Ticker

6/recent/ticker-posts

Ta Yaya Mace Zata Gane Tana Ɗauke Da Budurcinta?

𝐓𝐀𝐌BA𝐘𝐀

Assalamu Alaikum kamar yadda akace mace tana iya rasa budurcinta ta hanyan, tsalle-tsalle, daukan abu mai nauyi, hawa bishiya, hawa keke da sauran su. to ta yaya mace zata gane tana dauke da budurcinta.?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Bisa ga amsoshi da muka samu daga iyaye da yan'uwa mata Masu yawa, yasa muka fahimci abubuwa kamar haka:

Wai shin menene budurci.? Kuma Yaya yake.?

Shi Budurci wani tantanine da yake cikin farjin mace Yana nan kamar jijiya kuma wata abune kaman fata kuma baya da ƙwari  yana nan cikin farjin mace ana ce masa BIKARA Wanda matuƙar bawai shigarsa akaiba babu yadda za'ayi ya kauce daga hanyar da yake, Sai dai Masu mummunan aikinnan wato Lesbians to shi suna iya rasashi sakamakon wannan aikin.

Shi ne zamuga Idan anyiwa yara fyaɗe ko dai anshigi mace ta ƙarfi kokuma dai shigar farjin ba daidai ba  ma'ana akarkace ko a tanƙware kodai a zumudi ake fasashi ba daidaiba har hakan ya janyo zubar jini domin an buɗe hanyarsa ba akan yadda ya daceba. Har hakan yakan rabawa mutanenmu lissafi wasu suce sai anga jini adaren farko ne sannan mace take tabbatar da budurcinta. Kuma ba daga nan take ba.

Shi budurci aranar da aka kai mace namiji ya shigi mace indai ahankali yabita zaiji daga farkon shigansa yatarar da ƙofar arufe. Wanda inme hankaline da sanin yakamata zai dinga zuwa yana dawowa ne ahankali har fatar dake wajen  tareda jijiyar nan Mara ƙwari sudinga laushi suna rauni ahankali har yasamu yacimma burinsa inda mace zata danji zafi Amma Na rashin sabobe. Sai dai baza'a ga jinin nan ba, saɓanin wadda aka shigeta da garaje ko da gwajin ƙarfin tuwo. Kuma zakuga bazata kasa tafiyaba, sakamakon anbita a yadda musulunci yayi umarni.

Amma budurci tun adaren an fasashi  sai dai zata dinga jin zafi har sai anyi yan kwanaki sannan zata saba sakamakon ƙofar da aka buɗe sabuwa ta matancinta (ma'ana kasancewanta mace). Shiyasa Wasu suke samun wani magani mai suna Love Rican (Ana ce masa yauki da Hausa) Suna amfani dashi dan rage zafi da kuma wahala. Shi wannan magani ana sanya shi ne a gaban mace a lokacin saduwa. Saboda shi maganin yanada yauki ta yanda Zai rage wahalar.

Dan haka Bazai yiyu mace ta rasa budutcinta kwata-kwata ba hassai in na miji ya sadu da ita.

Saidai akwai abinda zaisa gaban mace ya buɗe (sune kamar abinda muka fada a cikin tambayar). To amma itama bazata zama kamar wanda aka sadu da itaba

Sannan ko mace ta aikata ɗaya daga cikin abinda aka ambata ba lallaine ta buɗe ba. Tananan a cikin budurcinta matikar bata ga alamomi ba.

Akwai alamomin da mace zata iya gane budurcinta ya ragu kafin miji ya kusanceta.

1. Alokacin da ta hau bishiya ko take tsalle-tsalle ko ta hau keke, zataga jini yana zuba bayan lokaci kaɗan.

2. Lokacinda al'adanta yazo zataga yana zuba da yawa, ba kaman yanda ya saba zuwaba.

3. Zataji raguwan Ni'ima (wato Sha'awa)

4. Idan mace ta buda kafafunta Zataji iska yana ahiganta can ciki.

To wayannan Alamu suna iya bayyana ga wanda budurcinta ya ragu, wato ta buɗe. Amma bawai ya karu bane.

Wannan shi ne a takaice abinda muka fahimta daga amsoshi da yan'uwa suka bamu akan wannan tambaya.

Muna Addu'ah Allah ya saka wa kowa da Alkhairi ya kara ilimi da basira.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/CfDLSdXaGD00Wpxdfy2ofp

𝐓𝐄��𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments