Citation: Maikwari, H.U. & Sani, A. (2020). Tahamisin Waƙaƙƙen Ƙa’idojin Rubutun Hausa. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.
512. Zancen duk da za ka kawo ga rubutu,
In dai wani ne ya
yi shi in za ka rubutu,
To sai ka yi yadda
za a gane a rubutun
Zance wani za ka
sanya ga rubutu,
In ba naka ne ba
tilas nunawa.
513. Don a fahimci kai ruwaya kaka yowa,
Zancen nan da an
ka yo ga rubutowa,
wani ne yay yi,
sai ka zo ga ruwaitowa,
Ba zancenka ne ba,
su ka karantowa,
Kai aikinka nan
wurin ɗai zanawa.
514. Tun farko ka sa alamar buɗewa,
Yo haka “ shi da
za shi karantawa,
In ya gan ta zai fahimci ruwaitowa,
Ce kaka yi batun
da kai ka rubutawa,
Shi zai nuna babu
hannunka ga cewa.
515. Don malam ya ce; “ɗabi’ar yaranta,
Ko mai kyau, irin
ta koyon malanta,
Koko akasinta mai
awa dai da mugunta,
In ko biyu ka haɗe da ƙeta da mugunta,
In aka girma kan
ta ba ta sauyawa.
516. Allah ya faɗa; “Waman ya ‘amal” lura,
Sannan Ya ce; “ Faman ya’amal” lura,
Ayoyin biyun ga an
nuna su a sura,
Az Zalzalah, ka
duba su ka lura,
Komai kay yi ran
gamo za ka ishewa.
517. Duk zancen da mun ka kawo ka kiyaye,
Wani yay yo shi,
don hakan sai a kiyaye,
Kuma mun bayyana gudun kar mu kuranye,
Sannan mun ka buɗe zance mu tumanye,
Gun buɗe shi ‘yan alamun ka gwadawa.
0 Comments
Post your comment or ask a question.