Ticker

6/recent/ticker-posts

Daukar Kayan Miji Ba Tare Da Izininsa Ba

TAMBAYA (43)

Assalamu alaikum malam barka da safiya dafatan antashi lfy, Allah yakara basira ameen. Malam tambayata a nan ita ce. Malam macece tai aure akauye alhali aburni aka haifeta harta isa aure sai tai aure akauye to malam garin bawani na gartaccen ilimi saiyaranta da suka haifa aka kaisu wajen iyayenta dan samun ilimi, malam mijin yaka sance marowacine kuma yanada halinshi daidai gwargwado maaikacine kuma manomi, baitaba siyen ko da sabuluba yaba iyayen matarshi maruka yayanshi saidai su sukagabaya siya konayaran sai sukace yadunga saima yaranshi ana masu wanki, to malam yahalatta matarshi idan zataje gida tadan kwana2 ta dibi abincinshi tatai da shi sudunga ci saboda iyayenta bahali garesuba intaje hannu biyu ga yaya haka zaaita wahalar neman abunci, shikuma idan zataje ba zaice ga ko kudin siyen kokoba haka zatatai da yaya hudu ko da za suyi sati, yahalatta tadibi danyen abinci tatafi da shi bai saniba dan inya sani ba zai bariba kuma ta ce tana barar addua Allah yashirya mata mijinta dan baya cikin na gari baya aikata zina baya shaye shaye amman halayensa basuda kyau mungode malam Allah yashirya zuria

AMSA

Waalaikumus, Warahmatullahi, Wabarakatuhum

Ma'aikaci kuma manomin a takaicedai Allah ya albarkacesa da rufin asiri amman jahilci ya kewayeshi, mafita a nan shi ne a bullo masa ta bangaren da yake da naƙasu wato ilimi

Kuskuren ta daya anan, me ya sa ta kai yayan nasa batareda izinin mijinba, a nan ta yi gaban kanta ke nan ta maida kanta jagora alhalin shi ne jagoran gidan wanda za ta iya yiwuwa silar hakan ya janye hannayensa daga ciyar da su da shayar dasu da tufatarwa. Kallon mai kudi amman jahili da dangi suke masa kadai isa ya sa shaidan ya yi nasarar da zaisa ya zare hannayensa daga lamuran yayannasa

Dukkansu sun yi kuskure. Ta hanyar da aka bi tanan yakamata a sauko

A shawarce kamata ya yi ta tambayeshi dalilin da ya sa baya taimakawa yayan nasu idan ya ce meyasa kuka daukesu batareda izinina ba to sai a bashi haƙuri wanda in sha Allahu silar hakan zai dinga taimaka musu

Idan kuma ya nuna cewar shi haka nan bashida ra'ayin taimaka musu to sai samu waliyyinki a sanardashi abin da ke faruwa

Rashin maida al'amarin matsalar aure ga waliyyai shi ne babban abin da yake kawo matsala ga al'ummar wannan zamanin. Wanda ma'aurata a da can za ka ga suna samun rashin jituwa za su gaggauta miƙa lamarin ga waliyyansu, kuma nan da nan zakaga an shawo kan matsalar

Don haka idan bai gyara halinnasa ba sai kije ki samu waliyyanki ki sanardasu duk abin da ke faruwa. Abin da nake jiye miki tsoro shi ne kada kiji wataran ganki kin daukar masa kayan abinci wanda shaidan zai raya masa ai ta dade ma tana dauka batareda saninka ba alhalin ke kin dauka ne da manufar ciyarda yayansa. Ance dai maganin kar ayi kar a fara. Kuma ki godewa Allah SWT da ya zamana iya wannan ne halin nasa

A karshe muna roƙon Allah SWT ya baki ikon cin jarabawar da kike ciki tun da daman gaba daya rayuwar kowa jarabawace kamar yanda Allah SWT ya fada a cikin Suratul Mulk ayata 2, sannan kuma ki dage da tsayuwar dare, In sha Allahu za ki ga sauyi domin kuwa babu abin da ya gagari Allah SWT kuma ki dauka wannan ƙaddararkice kuma Annabi SAW ya ce babu abin da ke sauya ƙaddara sai addu'a kamar yanda hakan ya tabbata a cikin sahihin hadisin da Abdullahi Ibn Abbas RA ya rawaito

(Duba littafin Tuhfat al-Ahwadhi wallafar Al-Mundhiri hadisi mai lambata 9, chapter 13)

Wallahu ta'ala a'alam

Amsawa:

Usman Danliti Mato (Usmannoor_As-salafy)

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu. . .

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp. com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www. facebook. com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t. me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments