Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Wanda Ya Manta Sujjadal Kabliyyah Ko Ba'adiyya

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As-Salaam Alaikum. Idan Sujudul Ƙabliyyah ta samu mutum, kuma ya manta bai yi ba har sai da ya yi sallama, yaya zai yi?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Ramatul Laah:

Asali dai idan mutum ya yi ƙari a cikin sallah Sujada Baadiyyah yake yi. Idan kuma ragi ne ya yi, ko ragi da ƙari a haɗe sai ya yi Sujada Ƙabaliyyah.

Sannan idan mutum ya manta da Sujadar Ba’adiyyah malamai sun yarda cewa, lallai ya yi ta a duk lokacin da ya tuna. Haka ma Ƙabaliyyah da ya manta bai yi ba sai a bayan sallama ya tuna, malamai sun yarda ya yi ta a bayan sallamar, ta zama Ba’adiyyah kenan.

Ko ba komai dai, akwai malaman da suka yarda da halaccin yin kowanne daga cikin Sujadar ko Ƙabaliyyah ko Ba’adiyyahi a kan kowace irin Rafkanuwa:

Al-Haafiz Ibn Hajr ya ce:

وَرَجَّحَ الْبَيْهَقِيُّ طَرِيقَةَ التَّخْيِيرِ فِي سُجُودِ السَّهْوِ قَبْلَ السَّلَامِ أَوْ بَعْدَهُ وَنَقَلَ الْمَاوَرْدِيُّ وَغَيْرُهُ الْإِجْمَاعَ عَلَى الْجَوَازِ وَإِنَّمَا الْخِلَافُ فِي الْأَفْضَلِ وَكَذَا أَطْلَقَ النَّوَوِيُّ.

Al-Baihaƙiy ya rinjayar da hanyar zaɓi a cikin Sujudar Rafkanuwa kafin sallama ko a bayan sallama. Kuma Al-Maawardiy da waninsa daga cikin malamai sun ciro ijma’in malamai a kan halaccin hakan. Sun yi saɓani ne kawai a kan wanda ya fi. Haka kuma shi ma An-Nawawiy ya faɗi maganar a sake. (Fat-hul Baariy: 3/94).

Shi kuma An-Nawawiy ya ce:

قَالَ الْقَاضِي عِيَاضٌ رَحِمَهُ اللَّهُ تَعَالَى وَجَمَاعَةٌ مِنْ أَصْحَابِنَا: وَلَا خِلَافَ بَيْنَ هَؤُلَاءِ الْمُخْتَلِفِينَ وَغَيْرِهِمْ مِنَ الْعُلَمَاءِ أَنَّهُ لَوْ سَجَدَ قَبْلَ السَّلَامِ أَوْ بَعْدَهُ لِلزِّيَادَةِ أَوِ النَّقْصِ أَنَّهُ يُجْزِئُهُ وَلَا تَفْسُدُ صَلَاتُهُ وَإِنَّمَا اخْتِلَافُهُمْ فِي الْأَفْضَلِ، وَاللَّهُ أَعْلَمُ .

Al-Ƙaadiy Iyaadh (Rahimahul Laah) da waɗansu daga cikin malaman mazhabarmu sun ce: Babu saɓani a tsakanin waɗannan malaman da suka saɓa wa juna da waɗansunsu cewa, ya wadaci mutum idan ya yi sujada kafin ko a bayan sallama domin ƙari ko ragi, kuma sallarsa ba ta ɓaci ba. Saɓaninsu dai kawai a kan wanda ya fi ne. (Sharhun Nawawiy: 5/56-57).

HUKUNCIN WANDA YA MANTA DA SUJJADA KABLI KO BA'ADI

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum Tambayata ita ce shin mene ne hukuncin wanda ya mance sujada kabli ko ba'adi yayin da ta kama shi?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salam Warahmatullahi Wabarkatuhu.

Imam Mardaawi (Rahimahullah) ya ce a cikin Al-musannaf (2/154) na Ibn Ƙudamah: A rankon sajadar mantuwa Akwai sharadi guda biyu.

1. Ya kasance cikin masallaci.

2. Ya kasance aikin baiyi tsawo ba. Ma'ana ba a samu tazarar lokacin yin mantuwar da tinawa ba.

Wannan shi ne ra'ayi mai kyau kamar yadda Al-Mardaawi yace. Imam Ahmad (rahimahullah) yace; Zai yi sajadar ne idan ya tina anan kusa. Koda kuwa ya fita daga masallacin ne. Kuma ya ce zai yi sajadar koda bayan lokaci mai tsawo ne ya tina, ko kuma ya yi magana, ko kuma har bayan ya fita masallaci ne. Wannan shi ne ra'ayin da Shaykhul Islam Ibn Taymiyyah ya zaba.

Al-Ikhtiyaaraat al-Fiƙhiyyah, Shafi na 94).

Idan mutum ya manta sujudar mantuwa wacce zai yi kafin sallama (Sajadar Ƙabli ke nan), har ya sallame bai tina ba, toh zai yi sujudar ƙablin ne anan take kuma wajibi ne yinta (idan ya tina anan kusa).

Amma idan kuma ya sallame kuma Bai tina ba har sai bayan an ɗauki lokaci mai tsawo, ko ya fita daga masallaci, ko alwalarsa ta warware. Toh anan babu bukatar yin sajadar mantuwa, kuma sallasa ta inganta. Al-Rawd al-Murabba’ Sharh Zaadal Mustaƙna’ (2/461)

MISALI: Idan mutum ya manta tahiyar farko, anan sajadar ƙabli ta kamashi, toh sai ya manta ya sallame batareda ya yi ƙabli ba, toh zai yi ƙablin ne idan ya tina nan take.

Amma idan bai tina ba anan kusa har sai bayan wani lokaci mai tsawo ko ya fita masallaci, toh anan bazai yi sajadar ƙablin ba kuma sallarsa tayi.

Shaykhul Islam Ibn Taymiyyah ya ce zai yi sajadar ne idan ya tina, koda ya tina ne bayan lokacin mai tsawo. Saboda hakan zai zama cikon abin da ya bari ne a sallarsa.

Amma Ra'ayin da ya fi kyau shi ne ra'ayin Mawallafin (rahimahullah) Wanda shi ne idan bai tina ba sai bayan lokaci mai tsawo, toh bazai rama sajadar ba kuma sallarsa tayi. Idan kuma ya tina anan kusa zai yi sajadar. 

WALLAHU A'ALAM

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments