Ticker

6/recent/ticker-posts

Bana Sha'awar Mijina

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Slm dan allah malam inasan ataimakamin da magani kwata kwata bana sha'awar mijina ko taɓani ya yi sai naji wani iri kuma da ba haka nakeba dan Allah ataimaka

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

To 'yar uwa dalililai dayawa dake haifar da wannan. Sai dai zan takaita akan abubuwa uku kaɗai.

1. Sha'awa takan gushe daga jikin Mace ta dalilin wata cuta dake tare da ita. Misali kamar ciwon sanyi da sauran nau'o'in cutukan dake shafar Mata a al'aurarsu.

2. Wani lokacin idan mace tana shan wasu Kwayoyi masu karfi na asibiti sukan gusar mata da sha'awa. Misali kamar magungunan hawan jini, ciwon Sugar, Sickler, Arthritis, Asthma, da sauransu.

3. Shafar Aljanu: Idan mace tana da matsalar shafar Aljanu (Musamman aljanun Soyayya) sukan ɗauke duk wata ni'ima daga jikinta kuma su haifar mata da ɗaukewar sha'awa, ko jin zafi yayin saduwa.

Wata ma da zarar ta kammala Jima'i da maigidanta za ta rika ganin Maniyyin yana zubewa.

Shawara anan ita ce idan kina fama da wasu daga dalilan nan dana Lissafa, to lallai sai kin magance abun kafin kisha kowanne maganin don samun dawowar sha'awa ɗin. Amma ga wata fa'idah nan ki jarraba:

1. Ki nemi ruwan kwakwa, madara peak, da kuma ruwan Inabi ki rika sha. Domin waɗannan duk sukan haddasa dawowar ni'ima ko sha'awa ajikin Mace ko namiji.

2. Ki samu shammar ki nikashi ki rika haɗawa da zuma kina sha. In Shã Allah zaki samu lafiya.

3. Namiji wanda be cika damuwa da mace ba ko kuma wanda bashida kuzari kuma yanaso yaga yana gamsarda matarsa yanada kyau ya jarraba wannan wanda nasan wasu suna sayan garin amma basu gane yanda ake haɗawa ba dabino za'a ɓare a jefar da kwallon asamu yayan zogale da furensa dukkansu waɗanda suka bushe a inuwa sannan sai garin habbatussauda a haɗasu waje ɗaya adakasu sannan ana diban garin anasha da madara peak ko nono wannan mace ko namiji kowa yanasha sai dai banda me ciki.

Allah ta'ala yasa mudace

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments