Ticker

6/recent/ticker-posts

Na Auri Mace, Sai Na Gano An Taɓa Kwanciya Da Ita, Ya Zanyi?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Mutum ne ya auri mace, bayan ya sadu da ita sai ya gano ashe ba budurwa bace, An taɓa saduwa da ita. Ya zai yi ??

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wannan yana da dalilai masu yawa, akwai tabbacin budurcin ya tafi ne saboda dalilai masu yawa.

Ya wajaba a kyautatawa matar zato idan alkhairi ya bayyana a gare ta, idan tsayuwarta a addini ya bayyana toh ya wajaba a kyautata mata zato akan haka.

Idan kuma ta taɓa yin alfasha (ma'ana: Zina), sai daga baya ta tuba har tayi nadama sannan alkhairi ya bayyana a gare ta toh hakan baze cutar da ita ba.

1. Yana iya yuwuwa budurcin ya tafi ne saboda tsananin haila. Domin haila mai tsanani yana tafiyar da budurcin mace kamar yadda malamai suka fadi haka.

2. Haka nan yin tsalle shima yana gusar da budurcin mace. Idan mace tana yin tsalle daga nan zuwa cen ko kuma ta sakko daga wuri mai tsawo zuwa ƙasa da sauri (kamar steps) shima yana tafiyar da budurcin mace.

Ba dole bane budurcin mace ya tafi ta hanyar Zina, A'a. Idan mace tace budurcin ta ya tafi ne ba hanyar zina ba, to babu laifi akan haka.

Kai!!! ko ma ta hanyar zinan ne budurcin ya tafi idan tace anyi mata fyaɗe ne ko an tilasta mata yin zinan ne toh hakan baya cutarwa. Idan tayi istibra'i ko tace ta tuba daga abinda ya faru a baya sannan tayi nadama, ko kuma tace tayi Zinan ne a lokacin da bata da wayo sosai amma yanzu ta tuba, tayi nadama, wannan babu laifi.

Baya halarta a tona mata asiri, ya kamata a rufa mata asiri. Idan mijin yana zaton ita mutuniyar kirki ce sai ya zauna da ita. Idan kuma yana gani ba matar kirki bace sai ya sake ta ba tare da ya bayyanar da abinda ya faru a tsakanin su ba.

Allaah shi ne mafi Sani.

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/Du5LNx31U9hDi6RƘbbrzgW

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments