TAMBAYA (42)❓
Aslm malan barka da warhaka, da fatan maln yana cikin koshin lafiya. Malam dan allah ina da tamba ya akwai abun da ya kullemin kai. dan allah ina son awar waremin. akan mijin mu ne ina da abokiyar zama.
Amman malm dan a ce yau
girkina ne sai yadau lokacina yakai mata kokuma ya je gidan ta da janaba ya yi wanka
a can kuma ya ce dan ya sadu da ita ba haramun ba ne sai ya ce mun nima in ina
son hakan zai kwanta DA NI ni akullun ina ce mishi a haka ake haifar shege
amman ayau na ce barinaji tabakin malam ko hakan kuskure ne
MIJINA YANA BA WA KISHIYATA
RANAR GIRKINA
AMSA❗
Waalaikumus, Warahmatullahi,
Wabarakatuhum
Tabbas ba haramun ba ne ba
idan ya sadu da ita tunda ai matarsa ce ta sunnah, saidai kuma idan kun yi alƙawari dashi cewar za ku dinga raba kwana
ita 1 kema 1 to anan ya saba alƙawarin
kuma ya zamo munafuki domin kuwa saba alƙawari
yana daya daga cikin suffofin munafukai kamar yanda Annabi SAW ya fada
(Sahih al-Bukhari 33, Sahih
Muslim 59)
Batun a haka ake haifar
shege kuma ai bai taso ba ma, domin kuwa shege shi ne wanda aka haifa ba ta alaƙar auratayya (auren sunnah) ba, kin ga
kuwa ai ita kishiyar taki ai yar uwarki ce musulma kuma matarsa ce halak malak
to me ya kawo batun shegantaka anan?
Idan har ranar girkinki ita
ce ranar da zai kwana a gidanki to bai kamata ya dinga dan waken zagaye yana
bullawa gidan abokiyar zaman ki ba harma yana ba ta aron lokacinki na
kebantuwa, hakan yana nuna bazai iya adalci a tsakaninku ba
Idan kuma har bazai iya
adalci din ba to bai kamata ma ya auri mace sama da 1 ba
Allah SWT ya ce:
(وَإِنْ خِفْتُمْ أَلَّا تُقْسِطُوا فِي الْيَتَامَىٰ فَانكِحُوا مَا طَابَ لَكُم مِّنَ النِّسَاءِ مَثْنَىٰ وَثُلَاثَ وَرُبَاعَ ۖ فَإِنْ خِفْتُمْ أَلَّا تَعْدِلُوا فَوَاحِدَةً أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُكُمْ ۚ ذَٰلِكَ أَدْنَىٰ أَلَّا تَعُولُوا )
النساء (3)
An-Nisaa
Kuma idan kun ji tsoron ba za
ku yi adalci ba a cikin marayu, to, (akwai yadda za a yi) ku auri abin da ya yi
muku daɗi
daga mata; biyu-biyu, da uku-uku, da huɗu-huɗu.
Sa'an nan idan kun ji tsoron ba za ku yi adalci ba, to, (ku auri) guda ko kuwa
abin da hannayenku na dama suka mallaka. Wannan shi ne mafi kusantar zama ba ku
wuce haddi ba
Shawara anan ita ce: Ki
bashi shawara a ilimance cewar abin da yake baya kyautawa a addinance, domin
kuwa duk wanda baya adalci tsakanin iyalansa to a ranar lahira zai tashi ne
tsagin jikinsa a shanye (paralyzed) kamar yanda hadisin ya tabbatar
(Sahih Muslim)
Amsawa:
✍Usman Danliti Mato (Usmannoor_As-salafy)
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu. . .
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp. com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www. facebook. com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t. me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.