyaye ba, idan suka nemi su aurar da ita ga wanda suke ganin ya dace.
Tare da sanin cewa sai sun nemi izininta da yardarta kafin auren.
A kullum
shawarar da muke bayarwa ga samari da ’yan mata ita ce: Su daina gaggawar ƙulla
soyayya a tsakaninsu da juna ba tare da sani da amincewar iyayensu da manyansu
ba. Domin ko ba komai ai abin da babba ya hango daga zaune, yaro ko rimi ya hau
ba zai iya hango shi ba, kamar yadda ake cewa.
Kin mutunta
kanki da iyayenki a wurin kowa idan kika fara sanar da iyayenki kafin ki amince
da duk mai nemanki a lokacin da ya gabatar da kansa a wurinki. Sannan kuma a
kullum gara ki auri wanda ya fi sonki fiye da wanda kika fi sonsa, domin shi
zai fi yin haƙuri da juriya a kan wasu ’yan kura-kuranki da munanawarki gare shi fiye da wanda
kika fi so.
[3] A gaskiya!
In dai tun farko iyayenki ko maɗaura
aurenki ba su san maganar saurayinki a tsawon shekaru uku da kuke tare ba, to
kun yi kuskure, kun faɗa
a cikin laifi.
Don haka,
yanzu sai ki gaya musu halin da kike ciki. Idan kuma suka kafe a kan
matsayinsu, to ni ina ganin ki yi haƙuri ke kanki, sannan ki ba saurayinki haƙuri
shi ma, ki dawo ki bi maganar iyayenki, don a zauna lafiya.
Kuma shi kansa
saurayin naki ba zai ƙi yarda da hakan ba: Ba zai ce kin bi son-zuciya ba, kuma ba
ki zalunce shi ba, sannan ba ki zama maciyar-amana ba! Maƙukar
dai yana son ki da gaske ne. Tun da dai ya san ba za ki iya ɗaura auren kanki gare shi
da kanki ba tare da yardar iyayenki ba. Shi ma kansa ba zai iya aurenki ba da
yarda da amincewar iyayensa ba, in dai har shi ɗin
na-kirki ne da gaske.
Allaah ya
taimake mu gaba-ɗaya,
ya datar da mu ga abin da yake so kuma yake yarda da shi a cikin maganganu da
ayyuka.
WALLAHU A'ALAM
Sheikh
Muhammad Abdullaahi Assalafiy
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.