𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Salamu alaikum Don Allah ataimakamin da Amsan
Tambayan nan Kawatace Tana turkey takeson Amsan Wai wanda xata aura ne Angama
maganan aure Wai shi sai Yayi kwanciyar aure da ita Sannan Xai aure ta malam
menene hukuncin wannan auren Nasu kuma ta Yaya xata iya gamsar dashi ciwa Allah
Ya Hana tacikin sauki daxai fahimce ta Wai shi Baxai iya auren Macen Da ba
virgin bace Don Allah Malam abata Amsan tambayan.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
wa'alaikum salam. To ai Allah ne ya hana yin zina,
danhaka Allah ne yafi kamata tayi ma biyayya fiye da mijin da zata Aura, in
tana tunanin Mijin yanada abinda ze iya bata in ta Aureshi to shikuma Allah
yanada abinda yafi na Mijin in tayimishi biyayya ze bata, danhaka yazama dole
ta ƙi
yarda da saɓon da
wannan Mijin yakeso ya sakata aciki dan tayi ma Allah biyayya.
Zina tana daga cikin manyan laifuka da Allah(ﷻ) ya haramta akan dukkan musulmi namiji ko
mace, Kamar yadda Allah(ﷻ) yake
cewa a Suratul isra'i Aya 32
وَلَا تَقْرَبُوا الزِّنَا ۖ إِنَّهُ كَانَ فَاحِشَةً وَسَاءَ سَبِيلًا
FASSARA:
Allah(ﷻ) ya ce: kada ku kusanci zina, domin ita alfahashace
dakuma mummunar hanya
Saboda Mugun laifin dake cikin zina, shi yasa
Allah ya tanadar da hukuncin Jefewa ga Mazinaci ko Mazinaciya in dai sun taɓa yin aure. Idan kuma Samari ne ko 'yan
mata ana yi musu bulala ɗari-ɗari ne mutukar dai laifin ya tabbata
akansu.
Danhaka in yace baze Auri Mace wacce ba virgin
bace to yabari in an Ɗaura Auran sannan yaji ba virgin bace se ya sa
awarware Auran abashi kuɗinshi
wannan haka yake ashari'an Muslinci.
Amma yanzu inyace ze yi Zina da ita kuma ita
tayarda to ya sakata acinkin Manyan Halaka guda 5:
1. Yayi disvirgin ɗinta, in yazo ya fasa yin Auren kuma ya
riga ya hanata Auran wani wanda yakeso ya Auri virgin kenan.
2. In tabari yayi amfani da ita tariga tashiga
fushin Allah, domin ta nuna tafi jin tsoranshi akan tsoron Allah danhaka se
Allah ya ƙyaleta
dashi yaƙi
temakonta akanshi.
3. Shikanshi baze dinga ƙosawa ya Aureta ba tunda yariga ya ɗanɗani zaƙinta.
4. Shi kanshi baze dinga yarda da itaba ko bayan
Auren tunda yasan zata iya yin zina da namiji dan ta samu wani abu wanda takeso
na Rayuwa.
5. Za'a iya zuwa asamu yaro sakamakon wannan
Zinan.
Danhaka taja hankalinshi ta hanya me sauƙi ya fahimta, Musamman gurin nunamishi
wannan saɓon
Allah ne kuma ko wace irin Musifa tana iya faruwa in an Saɓama Allah kaman yanda yake ganin in an Saɓa mishi zeyi wani abu na sharri. Kuma
sannan ba wani abu bane yana iya kai ƙara abashi kuɗinshi Araba Auren akotu in yaji ke ba
virgin ba ce.
Kuma in yaƙi yarda kisancewa ko ya rabu dake to sa'a kikaci
domin ya nuna shi ba me tsoron Allah bane se ki gode ma Allah da yarabaki da
mara tsoron Allah domin ko ya Aureki baze tsaremiki Haƙƙinki yanda ya kamataba.
Allah ta'ala ya tsare mana imaninmu
Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/BSA30hdZD7V3WSJF8WVwUj
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.