Ticker

6/recent/ticker-posts

Munyi Zina Bayan Na Biya Sadaki

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum warahamatulla ina son Dan Allah a taimaka muna da fatawa akan wannan "wani bawan Allah ne ya nemi mace ya bada sadaki kafin aure sai sukayi zina koda yake yanason ya nuna cewa kan zakarinsa ne kawai ya shiga sai yaji tsoron Allah ya fidda ma'ana bai zuba maniyyinsa a cikintaba .

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salam warahmatullahi Wabarkatuh

1. Bayar da sadaki bai mayar da ita matarsa ba,  har sai an daura auren. Don haka bai halatta daga biyan sadaki ya fara keɓancewa da ita a ɗaki ko a Zaire ko a notary ba. Haka kuma wannan bai halatta masa yin tafiya da ita zuwa wani gari ko wani wuri ba. Kamar kuma yadda bai halatta masa ya sadu da ita ba.

2. Saduwa da matar da ya biya sadakinta tun kafin a daura musu sahihin auren Sunnah ba daidai ba ne.  Wannan zina  ne kawai! Allaah ya kiyaye.

3. Ma'anar saduwa a wurin malaman musulunci shi ne abin da ambata, watau:Haduwar kaciyarsa da kaciyarta. Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

إذا التقى الختانان فقد وجب الغسل، وإن لم ينزل

Ma'ana: Idan kaciya biyu suka Haɗu da juna to wanka ya wajaba,  ko da kuwa bai fitar da maniyyi ba.

Watau a duk lokacin da wurin da aka yanke na kaciyar miji ya haɗu da wurin da ake yankewa a wurin kaciyar matarsa to shikenan janaba ta same su sai su yi shirin wanka kawai.

4. Wannan hukuncin wadanda suka zama ma'aurata kenan. Idan kuma ba ma'aurata ba ne,  watau ba a riƙa an daura musu sahihin aure ba, to a nan dole su tuba tare da yawaita istigfari, tun kafin a kama su a tsayar musu da haddin Allaah na buloli dari-dari, ko kuma na jefewa da duwatsu har matuwa, idan ya/ta taɓa yin aure!

5. Idan wannan abin ya auku a tsakanin masu neman aure,  ba za a daura auren ba sai lokacin da ta gama yin istibraa'i na tsawon jini guda ɗaya,  a maganar da ta fi inganci a wurin malamai.

WALLAHU A'ALAM

Shaikh Muhammad Abdullah Assalafiy

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/J1hm5Tw12uYBƙfaiPwf28l

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments