TAMBAYA (48)❓
Assalamualaikum.
Dan Allah memene ma'anar sunan (Haniya and nasreen). Ngd
AMSA❗
Waalaikumussalam
warahmatullahi taala wabarakatuhum
Alhamdulillah
Nasreen suna
ne na larabci wanda yana nufin fulawa (wild rose) mai kamshi musamman koriya
kokuma ja hawur, anfi samunta a yankin kasar Pakistan
Shi kuma sunan
Haniya asalinsa sunan larabci ne wanda yake nufin wajen da mutum zai samu farin
ciki da annashuwa, wasu suka ce a cikin wannan duniyar tamu wadda batada
tabbas, radawa jaririya sunan Haniya ko kuma Chanya a yaren Hebrew yana daya
daga cikin kyauta ta musamman a gareta wanda a yaren Hebrew ke nufin yardar
Allah
Sunan Haniya
ya fito (ba kai tsaye ba) a cikin Ƙur'ani:
Tur ayata 19 dakuma Al-Haƙƙa
ayata 24
Akwai wadanda
na san sunansu dayawa ya bisu, wani za kaji ana kiranshi da shaidan kuma za kaga
yanata shaidanci ya fitini al'umma, wani kuma rasta za kaga yana shaye-shaye
kala-kala wani kuma pastor ma naji yara suna kiransa kuma gaba daya baya maida
hankali wajen aiwatarda ibada ga addininsa (shiriyarsa shi ne fatanmu)
Haka kuma
akwai wani sanannen labarin wata mata da mijinta ya sakawa jaririnta suna
Muhammad matar ta ce ita bata son sunan, ta ce ita sai dai ta rinka kiransa da
sunan babanta marigayi, haka akai, amman Allah da ya tashi nuna ikonSa, silar
hakan sai yazamana duk sanda za'ayi wani taro a danginsu sai aga ta tashi tana
ta tiƙar rawa a
gaban iyaye ba kunya alhalin da can kuma mai kunyace, sai Allah ya cire kunyar
saboda illar canza sunan mai sunan
Abu Dawud ya
ce: Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya canza sunayen Al-'As, 'Azeez,
Atalah, Shaitan, Alhakam, Ghurab, Hubab, da Shihab wanda ya maida shi Hisham.
Ya canza sunan Harb (Yaki) zuwa Salam (Aminci). Ya maida Almudtaji' (Wanda yake
kwantawa) zuwaga Munba'ith (Wanda yake tashi)
Ya maida sunan
garin 'Afira (Kasar da bata karbar shuka) zuwaga Khadirah (Koriyar kasa ma'ana
mai karbar shuka), ya canza sunan dutsen Shi'b Ad-dalala (Hanyar dutsen
kuskure) zuwaga Shi'b Al-huda (Hanyar dutsen shiriya), ya canza sunan al'ummar
Banu Az-zinya (Yayan zina) zuwaga Banu Ar-rishda (Yayan shiryayyu), haka kuma
ya canza sunan al'ummar Banu Mughwiyah (Yayan matar da ta yi nisa wajen aikata
sabo) zuwaga Banu Rishdah (Yayan shiryayyiyar mata)"
Sannan kuma
yana daga cikin dabi'ar Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) cewar baya
son wucewa ta wajen da aka radawa suna mara kyau kamar wani lokaci da yazo
wucewa ta tsakanin wasu manyan dutsuna sai ya tambayi sunayensu sai aka ce masa
Fadhih (Danasani) dakuma Mukhzin (Rashin kunya), sai ya dawo ya fasa bi ta
hanyar duwatsun
(A duba
littafin Zaadil Ma'ad wallafar Ibn al-Ƙayyim)
Yakamata duk
musulmi idan zai rada sunan yar da aka haifa masa ko da, ya yi koyi da addini
don ganin ya radawa abinda aka haifa masa sunan da yake tattare da alkhairi a
tarihance musamman ma sunayen yayan Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) dakuma
sunayen annabawa da manzanni dakuma sahabbai guda 10 wadanda aka yiwa bushara
da gidan Aljannah tun anan duniyar
Hakama a
bangaren yaya mata ayi koyi da wadanda suka bawa musulunci gudunmawa kamar
mahaifiyar muminai, Nana Aisha RA da yayan Annabi (Sallallahu alaihi wasallam)
kamar Nana Fatima RA. Da kuma sunayen sahabbai 10 da akai musu bushara da gidan
Aljannah irinsu Abubakar, Umar, Usman, Aliyu (Allah ya kara musu yarda baki
daya), da sauransu
Ya Allah ka
bamu zuri'a dayyiba wadda zamu sakawa suna mai ma'ana
Wallahu ta'ala
a'alam
Amsawa;
Usman Danliti
Mato (Usmannoor_As-salafy)
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.