Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Wanda Ya Manta Sujjadal Kabliyyah

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As-Salaam Alaikum. Idan Sujudul Ƙabliyyah ta samu mutum, kuma ya manta bai yi ba har sai da ya yi sallama, yaya zai yi?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Ramatul Laah:

Asali dai idan mutum ya yi ƙari a cikin sallah Sujada Baadiyyah yake yi. Idan kuma ragi ne ya yi, ko ragi da ƙari a haɗe sai ya yi Sujada Ƙabaliyyah.

Sannan idan mutum ya manta da Sujadar Ba’adiyyah malamai sun yarda cewa, lallai ya yi ta a duk lokacin da ya tuna. Haka ma Ƙabaliyyah da ya manta bai yi ba sai a bayan sallama ya tuna, malamai sun yarda ya yi ta a bayan sallamar, ta zama Ba’adiyyah kenan.

Ko ba komai dai, akwai malaman da suka yarda da halaccin yin kowanne daga cikin Sujadar ko Ƙabaliyyah ko Ba’adiyyahi a kan kowace irin Rafkanuwa:

Al-Haafiz Ibn Hajr ya ce:

وَرَجَّحَ الْبَيْهَقِيُّ طَرِيقَةَ التَّخْيِيرِ فِي سُجُودِ السَّهْوِ قَبْلَ السَّلَامِ أَوْ بَعْدَهُ وَنَقَلَ الْمَاوَرْدِيُّ وَغَيْرُهُ الْإِجْمَاعَ عَلَى الْجَوَازِ وَإِنَّمَا الْخِلَافُ فِي الْأَفْضَلِ وَكَذَا أَطْلَقَ النَّوَوِيُّ.

Al-Baihaƙiy ya rinjayar da hanyar zaɓi a cikin Sujudar Rafkanuwa kafin sallama ko a bayan sallama. Kuma Al-Maawardiy da waninsa daga cikin malamai sun ciro ijma’in malamai a kan halaccin hakan. Sun yi saɓani ne kawai a kan wanda ya fi. Haka kuma shi ma An-Nawawiy ya faɗi maganar a sake. (Fat-hul Baariy: 3/94).

Shi kuma An-Nawawiy ya ce:

قَالَ الْقَاضِي عِيَاضٌ رَحِمَهُ اللَّهُ تَعَالَى وَجَمَاعَةٌ مِنْ أَصْحَابِنَا: وَلَا خِلَافَ بَيْنَ هَؤُلَاءِ الْمُخْتَلِفِينَ وَغَيْرِهِمْ مِنَ الْعُلَمَاءِ أَنَّهُ لَوْ سَجَدَ قَبْلَ السَّلَامِ أَوْ بَعْدَهُ لِلزِّيَادَةِ أَوِ النَّقْصِ أَنَّهُ يُجْزِئُهُ وَلَا تَفْسُدُ صَلَاتُهُ وَإِنَّمَا اخْتِلَافُهُمْ فِي الْأَفْضَلِ، وَاللَّهُ أَعْلَمُ .

Al-Ƙaadiy Iyaadh (Rahimahul Laah) da waɗansu daga cikin malaman mazhabarmu sun ce: Babu saɓani a tsakanin waɗannan malaman da suka saɓa wa juna da waɗansunsu cewa, ya wadaci mutum idan ya yi sujada kafin ko a bayan sallama domin ƙari ko ragi, kuma sallarsa ba ta ɓaci ba. Saɓaninsu dai kawai a kan wanda ya fi ne. (Sharhun Nawawiy: 5/56-57).

WALLAHU A'ALAM

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments