Ticker

6/recent/ticker-posts

Mijina Yana Ba Wa Kishiyata Ranar Girkina

TAMBAYA (42)

Aslm malan barka da warhaka, da fatan maln yana cikin koshin lafiya. Malam dan allah ina da tamba ya akwai abun da ya kullemin kai. dan allah ina son awar waremin. akan mijin mu ne ina da abokiyar zama.

Amman malm dan a ce yau girkina ne sai yadau lokacina yakai mata kokuma ya je gidan ta da janaba ya yi wanka a can kuma ya ce dan ya sadu da ita ba haramun ba ne sai ya ce mun nima in ina son hakan zai kwanta DA NI ni akullun ina ce mishi a haka ake haifar shege amman ayau na ce barinaji tabakin malam ko hakan kuskure ne

MIJINA YANA BA WA KISHIYATA RANAR GIRKINA

AMSA

Waalaikumus, Warahmatullahi, Wabarakatuhum

Tabbas ba haramun ba ne ba idan ya sadu da ita tunda ai matarsa ce ta sunnah, saidai kuma idan kun yi alƙawari dashi cewar za ku dinga raba kwana ita 1 kema 1 to anan ya saba alƙawarin kuma ya zamo munafuki domin kuwa saba alƙawari yana daya daga cikin suffofin munafukai kamar yanda Annabi SAW ya fada

(Sahih al-Bukhari 33, Sahih Muslim 59)

Batun a haka ake haifar shege kuma ai bai taso ba ma, domin kuwa shege shi ne wanda aka haifa ba ta alaƙar auratayya (auren sunnah) ba, kin ga kuwa ai ita kishiyar taki ai yar uwarki ce musulma kuma matarsa ce halak malak to me ya kawo batun shegantaka anan?

Idan har ranar girkinki ita ce ranar da zai kwana a gidanki to bai kamata ya dinga dan waken zagaye yana bullawa gidan abokiyar zaman ki ba harma yana ba ta aron lokacinki na kebantuwa, hakan yana nuna bazai iya adalci a tsakaninku ba

Idan kuma har bazai iya adalci din ba to bai kamata ma ya auri mace sama da 1 ba

Allah SWT ya ce:

 (وَإِنْ خِفْتُمْ أَلَّا تُقْسِطُوا فِي الْيَتَامَىٰ فَانكِحُوا مَا طَابَ لَكُم مِّنَ النِّسَاءِ مَثْنَىٰ وَثُلَاثَ وَرُبَاعَ ۖ فَإِنْ خِفْتُمْ أَلَّا تَعْدِلُوا فَوَاحِدَةً أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُكُمْ ۚ ذَٰلِكَ أَدْنَىٰ أَلَّا تَعُولُوا )

النساء (3) An-Nisaa

Kuma idan kun ji tsoron ba za ku yi adalci ba a cikin marayu, to, (akwai yadda za a yi) ku auri abin da ya yi muku daɗi daga mata; biyu-biyu, da uku-uku, da huɗu-huɗu. Sa'an nan idan kun ji tsoron ba za ku yi adalci ba, to, (ku auri) guda ko kuwa abin da hannayenku na dama suka mallaka. Wannan shi ne mafi kusantar zama ba ku wuce haddi ba

Shawara anan ita ce: Ki bashi shawara a ilimance cewar abin da yake baya kyautawa a addinance, domin kuwa duk wanda baya adalci tsakanin iyalansa to a ranar lahira zai tashi ne tsagin jikinsa a shanye (paralyzed) kamar yanda hadisin ya tabbatar

 (Sahih Muslim)

 Amsawa:

Usman Danliti Mato (Usmannoor_As-salafy)

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu. . .

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp. com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www. facebook. com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t. me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments