1.
Kullum alamu
nuni suke duniyar
nan ta zo k'arshe.
2.
Yau yaƙi a nan
gobe girgiza ƙasa
3.
Ba rana ɗaya
da za ta zo ta wuce
ace ba "Wayyo!"
4.
Fad'in Manzo ne (SAWS)
Ba za a yi tashin ta
ba sai an busa.
5.
Kafin nan fa
sai an yi auren jinsi
Zina ta fantsu.
6.
Kwanaki su yi
ta gudu wal Juma'a
zuwa Juma'a.
7.
A tafka kisa
Mai kisan bai da dalil
Gawar ma haka.
8.
Dajjal zai wanzu
Al-jannarsa duniya
Bi shi ka samu.
9.
Imaninka rau
kamar garwashin wuta
a tafin hannu.
10.
Adabi birjik
Ko'ina in ka duba
har Yanar gizo.
11.
Hoto, majigi
kai dai sayi damarka
Yalo ko d'ata.
12.
Rahayil aini
Idonka ya ganema
kunne jiye mas.
13.
Cututtuka fa?!
Sabbi fil da babu su
sanin iyaye.
14.
Tafiyar wata
a yini na kwana a
k'iftawar ido.
15.
Tafiya ake
Ba tsari babu tsaro
Shugabannin "now".
16.
Rana ta fito
ta yamma k'arshen tuba
In ka sha ka sha.
17.
Karambatan ku
Musulmi da Yahudu
Babu makawa.
18.
Nasara taku
Alkawarin Allaah ne
Ba Ya sa6awa.
19.
Zuwan Annabi
Isa (AS) ya kar alade
Haramta jizya
20.
Zuwan Mahadi
na cikin alamomin
Yajuj wa Majuj
21.
Allaah Ya ba mu
sa'a da rabo Ya sa
mu wanye lafiya.
From the Archive of:
Malam Muhammad Tajajjini Tijjani
Imel: mmtijjani@gmail.com
Lambar Waya: +2348067062960
©2023 Tijjani M. M.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.