TAMBAYA (97)❓
Assalamualaikum mallam. Ina
kwana, dafatan katashi lfy mallam, inna niman fatawa cikin wannan al'amari.
Matana ne ta tafi gidansu ta yi wa ma'aifiyanta karya wai bana ciyar da ita, ah hallin ba haka bane wallahi wallahi wallahi mallam babu randa ba ayin abinci agidana saidai randa idan taqiyi, mallam tsakani da Allah abinda yashiga tsakanin mu shine kamar haka
1) na hanata yin sana'ar ta na
kwaliya sabida bata zama agida kuma bata yimin abinci, intayima ba akan
lokaciba wani sa'in idan aikin agida zatayi sai nadawo gida sai na tsinci yan
mata wani 1 wani 2 wani 3 duk dai inda yaka kuma da zanuwa aqirijin su Kuma
baligai
2) saikuma saniya da muka hada
kudi zamu yanka da Sallah sai yanaso yakasa sai muka yanka ana Sallah sauran
sati 1 nakawo mata nace da ita tasoya naman nam ta'ajiye dashi zamuyi hidiman
Sallah amman se ta rabar da naman duka ga yan mata masu zuwa gujin ta aiki.
Kurum ranar Sallah da tatafi masallacin idi bata dawo gidana ba yanzu haka tana
gurin ma'aifiyanta domin ma'aifinta ya mutu. Mallam atemaka min da mataki daya
dace na dauka bissalam nagode
Mallam wallahi wallahi wallahi
wannan shine Dining dinmu dakuma kitchen dinmu ah haka wai bana ciyar wa
AMSA❗
Waalaikumussalam, warahmatullahi,
Wabarakatuh
Lahaula wala quwwata illa billah
To dan uwa, indai har yanda ka
fada dinnan haka maganar take to abinda ta aikata bai dace ba
Dangane da sana'ar da take yi,
indai har zata dinga fifita neman kudi ta hanyar yin kwalliya akan yi maka
biyayya wajen aiwatar da ayyukan gida kamar irinsu girki da sauransu to wannan
ta jahilci yanda ake rayuwar zamantakewar auratayya a bisa koyarwar shari'ah
Duk abinda yake kawo irin
wadannan matsalolin shine: rashin halartar makarantar yanda ake rayuwar aure a
shari'ance a musamman a lokacin da aka sakawa mace rana. Daga sanda aka ce an
kusa bikin mace to kamata yayi ta shiga makarantar koyar da zamantakewar aure
don ta samu ilimin da zata zauna da mijinta lafiya kamar yanda matan Annabi
Sallallahu alaihi wasallam suka zauna dashi
Kana da qwaqqwarar hujjar da zaka
hanata sana'ar nan saboda ko iya kallon mace baliga mai daurin kirji bai
halatta ba, tunda kafadunta suma al'aura ne. Kuma majority idan mata sun hadu a
gidan kwalliya ko kunshi ba hirar lahira ake yi ba ko kuma abinda ke faruwa a
cikin kabari, saidai abinda aka fi yi shine; tsegumi, gulma da munafurci kuma
idan itama matar mara wayo ce sai ta dinga fallasa asirin mijinta a gaban
wadanda takewa kwalliyan wanda cin naman mutum kuma haramun da nassi a cikin
Qur'ani da Allah Azzawajallah yace
( يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اجْتَنِبُوا كَثِيرًا مِّنَ الظَّنِّ
إِنَّ بَعْضَ الظَّنِّ إِثْمٌ ۖ وَلَا تَجَسَّسُوا وَلَا يَغْتَب بَّعْضُكُم بَعْضًا
ۚ أَيُحِبُّ أَحَدُكُمْ أَن يَأْكُلَ لَحْمَ أَخِيهِ مَيْتًا فَكَرِهْتُمُوهُ ۚ وَاتَّقُوا
اللَّهَ ۚ إِنَّ اللَّهَ تَوَّابٌ رَّحِيمٌ )
الحجرات
(12) Al-Hujuraat
Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku nĩsanci abu mai yãwa na
zato. Lalle sãshen zato laifi ne. Kuma kada ku yi rahõto, kuma kada sãshenku yã
yi gulmar sãshe. Shin, ɗayanku
nã son yã ci naman ɗan'uwansa
yanã matacce? To, kun ƙĩ shi
(cin nãman). Kuma ku
bi Allah da taƙawa. Lalle Allah Mai karɓar
tũba ne, Mai jin ƙai.
Haka kuma idan sana'ar kwalliya
din da take yi ya shafi har irinsu make up to da kuma saka man bleaching to
wannan haramun ne saboda canza halittar Allah ne, kuma daman Iblis ya dauki
alqawarin sai ya sa mutane sun canza halittar da Allah yayi musu, kamar yanda
Allah Subhanahu wata'ala ya labarta mana a cikin Qur'ani;
( وَلَأُضِلَّنَّهُمْ وَلَأُمَنِّيَنَّهُمْ وَلَآمُرَنَّهُمْ فَلَيُبَتِّكُنَّ
آذَانَ الْأَنْعَامِ وَلَآمُرَنَّهُمْ فَلَيُغَيِّرُنَّ خَلْقَ اللَّهِ ۚ وَمَن يَتَّخِذِ
الشَّيْطَانَ وَلِيًّا مِّن دُونِ اللَّهِ فَقَدْ خَسِرَ خُسْرَانًا مُّبِينًا
)
النساء
(119) An-Nisaa
"Kuma lalle ne, inã ɓatar da su, kuma lalle ne
inã sanya musu gũri, kuma lalle ne ina umurnin su dõmin su kãtse kunnuwan
dabbõbi, kuma lalle ne inã umurnin su dõmin su canza halittar Allah." Kuma
wanda ya riƙi
Shaiɗan majiɓinci, baicin Allah, to, haƙĩƙa yã yi hasara, hasara
bayyananniya.
Kuma masana kiwon lafiya sunce
"Yin kwalliyar bleaching yana kawo cutar Glaucoma (Hawan jinin ido)".
Wannan qalubale ne ga masu canza halittar Allah. Dadin dadawa kuma bai halatta
a kira ta kwalliya wani wajen ba, ba tare da ta nemi izininka ba
Duk wadannan hujjoji ne akan
abinda ya shafi sana'ar da take fifitawa akan Ibadah wato zaman aure
Dangane da batun watandar saniya
da kukayi tare, shima bai kamata ta rabar da naman gaba daya ga customers din
ta ba, ko da ace tayi hakanne don ihsani to amman shaidan zai iya rinjayarta ta
basu don ta kara jan su a jiki saboda sana'ar nan da take yi, abinda yafi
dacewa shine ta rabawa makusantan ta musamman la'akari da cewar su marayu ne
kamar yanda kace mahaifinta ya rasu, ka ga sune suka fi cancantar naman sallar
bawai masu zuwa kwalliya ba
Wasu matan basu da godiyar Allah,
yanzu ace wannan shine kitchen da kuma dining table din gidanka (Tabarakallah,
kamar yanda na ga ni a video din da ka turo) amman ace bazata yi maka girki
yanda kake so ba, alhalin wasu matan basu samu rabin-rabin irin wannan ba, kuma
ga halin da ake ciki na tsadar rayuwa
Wannan kadan kenan daga cikin
halayen wasu matan. Kuma shiyasa ma wasu mazajen suke saka sharadi kafin su
auri mace akan cewar ba zata yi aiki ba, wasu mazan ma suna dauke nauyin biyan
matan sana'ar da suke yi, duk wata
Dangane da matakin da zaka dauka,
shawarar da zan baka anan itace; ka qyaleta ta ci gaba da zama a gidan nasu,
tunda ai macen da aka saketa ita ake biko kuma kai baka sake ta ba, idan ta
gaji da zaman gidansu dole wataran zata kiraka a waya. Kamar yanda wata baiwar
Allah itama ta je gida, lokacin da suka samu matsala da mijinta karshe sai ga
ta tana yi masa flashing a waya saboda ta gaji da zaman gidannasu. Sai ga ta ba
shiri ta koma tana bawa mijin haquri
Kaima kada abin ya daga maka
hankali. Kuma kada shaidan yayi nasara akanka kace zaka saketa, saidai ko da ta
dawo to ka saka mata sharudda. Idan kuma waliyyanta sun kira ka sai ka je kayi
musu bayani. Amman idan ba wanda ya kira ka, kawai ka ci gaba da zuba ido ka ga
iya gudun ruwanta tunda ai igiyar aure a hannunka take ba a hannunta ba
Wallahu ta'ala a'alam
Amsawa
Usman Danliti Mato
(Usmannoor_Assalafy)
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.