Ticker

6/recent/ticker-posts

Bismillahi Farkon Zance: Ta Malam Zainu Zubairu Bunguɗu

 Citation: Bunguɗu, U.H. (2021). Bara da wasu waƙoƙin bara a ƙasar HausaAhmadu Bello University Press Limited.

Domin samun cikakken littafi, a tuntuɓi:

Dr. Haruna Umar Bunguɗu
(Sarkin Gobir Na Bunguɗu)
Email: harunaumarbungudu@gmail.com
Phone: 08065429369

Bara da wasu waƙoƙin bara a ƙasar Hausa

Bismillahi Farkon Zance: Ta Malam Zainu Zubairu Bunguɗu

1. Bismillahi farkon zance,

Na da nake nufin shiryawa.

 2. Mun gode wa sarkin baiwa,

 Allah wanda ba shi gushewa.

 3. Muna shukura muna ƙarawa,

 Baiwa rabbu na sabkowa.

 4. Tsira sallama da aminci,

 Gun mahmudu mai shiryawa.

 5. Bayan godiya da salati,

 Ga shakwa da zan bayarwa.

 6. Nai kuka ina ta hawaye,

 Laifuka na nake ta tunowa.

 7. Ga kaya muna Tarawa,

 Ga karfi shina ƙarewa.

 8. Ga kaya kwarai sun nauyaya,

 Ba gammo da zamu azawa.

 9. Ga mu cikin duhu ba haske,

 Babu abin da zan ya dawa.

 10. Ga mu cikin ruwa ga kaya,

 Ga gulbi shina kawo wa.

 11. Kowa ga mu kai yai zafi,

 Kana ba wurin hutawa.

 12. Gulbi ya cike yai baye,

 Amma ba ruwan kurɓawa.

 13. Kowa sai shina masha’a,

 Babu hani bare horawa.

 14. Don ga zamani ya canza,

 Ga ƙarfinmu bai ƙarawa.

 15. Ɓanna ta yawaita ga fili,

 Sai ‘yan ƙalla ke ɓoyewa.

 16. Kunya ta ƙaranta ga kowa,

 Manya yara ba runtsewa.

 17. Kowa duniya ya zaɓa,

 Sai ‘yan kalla ke waigawa.

 18. Ga gyaransa ga ɓarnassu,

 Kuwa ne basu san dainawa.

 19. Ga bami da burkutu fili,

 Sai in ba kason kurɓawa.

 20. Ga duma ga giya barasa,

 Ga kabso suna watsawa.

 21. Sauran shaye-shaye gaba ɗai,

 Ko fili ana saidawa.

 22. Ba tsoro bare jin kunya,

 Sai ‘yan ƙalla ke ɓoyewa.

 23. Caca da shan giya ba dama,

 Sai daɗuwa suke ƙarawa.

 24. Sata ci da ceto rashuwa,

 Ga bori suna ƙagawa.

 25. Ga zina ta yawaita a fili,

 Talla suke suna saidawa.

 26. Karuwa da su da karame,

 Har kullum suna tarawa.

 27. Manya yara ba mai kunya,

 Ɓanna ɗai suke kwaɓawa.

 28. Ba mai tattalin ayi gyara,

 Sai mai tattalin ɓatawa.

 29. Sun mance da ɗakin turɗa,

 Mai tsanani wajen kwantawa.

 30. Kabri ga duhu ga kewa,

 Sai halinka zaka ishewa.

 31. In khairinka ya rijaya,

 Shi ne ɗan’ uwan kwantawa.

 32. In mugun hali ka aika,

 Ka ɓata ba wurin hutawa.

 33. Ga duka Nakiri da Munkar,

 Bayan tambayar ruɗarwa.

 34. Ga shi wuta tana ɓullo mashi,

 Ga shi a kwance ba motsawa.

 35. Dangogin azaba tari,

 Sun riske shi bai tserewa.

 36. Ga shi cikin duhu ga kewa,

 Shina ƙarar da ba karɓawa.

 37. Hali nai dashi zai zauna,

 Dan nan ma har zuwa tayarwa.

 38. Allah ya tada shi ba fashi,

 In mun tuba zai yafewa.

 39. Komi ke yawan zunubanka,

 In yaso shina yafewa.

 40. Sai bawa baƙi mummuna,

 Mai shirka ba a yafewa.

 41. Sai ya tuba ya bar tsafi,

 Ya bi rasulu mai shiryawa.

 42. Sannan za shi sadu da jinƙai,

 Domin daha mai shiryawa.

 43. Ya bar godabensa da haske,

 Haske wanda baya dushewa.

 44. Har abada da bashi katsewa,

 Zance ne da bai canzawa.

 45. Islamu ne addini,

 Har abada da bai yankewa.

 46. Sa shirya garemu cikakka,

 Har ko yaushe ba saɓawa.

 47. Ya Allah kai ka ishemu,

 Samammu kaza da rasawa.

 48. Mai roƙo ka roƙi ta’ala,

 Shi ke baka shi ka hanawa.

 49. In ya baka to ka samu,

 Ba wani wanda za shi hanawa.

 50. In ya hana ka wa zai baka,

 Ba wani wanda za shi iyawa.

 51. Rayayye wadatacce ne,

 Komi na shi bai ƙarewa.

 52. Kai ɗai ke garan tun fari,

 Ban ƙara ba, ban ƙarawa.

 53. Komi nawa kai kab bani,

 Ba wani wanda zai amshewa.

 54. Ya Allah ban imani,

 Sabitu wanda bai katsewa.

 55. Ban ikon da na bauta ma,

 Bauta wadda ba tsaidawa.

 56. Ƙanana da manya,

 Har ko yaushe ba ƙetawa.

 57. Komi ka hana in barshi,

 Ban kamnarshi ban dubawa.

 58. Komi nawa kai kayyoshi,

 Sai ka yarda zan sheɗawa.

 59. Don haka kai roƙon kowa,

 Sai kai mai abin bayarwa.

 60. Ya razzaku arzittani,

 Ko yaushe ina walawa.

 61. Allah bani ilmi rasikhu,

 Har ko yaushe ban mantawa.

 62. Na roƙa ka ban ilhami,

 Koyaushe ina ganewa.

 63. Na yi tawassuli da Muhammad,

 Khairul kalki mai shiryawa.

64. Ya Allah ka bani bayani,

 Komi na shi zan kyawawa.

65. Don kakan Hassan da Hussaini,

 Mai baiwa shina ƙarawa.

66. In ka zo garai ya baka,

 Ko baka zo ba zai aikawa.

67. Ya mai tsamo masu nutsewa,

 Zaɓaɓɓe abin zaɓowa.

68. Ga mu cikin ruwa mun noce,

 Ba motsi bare tasowa.

69. Ya jirgin fito fishshe mu,

 Tun sheɗanmu da dawowa.

70. Cetanmu macecin bayi,

 Tun kukanmu na juyawa.

71. Don Allah ya zaɓeka,

 Shi ya raya ka ba togewa.

72. Gun darajjakka ba jayayya.

 Gun tsimma bare tserewa.

73. Tun farko fa ba tamkarka,

 Har ƙarshe ba’a samowa.

74. Kai ne mai daraja tamma,

 Zaɓaɓɓe wanda zashi musama.

75. Kai ne Swadiƙul masduƙu,

 Kwar roƙa ka bashi rasawa.

76. Mai baiwa da bashi kwarri,

 Ko ya baka zashi daɗawa.

 77. Baya son ka don samunka,

 Ba ya ƙin ka don jemewa.

78. Komi zo garai ya bayar,

 Mai baiwa shina ƙarawa.

79. Bai gajiya da bai wa manzo,

 Komi na shi bai ɓoyewa.

80. Shi zai baka har shi isheka,

 Ahmadu Ɗaha bai ƙosawa.

81. Mai so nai kaza mai ƙin shi,

 In zai baka bai ƙoshewa.

82. In ya baka sai ya ba shi,

 Har kullum ba zai fasawa.

83. Shi ne kamilul ihsani,

 Mai natsuwa mafi yafewa.

84. Ko ka cuci Annabi Ɗaha,

 Bai gurin shirin ramawa.

85. Ramko nai gareshi Nasiha,

 Ga khaira shi na ta daɗawa.

86. In ya baka sai ka gode,

 Har abada baka mantawa.

 87. Kowas so shi Ahmadu Ɗaha,

 Ya huta ba ya ƙonewa.

 88. Don haka na garai muka raɓa,

 Don ranarmu mai tarawa.

 89. Allah bamu yarda taka,

 In ga rasulu mai tserarwa.

 90. Bada wuya ba ya Allah,

 Don zati ba zamu rasuwa.

 91. Don zatinka shiryasshemu,

 Har mu ga Ɗaha ba ƙonawa.

 92. Don zatinka karɓi du’aina,

 In tsira ba Konawa.

 93. Laifina da nai yafe mani,

 Domin Ɗaha mai cetowa.

 94. Ga zunubai muna Tarawa,

 Ga kuka muna rabkawa.

 95. Yafe man zunubaina duk,

 Don rahamakka mai shafewa.

 96. Mata na dani da uwaye,

 Na da ɗiyanmu ba keɓewa.

 97. Dangina da almajiraina,

 Da ɗiyansu ban zaɓewa.

 98. Malamanmu su da masoya,

 Kakanninmu ba keɓewa.

 99. Sa jama’a musulmai su duka,

 Rayayyu da masu macewa.

 100. Kai muna arziki mu ga Annabi,

 Ko ciwon mu na warkewa.

 101. Kowa yagganai ya warke,

 Saura nai gidan hutawa.

 102. Can darus salami mu huta,

 Hutawa da ba ƙosawa.

 103. Baiti ne dari na tsara,

 Ga ishirin suna raɓewa.

 104. Fi hadi sashin na yi ta,

 Gun hijra mafi shiryawa.

 105. Salli alaihi ya Allahu,

 Alaye da masa biyawa.

 106. Aiki nai kaza zance nai,

 Ba su rage shi basu daɗawa.

 107. Bunguɗu ce garin mai waƙa,

 Zainu Zubairu ban ɓoyewa.

 108. Ga aiki gare ni daɗaɗɗe,

 Ɗan ilmin mu bai warkarwa.

 109. Datti gare shi ga shi kaɗanne,

 Na nutsa ko ina tasowa.

 110. Nan na dakata nai aya,

 Allah sa muna ƙarawa.

 111. Amin rabbu domin zafi,

 Sa gurin mu bai takewa.

Post a Comment

0 Comments