Ticker

6/recent/ticker-posts

Biyayya Ga Miji Tana Gaba Da Biyayaya Ga Iyaye.

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum Mallam ina cikin wani tashin hankali, iyayena ne suka samo min aiki, mijina yace ba zan yi ba, nayi nayi ya ki ya yarda, su kuma sun ce sai nayi, mahaifina yace idan mijin nawa ya ki yarda na yi tahowa ta na amshi posting letter na, in mijin ya gaji ya biyoni. Dan Allah mallam meye abin da ya kamata nayi? na rasa yadda zanyi. Magana ta gaskiya mijina bai rageni da komai ba, babu abin da baya min kawai dai aiki yace ba yanzu ba. Yanzu ni dai bana son na saɓa ma iyayena kuma bana so na ki bin umurnin mijina ya zanyi dan Allah ?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikum assalam. Ki yi kokari wajan gamsar da iyayanki, da hakurkurtar da su,  Idan ba su yarda ba, ki yi biyayya ga mijinki saboda ya fi mahaifinki girman hakki a kanki.

Allah ya yi Umarni da biyayya ga iyaye a ayoyi masu tarin yawa a cikin Al'ƙur'ani da hadisai, saidai a wajan Mace miji yana gaba da Uba, Annabi ( yana cewa: "Inda zan umarci wani ya yi sujjada ga wani, to da na umarci mace ta yi sujjada ga mijinta".

Tun da mijinki yana biya miki dukkan bukatunki, barin aikin ya zama wajibi, saboda aikin Gwamnati ga mace yana halatta ne in akwai bukata kuma ya aminta daga cakuɗawa da maza.

Tafiya wajan aiki ba tare da iznin mijinki ba saɓon Allah ne da keta alfarmar Shari'a,  Allah ya umarci Mace da ta zauna a gidanta a aya ta (33) a suratul Ahzaab:

وَقَرْنَ فِي بُيُوتِكُنَّ وَلَا تَبَرَّجْنَ تَبَرُّجَ الْجَاهِلِيَّةِ الْأُولَىٰ ۖ وَأَقِمْنَ الصَّلَاةَ وَآتِينَ الزَّكَاةَ وَأَطِعْنَ اللَّهَ وَرَسُولَهُ ۚ إِنَّمَا يُرِيدُ اللَّهُ لِيُذْهِبَ عَنْكُمُ الرِّجْسَ أَهْلَ الْبَيْتِ وَيُطَهِّرَكُمْ تَطْهِيرًا

Kuma ku tabbata a cikin gidãjenku, kuma kada ku yi fitar gãye-gãye irin fitar gãye-gãye ta jãhiliyyar farko. Kuma ku tsaĩda sallah, kuma ku bãyar da zakka, ku yi ɗã,ã ga Allah da ManzonSa. Allah na nufin Ya tafiyar da ƙazamta kawai daga gare ku, yã mutãnen Babban Gida! Kuma Ya tsarkake ku, tsarkakewa.

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/Cnf26Ƙ8MPƙz9yUYU1nxƙRƙ

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments