Ticker

6/recent/ticker-posts

Mu Gode Allahu Mai Rahama: Ta Malam Zainu Zubairu Bunguɗu

 Citation: Bunguɗu, U.H. (2021). Bara da wasu waƙoƙin bara a ƙasar HausaAhmadu Bello University Press Limited.

Domin samun cikakken littafi, a tuntuɓi:

Dr. Haruna Umar Bunguɗu
(Sarkin Gobir Na Bunguɗu)
Email: harunaumarbungudu@gmail.com
Phone: 08065429369

Bara da wasu waƙoƙin bara a ƙasar Hausa

Mu Gode Allahu Mai Rahama: Ta Malam Zainu Zubairu Bunguɗu

1. Mu gode Allahu Mai Rahama,

 Rahamarsa bai manta kowa ba.

2. Tsira ta dawwama ga manzonsa,

 Dukansu ba’a keɓe kowa ba,

3. Zuwansa yazan zuwan rahama,

 Garemu ba ko da nisa ba.

4. Alaye Sahabbai Iyalansa,

 Zuriyarsa ban zaɓe kowa ba.

5. Da Malamai masu bin sunnah,

 Ban ce da wannan ƙazami ba.

6. Allahu na roƙi ilhami,

 Gareka ba don isa ta ba.

7. Don shugabanmu macecinmu,

 Wannan da bai taɓa laifi ba.

8. Shi ya fi kowa wajen daraja,

 Tausai ba ai ba kamarshi ba.

9. Baiwa na zo karya kafirai,

 Zuwansa ba su sheda daɗi ba.

10. Da Larabawa da baubayi,

 Ba a samu gwarzo kamar shi ba.

11. Ba a haifi ɗa mai sifatai ba,

 Ba za’a haifi awar shi ba.

12. Madogarar masu addini,

 Islamiyya ba mishawa ba.

13. Aminu Sadiƙul Masduƙu,

 Ba a samu mai gaskiyatai ba.

14. Mu tattaro mu bi Allahu,

 Ba a yo mu don shagali ɗai ba.

15. Allahu ya yomu don bauta,

 Bai yo mu don bauta banza ba.

16. Jama’a mu bauta ma Allahu,

 Bai ce mu bauta wani nai ba.

17. A ɗau zancen huwa Allahu,

 Kalmag ga ba ta ba da fili ba.

18. Kowa da manzo wujibina,

 Ban ce ga kalmar khususiya ba.

19. Ma a ti kumdubi baɗato,

 Bayar da yinta da wasa ba.

20. Neman sani farlu aini ne,

 Tsakalaini ba a keɓe kowa ba.

21. Tardi da sunnah da wajibi,

 Ba a sauƙaƙa su ga kowa ba.

22. Duba ga zance hi wallahu,

 Bai keɓe kowa ga dibi ba.

23. Fasalu ahlazzikiri,

 Duba ta butu baka filiba.

24. Musan huwallahu shi ne ɗai,

 Zagi siga bada tsaniya ba.

25. Shi ya yi kome da kowa duka,

 Bai tara komi da kowa ba.

26. Hakan ga bauta mu bauta mai,

 Bai tara mulki da kowa ba.

27. Shi ka shikai na ibada to,

 Guda biyar ba da waiba.

28. Shahada taini kaza sallah,

 Ƙidansu bai zo da nauyi ba.

29. Azumi da zakka sako hajji,

 Rufesu bako da wargiba.

30. Dan babu wasa ga addini,

 Zancen ga bai zan fadata ba.

31. Wanka na tsarki wajibi na,

 Ga baligi ba ga kowa ba.

32. Ko yaushe janaba ta same ka,

 Wanka kake ba da nayyi ba.

33. Taro mazanmu da matanmu,

 Haɗa sagir ba a keɓe kowa ba.

34. Haila nifasi ga matanmu,

 Ba a sauƙaƙa ta ga kowa ba.

35. Tardi kudu’i ga mai sallah,

 Shi yi taimama ba wudu’i ba.

36. Sai wanda ya zan,

 Mulkinsa bai rage kowa ba.

37. Mu bauta Allahu mai ƙudura,

 Bai ɓata ƙarfinsa banza ba.

38. Ko wabbi Allahu ya huta,

 Dimma sun bi bada wargi ba.

39. Janfansu na can ya tara,

 Ba a hori kowa da bina ba.

40. Mukama sunnah mu bar bidi’ah,

 Bai bauta mai bashi komai ba.

41. Kowabbar bautarsa ya taɓe,

 Bautar ko ba ta duba komi ba.

42. Ku bauta banza kuzan banza,

 Mazanmu basu shafi kowa ba.

43. Mai tasbahal hajji inna,

 Dikinka bai kare kowa ba.

44. Dumaso shatu da mai sufi,

 Aikinka bai zan da shiriya ba.

45. Ƙarya namima munafunci,

 Mai yinsu ba za shi tsira ba.

46. Daci da ceto da kha’inci,

 Mai yinsu ba za shi tsira ba.

47. Haka shangiya yi da girman kai,

 Mai yinsu baza shi tsira ba.

48. Mu daina ƙwace mu bar fahara,

 Mai yinsu ba za shi tsira ba.

49. Da mai halatta haramiya,

 Wallahi ba za shi tsira ba.

50. Da mai haramta halaliya,

 Guzurinsa ba za a karɓa ba.

51. Da cin gululi zalinci,

 Mai yinshi ba zai tsira ba.

52. Haka nan riyar mu bar yinta,

 Mai yinta ba zai tsira ba.

53. Da dukiyar wanda bai da uba,

 Kwacci ta ba za shi tsira ba.

54. Mai cin amana da iskanci,

 Mai yinshi ba za shi tsira ba.

55. Da masu murna da kafirci,

 Murnassu bata da ɗa komi ba.

56. Kukansu na tsana an tara,

 Guzurinsu bai zan nasheshi ba.

57. Sai wanda ya tuba ya daina,

 Ba za a tuna hali nai ba.

58. Allahu yay muna alkawali,

 Ba za shi swaɓa faɗatai ba.

59. Komi kake so kana samu,

 Ni’i marta ba zata kare ba.

60. Ga kautsara salsalibu mu sha,

 Daɗinsa bamai iyaka ba.

61. Akwai gurasa akwai cincin,

 Da na kiya ba da nisa ba.

62. Akwai halawa dama,

 Da kin-kin bana tuya ba.

63. Aljanna shayi da alkuskus,

 Ba wagga suya ta mata ba.

64. Nama dafaffe da soyayye,

 Ni’imat ta ba za ta ƙaura ba.

65. Nama na kifi da tsuntsaye,

 Da marmari ba na yinwa ba.

66. Diyan itace da alkaki,

 Ga ɗakina ba na bunu ba.

67. Ga kasiratu suna murna,

 Angonsu bai zo gadaje ba.

68. Haskensu ya wuce haske duk,

 Ƙawarsu ba ta ɓoye bargo ba.

69. Ƙamshinsu yasina almiski,

 Tabshinsu ba zai misaltu ba.

70. Da shimfiɗu da gadajensu,

 Da majingini bana rimi ba.

71. Kuma ga kujeru na kin tayakin,

 Kafinta bai haɗa koɗai ba.

72. Zinariya wa su murjani,

 Ƙawarsu bata zan kama ɗai ba.

73. Da Lu’u-lu’u wasu di baji,

 Aljanna ba ta zan kama ɗai ba.

74. Wato tabna harzuƙa da faɗa,

 Ga munafukai ba da rauniya ba.

75. Duk hankalin kafirai shi ɓace,

 Sun hangi ba zasu tsira ba.

76. Son zuciya sunka tasamma,

 Sun zaɓi yau basu farko ba.

77. Kowabbi son zuciya nan,

 Halakarsu ba zata nau yi ba.

77. Biyar ta zaɓin gidan halaka,

 Hajjimmu ba zata sauna ba.

78. Ita kurkuku ce ga mai binta,

 Zaɓin ta bai bar ka shirya ba.

79. Zabaniyawa su kama shi,

 Duka suke ba da wargi ba.

80. Su basu saɓa faɗar Allah,

 Ko ƙanƙane ba kamar mu ba.

81. Duk wanda yaƙi umurninta,

 Ba zai ga wannan misibar ba.

82. Man khafa rabbahu ya huta,

 Munarsa ba a san iyaka ba.

83. Aljanna can zashi ba fashi,

 Wa’adinsa ba za shi tayar ba.

84. Aljanna daɗinta ya fi gida,

 Daɗinta ba a san iyaka ba.

85. Gulbin ruwa wanda ya fi zuma,

 Zaƙinsa ba a san iyaka ba.

86. Gulbin zuma madara da giya,

 Ka shata ba zaka maye ba.

87. Kuma ga azurta da marjani,

 Sifarta ba zata ganu ba.

88. Akwai tufafi iri da iri,

 Ba a san iyakar ƙawa tai ba.

89. Akwai awaki da raƙuma,

 Aljanna ba za mu tsufa ba.

90. Ba mai tunani da zai mutuwa,

 Abadan ba zai sake ƙaura ba.

91. Da babu ciwo ciki abada,

 N’imarta ba zata tsufa ba.

92. Matansu ba wadda ke haila,

 Bare ace bata yo tsarki ba.

93. Haka ba nifasi ga Aljanna,

 Shagali suke ba da ƙoshi ba.

94. Kuma ba turoso bare bauli,

 Ko kaci ba zaka khabasi ba.

95. Aljanna ba majinar hanci,

 Sai kwalliya ba ƙazamta ba.

96. Aljanna daɗinta ya fi gida,

 Ni’imarta ba za ta gamu ba.

97. Ya rabbi yafe zunubbaina,

 Dukkansu ba don halina ba.

98. Ya rabbi saukar da jinƙanka,

 Garemu ba don halina ba.

99. Kuka nike Nawa laifuka,

 Da na yi ban san iyaka ba.

100. Ƙanana sun fi dubu miliyan,

 Ban ƙirga laifin dana yo ba.

101. Manyansu sun fi ƙanana yawa,

 Ba zan gane halina ba.

102. Halin da na yi babu kyawo,

 Ba zani manta halina ba.

103. Saɓo nike bani fasawa,

 Kullin daɗi ba da rauni ba.

104. Tuna shi kan sani yin kuka,

 Halinga bai bani sha’awa ba.

105. Allahu na roƙi jin ƙanka,

 Ka bamu si ba da nisa ba.

106. Rahamarka tafi zunubai na,

 Jinƙanka bai rage kowa ba.

107. Wanke ni in zama tsarkaka,

 Islamu ba fa niyyarka lama ba.

108. Ya rabbana bamu jinƙanka,

 Mu san shiga ba da wargi ba.

109. Ya rabbana yafe laifinmu,

 Tun ba a kira mu zuwa can ba.

110. Ka yafe laifin da mun gwabza,

 Mu tsira tun ba da ƙuna ba.

111. Diyanmu tare da matanmu,

 Da ɗiyansu ban keɓe kowa ba.

112. Da ‘yan uwana masoya na,

 Islamu ba kafirawa ba.

113. Musa dawwama cikin ni’ima,

 Ni’imar da ba zata ƙare ba.

114. Ba don halinmu da cikinmu,

 Dumma su bi ba da wargi ba.

115. Domin sahabbai da alaye,

 Musa mu kai ba da suna ba.

116. Da sussuka daɗa tai tsaba,

 Aljannah bamu ƙuna da haushi ba.

117. Wa’azi nike gani ba ilimi,

 Kuma jahili ba cikakke ba.

118. Ya malamaina ku dube ni,

 Ku yi taimako ba da wargi ba.

119. Na roƙi gyara ga malumma,

 Na gaskiya ba mishawa ba.

120. In sun kace maka wai waƙa,

 Ɗan malami bada fahari ba.

121. Zubairu Bunguɗu babansa,

 Sunansa bai zan ɓatacce ba.

122. Uwarsa Aisha ‘yar Malam,

 Sayuɗi ban ɓoye komai ba.

123. Ismi Muhammad Ɗan Malam,

 Zubairu ban raɓa laƙabi ba.

124. Bare kace zaka neme ni,

 Ka kaini ba inda na kai ba.

125. Baiti ɗari munka ƙirga ta,

 Saba’in suna bi bila rai ba.

126. Sannan takwas sunka raɓo su,

 Bayansu bai ƙara komi ba.

127 Hijira ɗafin sahi na yi ta,

 Ɗakin rajab ba da ɓaci ba.

128. Tammat Wa amnat bi aunillahi,

 Rabil wara ba wani na ba.

Post a Comment

0 Comments